Sashe 103
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ai Hajiyayye na jin haka ta zube a kasa ta fashe da kuka. Tsoro yayi mata yawa zawon ya fara tsartuwa daga ma'ajiyarsa saboda tsoro. Muryar Awwab dama irin wannan deep voice din ce mai tahowa daga kirji. Mata da yawa suna fadawa soyayyarsa a kanta yayin da take razana marasa gaskiya irin Hajiyayye.
"Kayi min rai ranka ya dade aradun Allah karya nake ni ba mayya bace. Mutum ce kamar kowa kuma indai aurene ko bai sakeni ba ni na saki kaina yanzu zan tafi ba sai kun zo ba"
Dariya yake neman yi Radhiya tace da sauri "ranka ya dade bari na tayaku binciken kafin ku iso zan tabbatar da gaskiyarta" kashe wayar tayi ta ga kowa ya fara ja da baya saboda zawon Hajiyayye. Wari ya isheta amma haka ta daure bata matsa ba.
"Me kike cewa?"
"Nace ba, aurena da Malamijo wallahi duk shiri ne tsakanina da Talle. Rabonmu kawai muka zo yaga mu tafi amma bani da alaka da mayu. Kuyi hakuri yarana akwai marayu a ciki. Waye zai kula dasu?"
"Tunda har kun iya kulla cuta ki shirya ko ba'a kamaku an cinye ba zaki shiga prison. Kurkuku nake nufi" Emzee yace yana cin magani.
Rarrafawa tayi wurin Malamijo wanda hankalinsa ya kwanta da ya gano me Radhiya ta shirya. Dage hanci yayi ga wari ya dame shi "ki kwashe yaranki kada ki koma min cikin dakin Hajjo. Daga nan ki tsaya ki kirawo su. Sannan shanuna...."
Tana kuka tuni ta mike tana gyara zani babu kyan gani tace "suna gidan Talle"
"Me kike jira ne baki fita ba sun kusa isowa" Radhiya ta dada tsorata ta. Yaran ta kira suka fito a gurguje kan kace meye wannan sun fita Malamijo yana daga murya yana sanar da ita saki uku yayi mata.
Suna fita gidan ya kaure da hayaniya da murna. Malamijo tsananin farinciki yace "kowa ya shaida wallahi na bawa 'Yar Soja kyautar tunkiya, akwai wata mai ciki ta zama taki"
"Ahhh nifa gaskiya tayi min kadan" tace tana tura masa baki.
Baiyi fushi ba ya saki fuska "to me kike so Alherin babanta"
"Alheran ne fa ba Alheri ba"
"To ni dai sammakal...me kike so? Kai ku fito kowa yayi shaida zan yiwa babbar jika ta kyautar bajinta"
"Ni dai kada ka kasa fa"
"Ke! Dube ni nan da kyau Ali Gidado nake. Ciki lafiya baka lafiya. Da kudina a jikina"
Kowa ya fito harda maijego Atine. Hassana da Usainanta suna bayan Zayyana da Hibbah da suke jindadin daukar yaran. Radhiya ta dan hadiyi yawu kafin tace "Malamijo za ka dawo da Hajjo ko?"
"Kamar da kasa yarinya. Ai da shike Allah Ya taimakemu dole mata suke idda kinga bata gama ba har yanzu da damar kome tsakaninmu"
"To dama so nake tunda ka yarda za ka min abinda nake so su duka matan nan ka hada da Nene Marka da kai kanka Hajji me zuwa ayi daku"
Yawu mai daci ne ya tokare masa a wuya da yaji me tace. Dan murmushin nasa ya bace bat. Hajji har mutum shida kamar tana son talauta shi. Bai bata amsa ba yace Emzee su zo su tafi gidan Talle a fito masa da shanunsa. Radhiya tace to a bata tinkiyar mara ciki a yanka.
