Sashe 125
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ta rinka cewa bata je ba yana cewa sai ta fada masa gaskiya. Nan aka fara kiran sallah ya fita kamar ya tafi da ita. Ciki ta wuce ana ta layin alwala a waje mazan ma suna nasu.
Gidan sai bayan isha ya dan daidaita inda Daada da su Daddy da iyalansu suka zauna a falonsa suna hira. Mama ce tace ita dai sai ta bude gift din DK daga bangaren da matan suke zaune yaran nasu suka soma murna suna jira a bude. Mami ce ta farke abin suka ga takardu ne a ninke. Ta bude ta karanta tana wani irin murmushi ta mikawa Mama. Ita kam hawaye ne ya zubo mata na farinciki Baba Hadir na kallonsu yace "Zainab?" Da alamar tambaya yaji me ya faru.
Ibrahim ta bawa takardun yaje ya mika masa falon yayi shiru sai da ya karanta ya kalli Zayyan.
"Yayi. Yawa" ya daure yace shima muryarsa na nuni da taba masa zuciya da abin yayi.
"Babu ruwanka da kyautar uba da da kuyi mana addu'a Allah Yasa yaci gajiyarsa."
Amin kowa yace ana mamakin Zayyan ya mallakawa Zayyan Hadir gidansa na Kano. Wannan ya biyo bayan dogon nazarinsu shi da Ummi sun san cewa duka sunfi Hadir karfi yanzu kuma Daddy yana da gidan kansa a Katsina.
Mama ta karbi na Zayyana ta bude a take su ka bude baki da mamaki.
"Zayyan meye haka ne?" Daddy yace yana kallon dankareren saitin gwal din da ya mallakawa Zayyana. Dankunne, sarka hade da zube da manyan abin hannu guda biyu iri daya biyu iri daya na kudi har dubu dari biyar.
"Kada ku shiga tsakanina da 'ya'yana ba ku na bawa ba"
Mami ta share kwalla tana jinjinawa zumunci irin na Zayyan da matarsa mai goya masa baya.
Gift na karshe na Emzee mukullin mota ne sabuwa fil. Zayyan yace "waccan sai ta zama ta Ibrahim shi kadai. Allah Yayi muku albarka 'ya'yana"
Saidai ayi ta cewa amin domin babu sauran godiya a tsakanin wadannan iyalin. Kaya Zayyan ya chanja zuwa farare irin na Daddy da Baba Hadir ga matansu kayansu iri daya suka zauna akan 3 sitter mazan a tsaye kowa a bayan matarsa aka dauki hoton tarihi na iyali uku masoyan juna.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: *KUYI HAKURI DA RASHIN YAWANSA BANA JINDADI NE YAU. NAGODE*
Idanun Salame sunyi zuru-zuru saboda asirinta da wadannan 'ya'yan na Mairama suka sani. Daga nan kuma bata san yaya za ta kare ba. Radhiya kashe wayarta tayi bayan ta gama magana da Emzee ta koma kallon Salame tana ta hawaye.
"Me Ummi tayi miki Gwaggo? Mata nawa ne suka taba son wani Allah bai kaddari zamansu tare ba kuma suka hakura?" Matsowa ta rinka yi inda Salame ke tsaye gumi na karyo mata. Wannan shi ake cewa kada Allah Ya kaimu ranar da za'a tsare mutum ana masa tambaya akan laifukan da ya binne. Ya Allah Ka rabamu da hisabi irin wannan da za'a tono komai da komai da muka taba aikatawa a rayuwarmu domin WALLAHI da matukar wahala mu haye.
Kuka Radhiya take yi amma muryarta kowa naji a cikin gidan saboda karshe ranta ya kai kuloluwar baci "Kinsan tsananin da yake tattare da makanta kuwa? A lokacin Ummi ta rayu ba miji ga marayu sannan babu wadatar abincin da zata ci ta ciyar da yaranta. Gwaggo kina kallo sai da ta sayar da duk wani abu da ta mallaka muka dena karatu saboda neman magani." Kukanta ya kara tsanami ta matse kirjinta "sau nawa....sau nawa ina rokon Ummi ta barni nayi bara ko talla saboda bama koshi da abincin gidan Malamijo tana hanawa. Ba don Allah Ya dube mu su Innawuro sun zo ba kina jin da watarana bazata amince ba ko don kada yunwa tayi mana lahani. Sai Allah Ya sakawa Ummi Gwaggo" ta kare da fashewa da wani irin kuka. Rabonta da kuka sosai irin haka tun ranar da Ummi tace kada ta amsa cewar tana son Awwab. Yau ga abinda yafi rabuwa da Awwab kaji ko ka ga mutumin da baya kaunar mahaifiyarka kuma yake neman ganin bayanta.
