Sashe 65
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ido ta tsaya gogewa da hannu babu kunya babu tsoron Allah sakamakon gamon da tayi bayan ta dago. Wata take gani kamar kanwarta cikin shiga ta kece raini ta wuce sa'a. Daga sama har takalmin kafarta sai da ta bisu da ido tana jinjina kyau da haduwa irin na suturar da mai ita.
"Mairama? Mairama kece ko dai kama ce?"
Sassanyan murmushin nan nata mai kara kawata kyakkyawar fuskarta ta saki "Adda Salame nice mana"
Tsananin mamaki bai bar Salame ta dakata haka nan ba sai da ta ciro hannu tana yawo dashi a gaban fuskar Mairama wadda farin gilashinta ya karawa kwarjini.
"Kina ganin me nake da hannuna?" Tace baki na rawa.
Ummi sai ta kama hannun ta rike. Nata yayi laushi sosai saboda gyaran da akayi musu a salon. Na Salame kuwa sai dai ayi shiru ayi kurum inji dogaran sarki. Kanta da lamba...a daiyi shirun kawai.
"Adda idanuna sun bude cikin hukuncin ubangiji. Zamuyi magana dai ina da baki" ta fada tana yin gaba da sauri.
"Banten uba, kai!!!" Salame tace a gigice gabadaya ta kasa gane me take yi. Ko dai gizo ne tayi mata ba ita din bace a zahiri? A'a Mairama dai kanwarta ita ce da wannan shigar ta chanja tayi kyau haka kuma wai TANA GANI? Zuciyarta bugu take yi kawai kamar wadda tayi tsere ga bakinciki da takaici sun taru sunyi mata rubdugu.
Zaninta karamar yarinyar ta sake ja tayi nisa a tunani taji cikin kuka tana cewa "Umma, umfafa ta kare"
Wata mahaukaciyar mangara ta kaiwa yarinyar wadda take rike da zanin leshin da dama da kyar ta hade shi a jikinta saboda ciki. Yadda yarinyar tayi gaba ta fadi haka ta tafi da zanin babarta Salame a hannu. Sai ga Salame matar Alh Indararo a tsaye da dan sket dinta na ciki ya fita hayyacinsa saboda tsabar jigata da kodewa. Dan lace din da akayi masa cin baki dashi ya barke yana reto a jikin kafafunta wurin gwiwa bari daya ne dinkin bai gama fita ba. Kuma gashi na silk mai santsi wani zare zare nan duk ya fara fita daga inda dinkin lace din ya fita. Bata ma ankara da wuri ba sai da babbar 'yar tace "Umma ina zaninki?"
Baki ya goge da ashar har ta gama hado shi zata lafta mata ta ga mutane sun zuba mata ido wasu suna ta dariya. Sai a lokacin ta hango shi a hannun mai kuka. Kafafunta ta kalla kunya matsananciya da muzanta suka dirar mata. Ga ciki ga dan lace suna neman kayar da ita haka ta tafi da uban sauri ta finciko zanin ta daura mutane suna ta dariya. Duk masifarta sai ta rasa abin cewa ta shiga neman wurin buya saboda kofar gidan babu wani wurin wucewa an cika makil.
Lokacin da Radhiya ta fita Awwab yana tsaye a gefe suna magana da daya daga cikin mutanen Nijar din amma da yake tun zuwansa hankalinsa gabadaya yana kan kofar yana fatan fitowarta shiyasa tana leko da kanta ya hangeta. Ajiyar zuciya ya saki da ganin fuskar da yake matukar so da kauna. Ita kuwa sai waige waige take tana yi tana komar da kanta saboda mutane.
Alh Sidi ne ya fara ganinta daga inda suke tsaye ya tabo dan uwansa Alh Ghoumar yana murna "kaga Alheran"
Alh Ghoumar ya juya shima yayi sa'ar ganinta "Allah mai iko, ka ga kamaninta da tamu Alheran din?"