"Indai nama ne muje gonar sha Allah an dena miya lami a gidan Malamijo amma ki sake shawara akan batun zuwa hajji. Idan ba kaina zan sayar ba dame zan biya kudin"
***********
Safiyar laraba washegarin tahowarsu daga Abuja jiki a sanyaye Ummi ta ajiye wayarta tana matsar kwalla a boye. Ashe Daada yana kula da ita. Fita tazo yi daga dakin saboda kukan da ya taho mata ya yi saurin tare hanyar.
"Haba Fillo me zaki boye min? Waye ya rasu kike kuka kuma baki son na sani?"
Kukan gabadaya ya taho mata yana rarrashinta sannan da kyar ta fada masa cewa matar Badaru ce ta kirata wai yau sadakar uku na rasuwar Mal. Aminu abokin mahaifinsa mai matsayin uba a gareshi wanda yake ta dokin zuwa ya gani. Jikinsa ne ya saki ya zauna ya dafe kai.
"Sojana kayi hakuri" tace wata kwallar na taruwa a idonta.
"Waye ya isa yaja da ikon Allah? Zamu iya tafiya a yau ko kin gaji?"
Da sauri ta tashi "muje yau din."
Ba wasu kaya suka baza ba, abinci ma siya sukayi jiya da yau din shiyasa cikin abinda bai kai minti shabiyar ba sun gama kimtsawa dreban kawai suke jira yaje siyan mai. A hanyarsu ta zuwa Sakkwaton babu wata hira. Zayyan yaci burin zaman hira da Mal. Aminu Allah bai nufa ba. Sun isa da sauran haske Ummi ta rinka kwatantawa dreban Daddy din da ya kawosu. Zayyan ganin garin yayi kamar ba Sakkwaton da ya sani ba. Kamar sauran wuraren da ya gani nan ma an sami chanji na fasalin abubuwa da cigaban rayuwa. Karuwar tituna da gine gine yasa bai gane lungun gidan nasu ba. Har yanzu dai mota bata shiga amma duk da haka wurin ya sauya. Sun fara tafiya Ummi ta dan dakatar dashi da suka karya kwanar gidan Mal. Aminu maimakon su mike hanyar gidan nasa iyayen.
"Ko za ka jira na fara zuwa na sanar dasu kada ganinka ya tsorata mutane da yawa."
Bai musa mata ba don yasan gaskiya ta fada. Ita kadai ta karasa kofar gidan daga gefe an saka rumfa inda maza suke nasu zaman makokin. Kan ta a kasa taji an kira sunanta "Maman Radhiya kece da yamman nan?"
Rayyanu ne yayan Zayyan wanda yake bi. Gefe ta dan matsa yazo ya sameta suka gaisa.
"Kinje gidan babu kowa ko? Da yake yau za'a rufe zaman makokin duka muna nan"
Ta'aziyya ta fara yi masa kafin cikin nutsuwa ta sanar dashi dawowar Zayyan a takaice. Ikon Allah kawai ya rinka ambata kafin yace ta shiga ciki zai taho dashi. Tana kallonsa ya duka yana yiwa Badaru rada kafin ta karasa shiga gidan. A tare suka nufi hanyar da ta baro da sauri kamar zai tafi kafin su karasa.
Dan uwa dan uwane komai lalacewarsa. Lokacin da yake tare dasu a shekarun da suka gabata kiyayya, kyara, hassada da bakinciki ne kadai abinda yake gani a idanun 'yan uwan nasa. Yanzu kuwa kafin su karasa gaban juna daga shi har su hawayen farinciki suke zubdawa. Dayake dreban Daddy yana da labarin yadda akayi zaton Zayyan ya rasu da dawowarsa baiyi mamaki ba da ya ga magidanta irinsu rungume da juna suna hawaye. Hakuri ya rinka basu amma sai da kyar suka iya mallakar kawunansu don ma a waje suke.
"Muje Jume ta ganka Zayyan." Badaru ya ja hannunsa kamar ya kama yaro.