Jiki na rawa ga tsoro amma Salame bata so ta nunawa Radhiya sai cewa tayi "idan kin gama sharrin sai ki fita ki tafi in kuma zaki rama mata ne to na fara jin didif a jikina sai na san cewa kin haifu"
Kallon da Radhiya tayi mata da jajayen idanunta kallo ne mai firgitarwa da nuna kwarewa wurin fitina da sanin yadda zaka rama abu cikin ruwan sanyi.
"Ummi tayi mana tarbiya wadda ni ko Emzee bazamu taba watsa mata kasa a ido ba in sha Allah. Gwaggo Salame ke ba sa'ar yi na bace domin kin girmi mahaifiyata ma...amma.... zan hadaki da wanda yafi cancanta ya hukunta ki" tana kaiwa nan ta daga waya ta soma kiran mahaifinta Zayyan Tureta.
Duk wannan abu da suke yi Alh Indararo da Maman Danmama suna kofar dakin sai dai su basu kula da tsayuwarsu ba sannan shima yana so ya gama gane kan zancen kafin ya afkawa Salame.
A can hostel dinsu kuma Emzee bayan ya gama nasa kukan shima babu wanda yake so da burin saukewa nauyin zuciyarsa sai mahaifinsa. A take shima ya soma kiran wayar Zayyan din.
**********
Yana zaune a dakin Jume kan tabarma yana cin abincin da ta dafa masa da kanta suna hira. Abin mamakin da ya gani bai wuce sabon fenti ba ciki da wajen gidan ana ta gyare gyare wanda yawanci jikokin gidan samari keyi.
"Wai ni wannan gyaran Jume waye zaiyi amarya ne?" Zayyan ya tambayeta yana dariya.
" 'Yan uwanka ne suke son yin gyara saboda bikin Alheran mana. Ita ce fa jikar farko ta bangaren namiji a gidan nan ka ga kuwa mune da biki"
Dadi yaji sosai "Allah Ya saka da alkhairi Jume nagode"
Dan harararsa tayi "meye haka kamar wanda aka yiwa wani abu. Kai dai ka gama ci ga 'ya kayayyaki can da suka hadawa amarya."
"Harda wata wahala kuma?"
"Ashe ba 'yarsu bace indai abinda suka yi sunansa wahala"
Saurin bata hakuri yayi ya gama cin abincin sannan ya mika mata wata leda mai kauri. Budewa yayi ya dauko kullin kudi guda uku kowanne dubu dari biyar biyar yace gashi nan ta bawa yayunsa Badaru, Rayyan da Maikudi. Sannan ya dauko kananun kullin su kuma dubu dari bibbiyu ne yace na matan ne su ma su uku. Wannan duk cikin kudin da aka bashi ne wanda yake ganin idan bai nemi lada ya raya zumunci dasu ba yayi asara kuma bai godewa Allah da ya dawo dashi gida lafiya ba.
Jume sai kwalla tasa zani ta goge "Zayyanu da wane bakin zanyi maka godiya kuma in cigaba da rokon yafiya akan zaluncin da nayi maka?"
Baya son tana yi masa haka domin uwa ya dauketa "kisa min albarka kawai Jume abar maganar. In Allah Ya yarda ke kuma hajjin wannan shekarar zamu je dake da Mairama"
"Ayya...ayya Zayyanu...Allah Ya jikan Innarka da Malam. Na cutar da baiwar Allahn nan ashe nice da moriyar danta" tace tana kuka sosai. Cikin wanda ta ya fara bata na dubu dari biyar din ta dauko ta mika masa kuma tana sane saboda ta gano Maikudi ya taho dakin amma ya tsaya daga waje saboda ya hango Zayyan.
"Wannan ka rike kayanka Zayyanu don wallahi ko kwabo bazan baiwa Maikudi ba."
Da sauri Zayyan yake dubanta "haba Jume me yayi zafi haka?"
"Komai ma. Zayyanu komai da komai yayi zafi daga lokacin da Maikudi ya danne dukiyar marayu sannan saboda bakin hali da tsantsar mugunta ya aika da sakon mutuwarsu har Nijar ya dakile masu tallafa musu"
Maikudi yana daga waje yaji kamar ya rafka ihu. Shigowa yayi ya rakube a gefe ya durkusa amma ya kasa cewa Jume da kanin nasa komai. Ita kuwa kallon banza take masa saboda irin abubuwan da yayi da irin yadda itama ya rainata.