"Dalilin da yasa na ganeta ma kenan"
Tana wannan leken taji an kamo hannunta an ja ta gaba. Zata yi magana ta ga Emzee ne. Ita fa bata san da wasu baki ba Hammanta tazo gani. Yana rike da ita bai saketa ba sai a gabansu. Kanta ne ya nemi juyewa dama ga yara sun yanyame motocin saboda kyaunsu ga kuma su kansu mutanen da yawa suna ta fitowa daga mota. Kukan Mammee da ta rungumeta har yafi na dazu domin yadda Radhiya take diban yanayi sosai da yayarta. Murmushin da Radhiya tayi ya kara karya mata zuciya saboda lotsawar kumatun sak na yayarta ne.
Emzee yana yi mata bayani su ma suna ta yarensu suna dan hadowa da Hausa saboda jikokin nasu. Fada musu yayi su dan kara hakuri suka ce babu komai sun san gida ne na taro gashi ba'a san da zuwansu ba. Radhiya dai yau harda jin kunya yadda mutanen nan dukkansu suke ta rungumarta matan. Mazan ma ita dai taji wani ya kamo hannunta babba ne kuwa abokin wasan Zayyan sai dai kafin ta motsa taji wani tattausan hannu ya janyota baya sannan ya dawo gabanta ya tsaya tsakaninta da mutumin. Babu mai fahimtar mai Awwab yayi ko dalilinsa sai wanda yasan tsakaninsa sa Radhiya. Abinda yaji ya ratsa shi kuwa shima sai da yayi nadamar taba hannun nata. Daga inda yake tsaye yana kallon wannan runguma zuciyarsa ta tsinke da yaga mata sun kare kada a fara da maza. Kishin da ya yunkuro masa ba kadan bane. Allah ne Ya taimake shi ya taho da wuri yau da sai anyi abinda zai mutu bai manta ba, wato Alheran dinsa a jikin wani. Babu ruwansa da alakar dake tsakaninsu tunda ya tabbatar babu muharraminta ciki idan aka cire kakaninta biyu Alh Ghoumar da Alh Sidi. Sauran duk wanda ya tabata ya taba masa mata ne.
Ummi da kanta ta rufo mayafi ta leko kiransu. Mutane suna darewa wadannan jama'a guda wadanda dukkansu kowa ka kalla kasan ya taka wani abu a duniya na arziki mazansu da matansu suka shige inda aka nuna musu. Tabarmi ne sababbi manya aka shimfide musu suka zazzauna babu girman kai da jin su din wasu ne. Mammee ta rike Ummi tana ta sharar hawaye. Rabon da su hadu shekara goma shatara tun ranar sunan Alheran Radhiya.
Wurin minti goma ana ta matsar kwalla Ummi an fama mata rashin gwarzon namiji masoyin kwarai Zayyan uban 'ya'yanta.
"Mairama yaya bayan saduwa? Kiyi hakuri. Don Allah ke da 'ya'yan nan kuyi hakuri" Alh Sidi yace yana duban su duka su ukun.
Salame da kunya ta korota sashen mazan gidan nasu taci karo da wannan abin al'ajabi. Wurin gabadaya wani irin kamshi yake yi. Sakato tayi tana kallon mutanen. Maza biyu cikinsu wato su Alh Ghoumar sun dora rawaninsu na al'ada a kawunansu. Sauran kuwa sai ka rantse wasu larabawa ne. Buzaye ne gaba da baya da kudi ya kara gyarawa rayuwa suka kara fitowa. Bakinta bai iya neman abin fada ba na nuna mamaki taji muryar marainiyar wayonta Mairama.