A ciki kuma bayan yin gaisuwa ga Gwaggo Ladi da 'ya'yanta mata dake wurin Ummi ta matsa kusa da su Mubaraka da matan su Badaru ta fada musu dawowar Zayyan. Matan mazan na alhini yayunsa mata suna kuka. Jume ta zaga bayi sai Gwaggo Ladi suka fadawa. Hankula suka tattara suka koma kofar gida sai suka fara tunanin ko dai su koma nasu gidan ne tunda nan gidan gaisuwa ne ga matan mutane a zazzaune.
"Ku barni na ganshi kafin ku tafi. Allah bai kaddari haduwarsa da babansa ba ku bari na gane masa Zayyanu" cewar Gwaggo Ladi.
Sallamar babban dan Mal. Aminu da kannensa maza dasu Badaru ita ta sanya matan kuka da ganin Zayyan da yake tsakiyarsu. Idonsa a kan Gwaggo Ladi tana dago masa hannu ya taho gareta. Girma ya kamata sosai tafiya tana wahalar da ita. A gabanta ya durkusa gidan ya koma tamkar yanzu akayi mutuwar. Daga inda Jume take bayan ta fito daga bandakin take jiyo koke koke. A tsaye suke ita da wata jikarta ta wurin 'yarta mace ta saka ta kiran Maikudi a waya. Kare masa tanadi tayi rai a bace har anyi uku bai zo ba. Yana gidan ma aka aiko da rasuwar yaki fita wai ciwon jiki yake yi. Ya riga ya sakawa ransa cewa Mal. Aminu makiyinsa ne bai ga dalilin zuwa jana'iza ko gaisuwa ba. Sai da ta gama fadan ta ajiye wayar ta tako itama din kafafun sai a hankali.
Kamar ance ta kalli gaban Gwaggo Ladi sai ganin mutum tayi a durkushe gabanta 'yan uwansa sun kusa rufe shi. Gaba na faduwa da rawar murya tace "wa nake gani kar Mal. Muhammadu?"
Kama yayi mata sosai da mijinta matar Rayyanu ta kamo hannunta a hankali ta zaunar a gefen Gwaggo Ladi. Zayyan ya matso yana murmushi da 'yar kwallarsa.
"Jume Zayyanu ne ya dawo"
Idanunta ta shafa harda gogewa da zaninta tayi murmushi mai ciwo "ko dai nima na mutu ne?"
Sai ta sake tsinkewa jama'a zukata aka cigaba da kuka.
"Jume ni din ne dai Zayyanu ba mutuwa nayi ba"
"Nagode Allah da bakina zan rokeka gafara" tace tana wani irin kuka da take tuna bakar izayar da ta rinka gana masa tun kuruciya. Maikudi da ya gagareta har yanzu waye silar lalacewarsa idan ba ita ba.
Basu barta ta cigaba da magana ba suka tattara duka iyalin gidan Marigayi Muhammadu Tureta suka tafi nasu gidan. Murna a wurin 'yan uwansa da 'ya'yansu da suka sanshi a matsayin baban su Radhiya ba kadan ba.
"Me zan dafa maka Zayyanu? Ban yarda ka ci abincin kowa ba sai girkina. Kai ku hura min wutar icce ni ba son girkin risho nake ba"
Zaunar da ita Zayyan yayi yana dariyar yadda ta tashi hankalinta "ki zauna nayi ta kallonki Jume"
"Har me zaka kalla a jikin matar da taci zalinka ta kasa rike amanar maraya"
Mairamu da kowa ma hawaye suke yi na tausayinsu. Ga su Badaru da suka san yadda rayuwar gidan nasu ta kasance tun da su ma sai rokonsa gafara suke yi.