"Saboda kaji ana zancen kudi shine ka taho ko? Ka gani..." tace tana dorawa Zayyan kudinsa "to na bashi kayansa ban kuma lamunce ya baka ba ko da a bayan idona ba. Yau ba don dawowar abokansa ba ina da yakinin haka za ka yi ta gina kanka da dukiyarsu batare da nadama ba"
Zayyan kama bakinsa yayi tunda ita da danta sunfi kusa. Ba don zumunci domin Allah ake yinsa ba ko inuwar Maikudi bazai sake kallo ba. Mutumin da baiji tausayin matar da akace mijinta ya rasu ba ga danyen jego. Mutumin da yayi amfani da emotional sentiment din Mairama yasa ta hakura da takardun gidan mijinta akan wasikar da ya bar mata kafin ya tafi. Zumunci akwai dadi akwai wahala sai mutum ya daure ya kai zuciyarsa nesa.
Wayarsa yaji tana vibrating ya dauko sai lokacin ya kula da missed call din Radhiya da na Emzee. Tashi yayi ya saka kudinsa a aljihu yace da Jume yana zuwa. Wurin dakin Innarsa yaje ya tsaya zai kirasu Maikudi ya biyo shi da sauri. Dukar da kai yayi saboda mugun kwarjinin da Zayyan yayi masa.
"Yaya akayi?" Zayyan yace da dakakkiyar murya.
Kamar wanda aka tsuma a cikin ruwa don kunya Maikudi ya dago kai yana hada hannuwa "Zayyan ka duba girman zumunci..."
"Wannan ka biyo kenan Maikudi..." ya zura hannu ya dauko kudin ya mika masa "gashi na riga nayi niyya dama"
Ja baya Maikudi yayi "ba kudinka nake so ba Zayyan. Nasan akwai kunya in kalli idanunka ko na iyalinka in roki gafara amma ku taimaka don Allah. Kawu Aminu yace dama akwai ranar da zanji kunya gashi ko shekara baiyi a kasa ba lokacin yazo"
Zayyan yaji wayarsa ta sake vibrating kallo daya ya yiwa Maikudi yace " 'ya'yana suna bukata ta zamuyi magana anjima"
Bai jira cewarsa ba ya daga wayar gabansa ya fadi saboda jin muryar Radhiya tana kuka.
"Daada" tace lokaci guda tana kara sautin kukanta.
Faduwar gaba yaji sosai da sauri ya rinka watsa mata tambayoyi "Alheran menene? Ina Umminku? Me ya faru?"
Gidan sai bayan isha ya dan daidaita inda Daada da su Daddy da iyalansu suka zauna a falonsa suna hira. Mama ce tace ita dai sai ta bude gift din DK daga bangaren da matan suke zaune yaran nasu suka soma murna suna jira a bude. Mami ce ta farke abin suka ga takardu ne a ninke. Ta bude ta karanta tana wani irin murmushi ta mikawa Mama. Ita kam hawaye ne ya zubo mata na farinciki Baba Hadir na kallonsu yace "Zainab?" Da alamar tambaya yaji me ya faru.
Ibrahim ta bawa takardun yaje ya mika masa falon yayi shiru sai da ya karanta ya kalli Zayyan.
"Yayi. Yawa" ya daure yace shima muryarsa na nuni da taba masa zuciya da abin yayi.
"Babu ruwanka da kyautar uba da da kuyi mana addu'a Allah Yasa yaci gajiyarsa."
Amin kowa yace ana mamakin Zayyan ya mallakawa Zayyan Hadir gidansa na Kano. Wannan ya biyo bayan dogon nazarinsu shi da Ummi sun san cewa duka sunfi Hadir karfi yanzu kuma Daddy yana da gidan kansa a Katsina.
Mama ta karbi na Zayyana ta bude a take su ka bude baki da mamaki.
"Zayyan meye haka ne?" Daddy yace yana kallon dankareren saitin gwal din da ya mallakawa Zayyana. Dankunne, sarka hade da zube da manyan abin hannu guda biyu iri daya biyu iri daya na kudi har dubu dari biyar.
"Kada ku shiga tsakanina da 'ya'yana ba ku na bawa ba"
Mami ta share kwalla tana jinjinawa zumunci irin na Zayyan da matarsa mai goya masa baya.