"Don Allah ku dena bamu hakuri ba laifinku bane. Kaddara ce kawai da kuma abinda Kawun yaran nan yayi mana"
Kallo ta bita dashi suna zaune tsakiyar mutanen da ita da 'ya'yanta. Zuciyarta har wani girgiza tayi da ta kalli Emzee. Itama sai ya tuna mata da nata tsohon mikin na son mijin kanwarta. Babban abin da ya daure mata kai shine sanin da tayi Mairama ta makance suna kauye ita da gayyar yaranta. To tana ina ne ta warke kuma suka yi fes dasu ba yadda take tsammanin ganinsu ba? Ga wani kyakkyawan saurayi tsaye a gefe ya tokare kafarsa daya da bango shi kuma ko waye? Tambayoyi take ta yiwa kanta tana neman amsa ido rufe.
"Matsa a wuce" taji ance daga bayanta. Matsawar tayi kuwa aka fara shigowa da tray-tray na kayan abinci da abubuwan sha. Duk abinda za'a tanada Innawuro ce ta kwance gefen zaninta ta bada kudi masu yawa har su Yadikko sai da suka yi mamaki. Bafillatana tana zaune haka cikinsu ana dariya ashe dukiya ce a jikinta. An dibar musu cikin abincin bikin sannan aka siyo tsire da balangu mai yawa da lemukan roba da ruwa masu sanyi.
"Shiga ku gaisa mana 'yan uwan Marigayi ne daga Nijar" Hajjo tayi maganar tana wucewa ciki ita da su Nene Marka suka gaisa da bakin aka gabatar musu da abinci. Kamar zata hadiyi zuciya ta juya batare da ta cewa kowa uffan ba ta bar wurin. Su dinma babu wanda ya kula da ita suna murnar ganin juna.
"Bari mu baku wuri kuci abinci don Allah. An tafi kiran babana sai ku gaisa"
"Ki bar mana yaran idan tashi zaki yi"
Wata mata mai faram faram tace cikin hausar da tafi kama da ta Kanawa. Ilai kuwa ashe aure ne ya kaita Nijar ita ce amarya cikin matan Alh Sidi amma mutuniyar Kano ce.
Ummi tana murmushi tace dama wa ya aiketa. Inda Awwab yake tsaye ta kalla "dan Ummi zo muje kaci abinci"
"Bazai ci cikinmu ba? Tare muka taho shima bako ne" saurayin da suke magana dazu dashi yace yana dariya.
"Wannan naku ne kada ka damu dani" Radhiya ya kalla ta wani nutsu kamar ba ita ba "taso ki zuba min".
Ummi na jin haka tayi gaba abinta tana murmushi suka tashi aka basu wuri domin su samu su sake musamman mazan. Emzee ne kawai bai tashi ba yana aikin amsa musu tambayoyin da suke yi masa game da rayuwarsu.
Kofar da zata fitar dashi waje Awwab ya bi ba wadda zata sada shi da ainihin tsakar gidan ba. Radhiya sai tabi bayansa suka fito yayi hanyar inda ya ajiye tasa motar. Baya ya bude mata babu musu ta zauna shima ya zauna a gaba bangaren dreba kafafunsu suna waje. Lallen kafarta ya kalla ta saka daya daga cikin takalman da ya kawo mata tayi matukar kyau.
"Shigar da kafarki ciki"
Zumbura masa baki tayi sannan ta dauke kafafun.
"Me yasa kika dena daukar wayata yau kwana biyu?" Ya tambayeta da wannan deep voice din tasa.
Shagwabe fuska tayi kafin tace "to ba kaine ka dena kirana ba saboda ka koma Katsina wurin....wurin"
Fada yaso yi mata na hora shi da tayi ta hana shi jin daddadar muryarta idan tana shagwaba ko ta hado wani shirmen nata sai ya kasa. Ganinta kawai da yadda tayi masa kyau ya kawar da komai.
"Wurin wa?"
Harara ta galla masa tana juya idanu ita anyi mata laifi sai dai gabadaya abin da tayi sauke masa kasala yayi "ai ka fini sanin wa nake nufi. Wurin My G mana ni kuma ka manta dani"
Bushewa yayi da dariya damuwarsa ta ragu sosai. Babu wani abu da yake tunani sama da mallakar wannan yarinyar da take gabansa a matsayin matar aurensa.