"Bana jindadin yadda kuke yi min. Jume ke uwa ce a gareni mai cikakken iko akan danta. Da dadi da babu dadi kinci kashina kinci fitsarina. Wahalar da nasha ta kuruciya ita ta samar da Zayyan din da yake gabanki mai hakuri da juriya" ya juya ga 'yan uwansa "idan kuna biye mata za ku tabbatar min da cewa ni din dan uba ne kawai baku daukeni kaninku ba"
"Kayi min rai ranka ya dade aradun Allah karya nake ni ba mayya bace. Mutum ce kamar kowa kuma indai aurene ko bai sakeni ba ni na saki kaina yanzu zan tafi ba sai kun zo ba"
Dariya yake neman yi Radhiya tace da sauri "ranka ya dade bari na tayaku binciken kafin ku iso zan tabbatar da gaskiyarta" kashe wayar tayi ta ga kowa ya fara ja da baya saboda zawon Hajiyayye. Wari ya isheta amma haka ta daure bata matsa ba.
"Me kike cewa?"
"Nace ba, aurena da Malamijo wallahi duk shiri ne tsakanina da Talle. Rabonmu kawai muka zo yaga mu tafi amma bani da alaka da mayu. Kuyi hakuri yarana akwai marayu a ciki. Waye zai kula dasu?"
"Tunda har kun iya kulla cuta ki shirya ko ba'a kamaku an cinye ba zaki shiga prison. Kurkuku nake nufi" Emzee yace yana cin magani.
Rarrafawa tayi wurin Malamijo wanda hankalinsa ya kwanta da ya gano me Radhiya ta shirya. Dage hanci yayi ga wari ya dame shi "ki kwashe yaranki kada ki koma min cikin dakin Hajjo. Daga nan ki tsaya ki kirawo su. Sannan shanuna...."
Tana kuka tuni ta mike tana gyara zani babu kyan gani tace "suna gidan Talle"
"Me kike jira ne baki fita ba sun kusa isowa" Radhiya ta dada tsorata ta. Yaran ta kira suka fito a gurguje kan kace meye wannan sun fita Malamijo yana daga murya yana sanar da ita saki uku yayi mata.
Suna fita gidan ya kaure da hayaniya da murna. Malamijo tsananin farinciki yace "kowa ya shaida wallahi na bawa 'Yar Soja kyautar tunkiya, akwai wata mai ciki ta zama taki"
"Ahhh nifa gaskiya tayi min kadan" tace tana tura masa baki.
Baiyi fushi ba ya saki fuska "to me kike so Alherin babanta"
"Alheran ne fa ba Alheri ba"
"To ni dai sammakal...me kike so? Kai ku fito kowa yayi shaida zan yiwa babbar jika ta kyautar bajinta"
"Ni dai kada ka kasa fa"
"Ke! Dube ni nan da kyau Ali Gidado nake. Ciki lafiya baka lafiya. Da kudina a jikina"
Kowa ya fito harda maijego Atine. Hassana da Usainanta suna bayan Zayyana da Hibbah da suke jindadin daukar yaran. Radhiya ta dan hadiyi yawu kafin tace "Malamijo za ka dawo da Hajjo ko?"
"Kamar da kasa yarinya. Ai da shike Allah Ya taimakemu dole mata suke idda kinga bata gama ba har yanzu da damar kome tsakaninmu"
"To dama so nake tunda ka yarda za ka min abinda nake so su duka matan nan ka hada da Nene Marka da kai kanka Hajji me zuwa ayi daku"
Yawu mai daci ne ya tokare masa a wuya da yaji me tace. Dan murmushin nasa ya bace bat. Hajji har mutum shida kamar tana son talauta shi. Bai bata amsa ba yace Emzee su zo su tafi gidan Talle a fito masa da shanunsa. Radhiya tace to a bata tinkiyar mara ciki a yanka.
"Indai nama ne muje gonar sha Allah an dena miya lami a gidan Malamijo amma ki sake shawara akan batun zuwa hajji. Idan ba kaina zan sayar ba dame zan biya kudin"
***********
Safiyar laraba washegarin tahowarsu daga Abuja jiki a sanyaye Ummi ta ajiye wayarta tana matsar kwalla a boye. Ashe Daada yana kula da ita. Fita tazo yi daga dakin saboda kukan da ya taho mata ya yi saurin tare hanyar.