Gift na karshe na Emzee mukullin mota ne sabuwa fil. Zayyan yace "waccan sai ta zama ta Ibrahim shi kadai. Allah Yayi muku albarka 'ya'yana"
Saidai ayi ta cewa amin domin babu sauran godiya a tsakanin wadannan iyalin. Kaya Zayyan ya chanja zuwa farare irin na Daddy da Baba Hadir ga matansu kayansu iri daya suka zauna akan 3 sitter mazan a tsaye kowa a bayan matarsa aka dauki hoton tarihi na iyali uku masoyan juna.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: *KUYI HAKURI DA RASHIN YAWANSA BANA JINDADI NE YAU. NAGODE*
Idanun Salame sunyi zuru-zuru saboda asirinta da wadannan 'ya'yan na Mairama suka sani. Daga nan kuma bata san yaya za ta kare ba. Radhiya kashe wayarta tayi bayan ta gama magana da Emzee ta koma kallon Salame tana ta hawaye.
"Me Ummi tayi miki Gwaggo? Mata nawa ne suka taba son wani Allah bai kaddari zamansu tare ba kuma suka hakura?" Matsowa ta rinka yi inda Salame ke tsaye gumi na karyo mata. Wannan shi ake cewa kada Allah Ya kaimu ranar da za'a tsare mutum ana masa tambaya akan laifukan da ya binne. Ya Allah Ka rabamu da hisabi irin wannan da za'a tono komai da komai da muka taba aikatawa a rayuwarmu domin WALLAHI da matukar wahala mu haye.
Kuka Radhiya take yi amma muryarta kowa naji a cikin gidan saboda karshe ranta ya kai kuloluwar baci "Kinsan tsananin da yake tattare da makanta kuwa? A lokacin Ummi ta rayu ba miji ga marayu sannan babu wadatar abincin da zata ci ta ciyar da yaranta. Gwaggo kina kallo sai da ta sayar da duk wani abu da ta mallaka muka dena karatu saboda neman magani." Kukanta ya kara tsanami ta matse kirjinta "sau nawa....sau nawa ina rokon Ummi ta barni nayi bara ko talla saboda bama koshi da abincin gidan Malamijo tana hanawa. Ba don Allah Ya dube mu su Innawuro sun zo ba kina jin da watarana bazata amince ba ko don kada yunwa tayi mana lahani. Sai Allah Ya sakawa Ummi Gwaggo" ta kare da fashewa da wani irin kuka. Rabonta da kuka sosai irin haka tun ranar da Ummi tace kada ta amsa cewar tana son Awwab. Yau ga abinda yafi rabuwa da Awwab kaji ko ka ga mutumin da baya kaunar mahaifiyarka kuma yake neman ganin bayanta.
Jiki na rawa ga tsoro amma Salame bata so ta nunawa Radhiya sai cewa tayi "idan kin gama sharrin sai ki fita ki tafi in kuma zaki rama mata ne to na fara jin didif a jikina sai na san cewa kin haifu"
Kallon da Radhiya tayi mata da jajayen idanunta kallo ne mai firgitarwa da nuna kwarewa wurin fitina da sanin yadda zaka rama abu cikin ruwan sanyi.
"Ummi tayi mana tarbiya wadda ni ko Emzee bazamu taba watsa mata kasa a ido ba in sha Allah. Gwaggo Salame ke ba sa'ar yi na bace domin kin girmi mahaifiyata ma...amma.... zan hadaki da wanda yafi cancanta ya hukunta ki" tana kaiwa nan ta daga waya ta soma kiran mahaifinta Zayyan Tureta.
Duk wannan abu da suke yi Alh Indararo da Maman Danmama suna kofar dakin sai dai su basu kula da tsayuwarsu ba sannan shima yana so ya gama gane kan zancen kafin ya afkawa Salame.
A can hostel dinsu kuma Emzee bayan ya gama nasa kukan shima babu wanda yake so da burin saukewa nauyin zuciyarsa sai mahaifinsa. A take shima ya soma kiran wayar Zayyan din.
**********
Yana zaune a dakin Jume kan tabarma yana cin abincin da ta dafa masa da kanta suna hira. Abin mamakin da ya gani bai wuce sabon fenti ba ciki da wajen gidan ana ta gyare gyare wanda yawanci jikokin gidan samari keyi.
"Wai ni wannan gyaran Jume waye zaiyi amarya ne?" Zayyan ya tambayeta yana dariya.
" 'Yan uwanka ne suke son yin gyara saboda bikin Alheran mana. Ita ce fa jikar farko ta bangaren namiji a gidan nan ka ga kuwa mune da biki"
Dadi yaji sosai "Allah Ya saka da alkhairi Jume nagode"
Dan harararsa tayi "meye haka kamar wanda aka yiwa wani abu. Kai dai ka gama ci ga 'ya kayayyaki can da suka hadawa amarya."
"Harda wata wahala kuma?"