"Mairama? Mairama kece ko dai kama ce?"
Sassanyan murmushin nan nata mai kara kawata kyakkyawar fuskarta ta saki "Adda Salame nice mana"
Tsananin mamaki bai bar Salame ta dakata haka nan ba sai da ta ciro hannu tana yawo dashi a gaban fuskar Mairama wadda farin gilashinta ya karawa kwarjini.
"Kina ganin me nake da hannuna?" Tace baki na rawa.
Ummi sai ta kama hannun ta rike. Nata yayi laushi sosai saboda gyaran da akayi musu a salon. Na Salame kuwa sai dai ayi shiru ayi kurum inji dogaran sarki. Kanta da lamba...a daiyi shirun kawai.
"Adda idanuna sun bude cikin hukuncin ubangiji. Zamuyi magana dai ina da baki" ta fada tana yin gaba da sauri.
"Banten uba, kai!!!" Salame tace a gigice gabadaya ta kasa gane me take yi. Ko dai gizo ne tayi mata ba ita din bace a zahiri? A'a Mairama dai kanwarta ita ce da wannan shigar ta chanja tayi kyau haka kuma wai TANA GANI? Zuciyarta bugu take yi kawai kamar wadda tayi tsere ga bakinciki da takaici sun taru sunyi mata rubdugu.
Zaninta karamar yarinyar ta sake ja tayi nisa a tunani taji cikin kuka tana cewa "Umma, umfafa ta kare"
Wata mahaukaciyar mangara ta kaiwa yarinyar wadda take rike da zanin leshin da dama da kyar ta hade shi a jikinta saboda ciki. Yadda yarinyar tayi gaba ta fadi haka ta tafi da zanin babarta Salame a hannu. Sai ga Salame matar Alh Indararo a tsaye da dan sket dinta na ciki ya fita hayyacinsa saboda tsabar jigata da kodewa. Dan lace din da akayi masa cin baki dashi ya barke yana reto a jikin kafafunta wurin gwiwa bari daya ne dinkin bai gama fita ba. Kuma gashi na silk mai santsi wani zare zare nan duk ya fara fita daga inda dinkin lace din ya fita. Bata ma ankara da wuri ba sai da babbar 'yar tace "Umma ina zaninki?"
Baki ya goge da ashar har ta gama hado shi zata lafta mata ta ga mutane sun zuba mata ido wasu suna ta dariya. Sai a lokacin ta hango shi a hannun mai kuka. Kafafunta ta kalla kunya matsananciya da muzanta suka dirar mata. Ga ciki ga dan lace suna neman kayar da ita haka ta tafi da uban sauri ta finciko zanin ta daura mutane suna ta dariya. Duk masifarta sai ta rasa abin cewa ta shiga neman wurin buya saboda kofar gidan babu wani wurin wucewa an cika makil.
Lokacin da Radhiya ta fita Awwab yana tsaye a gefe suna magana da daya daga cikin mutanen Nijar din amma da yake tun zuwansa hankalinsa gabadaya yana kan kofar yana fatan fitowarta shiyasa tana leko da kanta ya hangeta. Ajiyar zuciya ya saki da ganin fuskar da yake matukar so da kauna. Ita kuwa sai waige waige take tana yi tana komar da kanta saboda mutane.
Alh Sidi ne ya fara ganinta daga inda suke tsaye ya tabo dan uwansa Alh Ghoumar yana murna "kaga Alheran"
Alh Ghoumar ya juya shima yayi sa'ar ganinta "Allah mai iko, ka ga kamaninta da tamu Alheran din?"