"Haba Fillo me zaki boye min? Waye ya rasu kike kuka kuma baki son na sani?"
Kukan gabadaya ya taho mata yana rarrashinta sannan da kyar ta fada masa cewa matar Badaru ce ta kirata wai yau sadakar uku na rasuwar Mal. Aminu abokin mahaifinsa mai matsayin uba a gareshi wanda yake ta dokin zuwa ya gani. Jikinsa ne ya saki ya zauna ya dafe kai.
"Sojana kayi hakuri" tace wata kwallar na taruwa a idonta.
"Waye ya isa yaja da ikon Allah? Zamu iya tafiya a yau ko kin gaji?"
Da sauri ta tashi "muje yau din."
Ba wasu kaya suka baza ba, abinci ma siya sukayi jiya da yau din shiyasa cikin abinda bai kai minti shabiyar ba sun gama kimtsawa dreban kawai suke jira yaje siyan mai. A hanyarsu ta zuwa Sakkwaton babu wata hira. Zayyan yaci burin zaman hira da Mal. Aminu Allah bai nufa ba. Sun isa da sauran haske Ummi ta rinka kwatantawa dreban Daddy din da ya kawosu. Zayyan ganin garin yayi kamar ba Sakkwaton da ya sani ba. Kamar sauran wuraren da ya gani nan ma an sami chanji na fasalin abubuwa da cigaban rayuwa. Karuwar tituna da gine gine yasa bai gane lungun gidan nasu ba. Har yanzu dai mota bata shiga amma duk da haka wurin ya sauya. Sun fara tafiya Ummi ta dan dakatar dashi da suka karya kwanar gidan Mal. Aminu maimakon su mike hanyar gidan nasa iyayen.
"Ko za ka jira na fara zuwa na sanar dasu kada ganinka ya tsorata mutane da yawa."
Bai musa mata ba don yasan gaskiya ta fada. Ita kadai ta karasa kofar gidan daga gefe an saka rumfa inda maza suke nasu zaman makokin. Kan ta a kasa taji an kira sunanta "Maman Radhiya kece da yamman nan?"
Rayyanu ne yayan Zayyan wanda yake bi. Gefe ta dan matsa yazo ya sameta suka gaisa.
"Kinje gidan babu kowa ko? Da yake yau za'a rufe zaman makokin duka muna nan"
Ta'aziyya ta fara yi masa kafin cikin nutsuwa ta sanar dashi dawowar Zayyan a takaice. Ikon Allah kawai ya rinka ambata kafin yace ta shiga ciki zai taho dashi. Tana kallonsa ya duka yana yiwa Badaru rada kafin ta karasa shiga gidan. A tare suka nufi hanyar da ta baro da sauri kamar zai tafi kafin su karasa.
Dan uwa dan uwane komai lalacewarsa. Lokacin da yake tare dasu a shekarun da suka gabata kiyayya, kyara, hassada da bakinciki ne kadai abinda yake gani a idanun 'yan uwan nasa. Yanzu kuwa kafin su karasa gaban juna daga shi har su hawayen farinciki suke zubdawa. Dayake dreban Daddy yana da labarin yadda akayi zaton Zayyan ya rasu da dawowarsa baiyi mamaki ba da ya ga magidanta irinsu rungume da juna suna hawaye. Hakuri ya rinka basu amma sai da kyar suka iya mallakar kawunansu don ma a waje suke.
"Muje Jume ta ganka Zayyan." Badaru ya ja hannunsa kamar ya kama yaro.