"Ashe ba 'yarsu bace indai abinda suka yi sunansa wahala"
Saurin bata hakuri yayi ya gama cin abincin sannan ya mika mata wata leda mai kauri. Budewa yayi ya dauko kullin kudi guda uku kowanne dubu dari biyar biyar yace gashi nan ta bawa yayunsa Badaru, Rayyan da Maikudi. Sannan ya dauko kananun kullin su kuma dubu dari bibbiyu ne yace na matan ne su ma su uku. Wannan duk cikin kudin da aka bashi ne wanda yake ganin idan bai nemi lada ya raya zumunci dasu ba yayi asara kuma bai godewa Allah da ya dawo dashi gida lafiya ba.
Jume sai kwalla tasa zani ta goge "Zayyanu da wane bakin zanyi maka godiya kuma in cigaba da rokon yafiya akan zaluncin da nayi maka?"
Baya son tana yi masa haka domin uwa ya dauketa "kisa min albarka kawai Jume abar maganar. In Allah Ya yarda ke kuma hajjin wannan shekarar zamu je dake da Mairama"
"Ayya...ayya Zayyanu...Allah Ya jikan Innarka da Malam. Na cutar da baiwar Allahn nan ashe nice da moriyar danta" tace tana kuka sosai. Cikin wanda ta ya fara bata na dubu dari biyar din ta dauko ta mika masa kuma tana sane saboda ta gano Maikudi ya taho dakin amma ya tsaya daga waje saboda ya hango Zayyan.
"Wannan ka rike kayanka Zayyanu don wallahi ko kwabo bazan baiwa Maikudi ba."
Da sauri Zayyan yake dubanta "haba Jume me yayi zafi haka?"
"Komai ma. Zayyanu komai da komai yayi zafi daga lokacin da Maikudi ya danne dukiyar marayu sannan saboda bakin hali da tsantsar mugunta ya aika da sakon mutuwarsu har Nijar ya dakile masu tallafa musu"
Maikudi yana daga waje yaji kamar ya rafka ihu. Shigowa yayi ya rakube a gefe ya durkusa amma ya kasa cewa Jume da kanin nasa komai. Ita kuwa kallon banza take masa saboda irin abubuwan da yayi da irin yadda itama ya rainata.
"Saboda kaji ana zancen kudi shine ka taho ko? Ka gani..." tace tana dorawa Zayyan kudinsa "to na bashi kayansa ban kuma lamunce ya baka ba ko da a bayan idona ba. Yau ba don dawowar abokansa ba ina da yakinin haka za ka yi ta gina kanka da dukiyarsu batare da nadama ba"
Zayyan kama bakinsa yayi tunda ita da danta sunfi kusa. Ba don zumunci domin Allah ake yinsa ba ko inuwar Maikudi bazai sake kallo ba. Mutumin da baiji tausayin matar da akace mijinta ya rasu ba ga danyen jego. Mutumin da yayi amfani da emotional sentiment din Mairama yasa ta hakura da takardun gidan mijinta akan wasikar da ya bar mata kafin ya tafi. Zumunci akwai dadi akwai wahala sai mutum ya daure ya kai zuciyarsa nesa.
Wayarsa yaji tana vibrating ya dauko sai lokacin ya kula da missed call din Radhiya da na Emzee. Tashi yayi ya saka kudinsa a aljihu yace da Jume yana zuwa. Wurin dakin Innarsa yaje ya tsaya zai kirasu Maikudi ya biyo shi da sauri. Dukar da kai yayi saboda mugun kwarjinin da Zayyan yayi masa.
"Yaya akayi?" Zayyan yace da dakakkiyar murya.
Kamar wanda aka tsuma a cikin ruwa don kunya Maikudi ya dago kai yana hada hannuwa "Zayyan ka duba girman zumunci..."
"Wannan ka biyo kenan Maikudi..." ya zura hannu ya dauko kudin ya mika masa "gashi na riga nayi niyya dama"
Ja baya Maikudi yayi "ba kudinka nake so ba Zayyan. Nasan akwai kunya in kalli idanunka ko na iyalinka in roki gafara amma ku taimaka don Allah. Kawu Aminu yace dama akwai ranar da zanji kunya gashi ko shekara baiyi a kasa ba lokacin yazo"
Zayyan yaji wayarsa ta sake vibrating kallo daya ya yiwa Maikudi yace " 'ya'yana suna bukata ta zamuyi magana anjima"
Bai jira cewarsa ba ya daga wayar gabansa ya fadi saboda jin muryar Radhiya tana kuka.
"Daada" tace lokaci guda tana kara sautin kukanta.
Faduwar gaba yaji sosai da sauri ya rinka watsa mata tambayoyi "Alheran menene? Ina Umminku? Me ya faru?"