Sashe 50
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hanjin cikin Maikudi ya buga wani uban sauti shi ba na yunwa ba shi ba na lalacewar ciki ba. Kallonsu yake tsakanin Major Mustapha da Captain Onomza wanne ne zaifi dan dama dama wurin sassauci. Yawun bakinsa duk ya kafe ya laso lebe ga gumi ya fara jika shi. Muryarsa kamar an takewa muzuru jela da takalmin karfe yace da Major "me yayi zafi ne haka ranka ya dade? Yarinyar nan da kaina zan kaika garin da suke. Ko makon da ya gabata naje na fada musu kazo kana nemansu shine uwar tace babu inda zasu je. To amma yanzu tunda anyi haka ina maka rantsuwa irin ta addinin Islama ko a ka ne zan dauko Radhiya na kawo maka. Kai harda kanin nata Zayyanu."
Gigitacciyar tsawar da Captain Onomza ya daka masa ita ta janyo mararsa ta saki fitsari ya soma tsartuwa. Mutane har sun fara fitowa kallo tunda sun fuskanci an kama wanda aka zo dominsa.
"Nine ka yiwa kerya yace min wife na Lt Zayyan yayi aure, baby ya mutu and you have the girl with you. Ko ba anyi haka ba"
Idanun Maikudi kamar an kasa kwai a faranti sunyi tsilli tsilli yace "ni ban fahimci me kake cewa bare na baka amsa"
Wawan mari ya dauke Maikudi dashi sai ji kake garam-garam masu leke suna komawa inda suka fito ana rufe kofofi. Captain Onomza da ko cikin sojojin ma ana tsoronsa saboda baya sassautawa mara gaskiya shine Maikudi zai kawowa wargi.
A take habo ya kama Maikudi. Major ya kawar da kansa su Baffa jiki ya hau tsuma. Da sunsan abin zai hada da sojoji babu abinda zai fito dasu daga rugarsu.
"Ka fahimta wanna ko"
"Kuyi hakuri yallabai yanzu me kuke bukata?"
"Bundle him up"
Mutum biyu ne suka taho kan Maikudi aka cukwikuye shi guda ya saba shi a kafada yayi gaba dashi.
Major da Captain Onomza suka sake gaisawa Captain din yace zai kira shi ya tabbatar masa a daren yau kafin gari ya waye Maikudi zai fadi ina kudaden marayun suke. Gidansu na Kano ma zai fadi me yayi dashi haka zalika idan yana da hannu a dauke kafar da 'yan uwan Innar Zayyan suka yi shima duk zai fada da bakinsa. Da sassarfa suka bar lungun sannan Major yace su shiga gidan.
Jume bata yi mamaki ba bayan ya gama mata bayanin me aka yiwa dan nata.
"Yanzu sai yaushe zaku sake shi?" Ta tambaya cike da jimami ga matarsa da yara suna kuka don labari ya iso gidan tun kafin shigarsu ma.
"Sati daya zaiyi in sha Allah"
"Yanzu babu wani abu da zaku iya yi a fitar dashi?"
Wani murmushi Major yayi da ya tabbatar musu babu wani abu da zasu yi da zai sa ya fito da Maikudi. Dole Jume taji babu dadi amma dan nata yana bukatar saiti ita kanta ta sani. Su Major sun tafi akan idan da wani abu zai nemesu.
"Uhmm nace ko zaka nemi Mal.Aminu. Aminin Malam ne da suke zuwa Nijar din tare, dashi akayi komai na auren Malam din da ita Innar Zayyanu"
Godiya Major yayi mata suka rabu zasu dawo washegari a raka su gidan Mal. Aminu.
Captain Onomza baiyi sanya ba wurin ganin Maikudi ya samu tarba irin wadda ta dace da macuta irinsa. A wannan daren ya bambance aya da tsakuwa, ya gane waye soja da hatsarin dake tattare da shiga hurumin sojoji ko da a bayan ransu ne. Mutane ne masu hadin kai da tsayawa juna domin kare martabarsu koda a bayan idanunsu ne. Abinda ya kara tunzura Captain Onomza shine takaicin ace dan uwa na jini ne da wannan muguntar. Kuma ya rasa wa zai ha'inta sai iyalin Zayyan dinsu.