A ciki kuma bayan yin gaisuwa ga Gwaggo Ladi da 'ya'yanta mata dake wurin Ummi ta matsa kusa da su Mubaraka da matan su Badaru ta fada musu dawowar Zayyan. Matan mazan na alhini yayunsa mata suna kuka. Jume ta zaga bayi sai Gwaggo Ladi suka fadawa. Hankula suka tattara suka koma kofar gida sai suka fara tunanin ko dai su koma nasu gidan ne tunda nan gidan gaisuwa ne ga matan mutane a zazzaune.
"Ku barni na ganshi kafin ku tafi. Allah bai kaddari haduwarsa da babansa ba ku bari na gane masa Zayyanu" cewar Gwaggo Ladi.
Sallamar babban dan Mal. Aminu da kannensa maza dasu Badaru ita ta sanya matan kuka da ganin Zayyan da yake tsakiyarsu. Idonsa a kan Gwaggo Ladi tana dago masa hannu ya taho gareta. Girma ya kamata sosai tafiya tana wahalar da ita. A gabanta ya durkusa gidan ya koma tamkar yanzu akayi mutuwar. Daga inda Jume take bayan ta fito daga bandakin take jiyo koke koke. A tsaye suke ita da wata jikarta ta wurin 'yarta mace ta saka ta kiran Maikudi a waya. Kare masa tanadi tayi rai a bace har anyi uku bai zo ba. Yana gidan ma aka aiko da rasuwar yaki fita wai ciwon jiki yake yi. Ya riga ya sakawa ransa cewa Mal. Aminu makiyinsa ne bai ga dalilin zuwa jana'iza ko gaisuwa ba. Sai da ta gama fadan ta ajiye wayar ta tako itama din kafafun sai a hankali.
Kamar ance ta kalli gaban Gwaggo Ladi sai ganin mutum tayi a durkushe gabanta 'yan uwansa sun kusa rufe shi. Gaba na faduwa da rawar murya tace "wa nake gani kar Mal. Muhammadu?"
Kama yayi mata sosai da mijinta matar Rayyanu ta kamo hannunta a hankali ta zaunar a gefen Gwaggo Ladi. Zayyan ya matso yana murmushi da 'yar kwallarsa.
"Jume Zayyanu ne ya dawo"
Idanunta ta shafa harda gogewa da zaninta tayi murmushi mai ciwo "ko dai nima na mutu ne?"
Sai ta sake tsinkewa jama'a zukata aka cigaba da kuka.
"Jume ni din ne dai Zayyanu ba mutuwa nayi ba"
"Nagode Allah da bakina zan rokeka gafara" tace tana wani irin kuka da take tuna bakar izayar da ta rinka gana masa tun kuruciya. Maikudi da ya gagareta har yanzu waye silar lalacewarsa idan ba ita ba.
Basu barta ta cigaba da magana ba suka tattara duka iyalin gidan Marigayi Muhammadu Tureta suka tafi nasu gidan. Murna a wurin 'yan uwansa da 'ya'yansu da suka sanshi a matsayin baban su Radhiya ba kadan ba.
"Me zan dafa maka Zayyanu? Ban yarda ka ci abincin kowa ba sai girkina. Kai ku hura min wutar icce ni ba son girkin risho nake ba"
Zaunar da ita Zayyan yayi yana dariyar yadda ta tashi hankalinta "ki zauna nayi ta kallonki Jume"
"Har me zaka kalla a jikin matar da taci zalinka ta kasa rike amanar maraya"
Mairamu da kowa ma hawaye suke yi na tausayinsu. Ga su Badaru da suka san yadda rayuwar gidan nasu ta kasance tun da su ma sai rokonsa gafara suke yi.
"Bana jindadin yadda kuke yi min. Jume ke uwa ce a gareni mai cikakken iko akan danta. Da dadi da babu dadi kinci kashina kinci fitsarina. Wahalar da nasha ta kuruciya ita ta samar da Zayyan din da yake gabanki mai hakuri da juriya" ya juya ga 'yan uwansa "idan kuna biye mata za ku tabbatar min da cewa ni din dan uba ne kawai baku daukeni kaninku ba"