"Dalilin da yasa na ganeta ma kenan"
Tana wannan leken taji an kamo hannunta an ja ta gaba. Zata yi magana ta ga Emzee ne. Ita fa bata san da wasu baki ba Hammanta tazo gani. Yana rike da ita bai saketa ba sai a gabansu. Kanta ne ya nemi juyewa dama ga yara sun yanyame motocin saboda kyaunsu ga kuma su kansu mutanen da yawa suna ta fitowa daga mota. Kukan Mammee da ta rungumeta har yafi na dazu domin yadda Radhiya take diban yanayi sosai da yayarta. Murmushin da Radhiya tayi ya kara karya mata zuciya saboda lotsawar kumatun sak na yayarta ne.
Emzee yana yi mata bayani su ma suna ta yarensu suna dan hadowa da Hausa saboda jikokin nasu. Fada musu yayi su dan kara hakuri suka ce babu komai sun san gida ne na taro gashi ba'a san da zuwansu ba. Radhiya dai yau harda jin kunya yadda mutanen nan dukkansu suke ta rungumarta matan. Mazan ma ita dai taji wani ya kamo hannunta babba ne kuwa abokin wasan Zayyan sai dai kafin ta motsa taji wani tattausan hannu ya janyota baya sannan ya dawo gabanta ya tsaya tsakaninta da mutumin. Babu mai fahimtar mai Awwab yayi ko dalilinsa sai wanda yasan tsakaninsa sa Radhiya. Abinda yaji ya ratsa shi kuwa shima sai da yayi nadamar taba hannun nata. Daga inda yake tsaye yana kallon wannan runguma zuciyarsa ta tsinke da yaga mata sun kare kada a fara da maza. Kishin da ya yunkuro masa ba kadan bane. Allah ne Ya taimake shi ya taho da wuri yau da sai anyi abinda zai mutu bai manta ba, wato Alheran dinsa a jikin wani. Babu ruwansa da alakar dake tsakaninsu tunda ya tabbatar babu muharraminta ciki idan aka cire kakaninta biyu Alh Ghoumar da Alh Sidi. Sauran duk wanda ya tabata ya taba masa mata ne.
Ummi da kanta ta rufo mayafi ta leko kiransu. Mutane suna darewa wadannan jama'a guda wadanda dukkansu kowa ka kalla kasan ya taka wani abu a duniya na arziki mazansu da matansu suka shige inda aka nuna musu. Tabarmi ne sababbi manya aka shimfide musu suka zazzauna babu girman kai da jin su din wasu ne. Mammee ta rike Ummi tana ta sharar hawaye. Rabon da su hadu shekara goma shatara tun ranar sunan Alheran Radhiya.
Wurin minti goma ana ta matsar kwalla Ummi an fama mata rashin gwarzon namiji masoyin kwarai Zayyan uban 'ya'yanta.
"Mairama yaya bayan saduwa? Kiyi hakuri. Don Allah ke da 'ya'yan nan kuyi hakuri" Alh Sidi yace yana duban su duka su ukun.
Salame da kunya ta korota sashen mazan gidan nasu taci karo da wannan abin al'ajabi. Wurin gabadaya wani irin kamshi yake yi. Sakato tayi tana kallon mutanen. Maza biyu cikinsu wato su Alh Ghoumar sun dora rawaninsu na al'ada a kawunansu. Sauran kuwa sai ka rantse wasu larabawa ne. Buzaye ne gaba da baya da kudi ya kara gyarawa rayuwa suka kara fitowa. Bakinta bai iya neman abin fada ba na nuna mamaki taji muryar marainiyar wayonta Mairama.
"Don Allah ku dena bamu hakuri ba laifinku bane. Kaddara ce kawai da kuma abinda Kawun yaran nan yayi mana"
Kallo ta bita dashi suna zaune tsakiyar mutanen da ita da 'ya'yanta. Zuciyarta har wani girgiza tayi da ta kalli Emzee. Itama sai ya tuna mata da nata tsohon mikin na son mijin kanwarta. Babban abin da ya daure mata kai shine sanin da tayi Mairama ta makance suna kauye ita da gayyar yaranta. To tana ina ne ta warke kuma suka yi fes dasu ba yadda take tsammanin ganinsu ba? Ga wani kyakkyawan saurayi tsaye a gefe ya tokare kafarsa daya da bango shi kuma ko waye? Tambayoyi take ta yiwa kanta tana neman amsa ido rufe.