**********
Matafiya suna ta shiri an gama wanka da cin abinci. Ummi da Mami ake jira basu gama hirar da suka dauko ba bayan wayar da suka gama da Mama Zainab. Zuwansu asibiti jiya likitan da suke gani ya gama bincike akan likitocin da ake kira neurosurgeons inda cikin sa'a ya sami wani kwararre da zai je Kuwait sati biyu masu zuwa. Likitan dan asalin kasar Philippines kusan yawo yake kasa kasa yana duba patients. Matsalar dai bata wuce samun shiga gurbin appointment dinsa ba karamin abu bane. Yini guda suna ta cuku cuku aka cusa Hadir a matsayin patient na karshe da zai gani a wani babban asibiti a Kuwait. Ba komai yaja hankalinsa ya karbe shi ba sai dadewar da Hadir yayi da lalurar da kuma jin cewa soja ne da ya sami rauni a filin daga. Tsananin rabo da addua suka sami alfarmar nan. Kudi dai Zainab zata kashe ba na wasa ba abu ya tasarwa miliyan tara. Zuciyarta ta karye hankalinta ya tashi. Idan ta bayar da wannan kudaden hakika zata tagayyara jarinta. Allah Ya taimaketa akwai kayan da tayi order daga China dake kan ruwa da basu sauka ba. Sune zasu riketa idan tayi sa'ar kasuwa.
Mami ta kwantar mata da hankali za ta sanar da Major domin nauyin ba nata bane ita kadai. Ummi bata bata lokaci ba itama wurin neman Innawuro a waya. Shanu biyar cikin abinda iyayen nata suka bata bayan ta koma hannunsu manya manya ta roki alfarmar a saka a kasuwa a ga nawa zasu samu. Dama ajiyarsu take saboda karatun 'ya'yanta da auren Radhiya idan ya taso.
"Abinda za'ayi Mami ku tafi da Karami domin su hadu da Ibrahim su taimaka mata. Bikin namu na kwana daya ne ana kai amaren washegari zamu tafi Kanon mu jira har su tashi"
"Baiwar Allah wallahi ina tausayin Zainab. Hadir ya godewa Allah bana jin zai taba haduwa da matar da zata kaunace shi rabi rabin yadda Zainab take yi"
Murmushi Mairama tayi ta bata labarin da Zayyan ya bata tun yana raye na ainihin waye saurayin Zainab din. Sun sha dariya su biyun yadda abotar su ta kasance.
Kowa ya shirya sun fara fitowa amma babu Radhiya har Mami sai da tayi cigiya.
"Tana kwance inda tayi sallar asuba tana bacci"
"Bacci kuma?" Mairama tace tana mamaki don Radhiya ba mai baccin safe bace musamman ma dai na yau da su Mami zasu koma.
"Taso ta Fauziyya tazo kuyi sallama"
Mami tayi saurin hanata "A'a wallahi ku dauko kayanku mu tafi. Nasan bai wuce gajiya ba"
Kusan kwana tayi tana kukan hotunan wayar Awwab. Duk da ya goge takaici take don me yasa ya tsaya har mace ta saka masa abinci a baki. Wannan ma salon ya jawo musu zagi ne ace yayanta bashi da kamun kai. Ko mutum nawa ne suka gani? Mata nawa ya bawa ko suka bashi abinci a baki? Alawar da ya bata ma sai da ta tuna ko sun taba yin haka da wata kafin ita. Wannan yafi tsaya mata a rai taci kuka ta godewa Allah shine fa bacci yayi awon gaba da ita da asuba.
Ghazalatu dama jira take kowa ya fita daga dakin ta zauna kamar tana gyara daurin dankwali. Zahra na fita ta fiddo wayarta taje ta zame hijabin Radhiya da babu dankwali ta kasansa a hankali wani bangare na kan ta ya bayyana tayi saurin daukarta a hoto tana kunshe dariyarta. Awwab zata nunawa kawai don ta rage karfin alakarsu duk ta yadda ya samu.
Awwab da yasan yadda ya rabu da kanwar tasa ya shigo tsakar gidan ya kai sau biyar ko zai ga gilmawarta. Da yaji ance bacci take yi hankalinsa tashi yayi fiye da zatonsa. Ta yaya zai tafi bai sake ganinta ba sai nan da sati biyu. Walwalar fuskarsa gabadaya ta bace yana jin kansa sukuku suka fito. Rakiya harda Malamijo shima yana cigiyar jikarsa mai fitina akace tana bacci.
"Kun taba jikinta kuwa lafiya take babu zazzabi? 'Yar sojan ce zata yi bacci har goma na safe indai ba kwaya ta soma sha ba". Dariya ya basu sosai.
"Mami ko dai bata da lafiyar? Hancinta na gani yayi swelling da saman idonta" inji Zayyana.
Ummi tace "ko ma meye ku bari su tafi a taso ta don yanzu tana zuwa sai ta bata musu lokaci"
Ba dai kukan ta sake yi ba Awwab ya tambayi zuciyarsa. Tamkar kada su tafi haka ya rinka ji. Ghazalatu motarsu ta koma Zahra ta shiga wadda su Mami suka zo don kada a barta ita daya.
Kusan awa daya da tafiyarsu bayan Radhiya ya soma damunta saboda kwanciyar kasa ta bude ido tana mika. Dakin shiru babu kowa ta tashi da sauri babu jakunkunansu sun gyare dakin da katifar. Nauyin bacci gareta shiyasa bata ji motsinsu ba. Gabanta na dukan uku-uku ta garzaya dakin Hajjo wurin Ummi.