"Matsa a wuce" taji ance daga bayanta. Matsawar tayi kuwa aka fara shigowa da tray-tray na kayan abinci da abubuwan sha. Duk abinda za'a tanada Innawuro ce ta kwance gefen zaninta ta bada kudi masu yawa har su Yadikko sai da suka yi mamaki. Bafillatana tana zaune haka cikinsu ana dariya ashe dukiya ce a jikinta. An dibar musu cikin abincin bikin sannan aka siyo tsire da balangu mai yawa da lemukan roba da ruwa masu sanyi.
"Shiga ku gaisa mana 'yan uwan Marigayi ne daga Nijar" Hajjo tayi maganar tana wucewa ciki ita da su Nene Marka suka gaisa da bakin aka gabatar musu da abinci. Kamar zata hadiyi zuciya ta juya batare da ta cewa kowa uffan ba ta bar wurin. Su dinma babu wanda ya kula da ita suna murnar ganin juna.
"Bari mu baku wuri kuci abinci don Allah. An tafi kiran babana sai ku gaisa"
"Ki bar mana yaran idan tashi zaki yi"
Wata mata mai faram faram tace cikin hausar da tafi kama da ta Kanawa. Ilai kuwa ashe aure ne ya kaita Nijar ita ce amarya cikin matan Alh Sidi amma mutuniyar Kano ce.
Ummi tana murmushi tace dama wa ya aiketa. Inda Awwab yake tsaye ta kalla "dan Ummi zo muje kaci abinci"
"Bazai ci cikinmu ba? Tare muka taho shima bako ne" saurayin da suke magana dazu dashi yace yana dariya.
"Wannan naku ne kada ka damu dani" Radhiya ya kalla ta wani nutsu kamar ba ita ba "taso ki zuba min".
Ummi na jin haka tayi gaba abinta tana murmushi suka tashi aka basu wuri domin su samu su sake musamman mazan. Emzee ne kawai bai tashi ba yana aikin amsa musu tambayoyin da suke yi masa game da rayuwarsu.
Kofar da zata fitar dashi waje Awwab ya bi ba wadda zata sada shi da ainihin tsakar gidan ba. Radhiya sai tabi bayansa suka fito yayi hanyar inda ya ajiye tasa motar. Baya ya bude mata babu musu ta zauna shima ya zauna a gaba bangaren dreba kafafunsu suna waje. Lallen kafarta ya kalla ta saka daya daga cikin takalman da ya kawo mata tayi matukar kyau.
"Shigar da kafarki ciki"
Zumbura masa baki tayi sannan ta dauke kafafun.
"Me yasa kika dena daukar wayata yau kwana biyu?" Ya tambayeta da wannan deep voice din tasa.
Shagwabe fuska tayi kafin tace "to ba kaine ka dena kirana ba saboda ka koma Katsina wurin....wurin"
Fada yaso yi mata na hora shi da tayi ta hana shi jin daddadar muryarta idan tana shagwaba ko ta hado wani shirmen nata sai ya kasa. Ganinta kawai da yadda tayi masa kyau ya kawar da komai.
"Wurin wa?"
Harara ta galla masa tana juya idanu ita anyi mata laifi sai dai gabadaya abin da tayi sauke masa kasala yayi "ai ka fini sanin wa nake nufi. Wurin My G mana ni kuma ka manta dani"
Bushewa yayi da dariya damuwarsa ta ragu sosai. Babu wani abu da yake tunani sama da mallakar wannan yarinyar da take gabansa a matsayin matar aurensa.