"Ummi sun tafi ne?" Tace cikin tashin hankali.
"Ina hankalinki ne, babu sallama babu gaisuwa"
Fita tayi ta dawo cikin sauri ta gyara kuskurenta sannan ta maimaita tambayar da ta riga tasan amsarta tunda bata ga Mami ba kuma babu kayanta.
"Sun tafi kina can kina bacci. Ko baki da lafiya ne?"
Hawaye ne ya taho mata tayi kokarin boyewa "shine basu tashe ni ba?"
"Kiji dadin isarsu da surutu ba. Sun wuce da Karami zai zauna a Kano..."
Alamun kukan Radhiyan taji ta dakata tare da mika hannu inda take jin sautin tun yana tashi a hankali har yayi karfi. Wani irin kunci da bacin rai take ji hade da gagarumar kewar Hamma Awwab. Me yasa bai ce a tasheta ba sunyi sallama. Me yasa daga zuwansa zuciyarta take shiga mabambantan yanayi daga tsananin farinciki sai bacin rai irin na jiya da ta ganshi da mata. Yau kuma don bai damu da ita ba yayi tafiyarsa.
"Ke menene?"
"Ummi ba komai" ta amsa muryarta na sake karyewa. Ta dauki kanta jarumar mace mai dauriya amma lokaci kalilin ta zubar da hawaye fiye da tunaninta. Ita kanta bata san me ya sameta ba sai an mata karin bayani.
Tun Ummin ta na rarrashi har ta koma fada amma taki cewa komai sai kuka. Daga karshe karamar wayar da Mami ta bar mata ta dauko. Ba kudin sayen bane dama ta rasa sai dai karancin wadanda zata kira. Emzee da Radhiya kuwa taki saya musu ne duk da tasan ana yayinta sosai tana jiran su gama sakandire.
"Ungo ki kira Mami da sauran 'yan uwanki ku gaisa kiyi musu sallama kinji 'Yar sojan Daaadaa"
Gigitacciyar tsawar da Captain Onomza ya daka masa ita ta janyo mararsa ta saki fitsari ya soma tsartuwa. Mutane har sun fara fitowa kallo tunda sun fuskanci an kama wanda aka zo dominsa.
"Nine ka yiwa kerya yace min wife na Lt Zayyan yayi aure, baby ya mutu and you have the girl with you. Ko ba anyi haka ba"
Idanun Maikudi kamar an kasa kwai a faranti sunyi tsilli tsilli yace "ni ban fahimci me kake cewa bare na baka amsa"
Wawan mari ya dauke Maikudi dashi sai ji kake garam-garam masu leke suna komawa inda suka fito ana rufe kofofi. Captain Onomza da ko cikin sojojin ma ana tsoronsa saboda baya sassautawa mara gaskiya shine Maikudi zai kawowa wargi.
A take habo ya kama Maikudi. Major ya kawar da kansa su Baffa jiki ya hau tsuma. Da sunsan abin zai hada da sojoji babu abinda zai fito dasu daga rugarsu.
"Ka fahimta wanna ko"
"Kuyi hakuri yallabai yanzu me kuke bukata?"
"Bundle him up"
Mutum biyu ne suka taho kan Maikudi aka cukwikuye shi guda ya saba shi a kafada yayi gaba dashi.
Major da Captain Onomza suka sake gaisawa Captain din yace zai kira shi ya tabbatar masa a daren yau kafin gari ya waye Maikudi zai fadi ina kudaden marayun suke. Gidansu na Kano ma zai fadi me yayi dashi haka zalika idan yana da hannu a dauke kafar da 'yan uwan Innar Zayyan suka yi shima duk zai fada da bakinsa. Da sassarfa suka bar lungun sannan Major yace su shiga gidan.
Jume bata yi mamaki ba bayan ya gama mata bayanin me aka yiwa dan nata.
"Yanzu sai yaushe zaku sake shi?" Ta tambaya cike da jimami ga matarsa da yara suna kuka don labari ya iso gidan tun kafin shigarsu ma.
"Sati daya zaiyi in sha Allah"
"Yanzu babu wani abu da zaku iya yi a fitar dashi?"
Wani murmushi Major yayi da ya tabbatar musu babu wani abu da zasu yi da zai sa ya fito da Maikudi. Dole Jume taji babu dadi amma dan nata yana bukatar saiti ita kanta ta sani. Su Major sun tafi akan idan da wani abu zai nemesu.
"Uhmm nace ko zaka nemi Mal.Aminu. Aminin Malam ne da suke zuwa Nijar din tare, dashi akayi komai na auren Malam din da ita Innar Zayyanu"
Godiya Major yayi mata suka rabu zasu dawo washegari a raka su gidan Mal. Aminu.
Captain Onomza baiyi sanya ba wurin ganin Maikudi ya samu tarba irin wadda ta dace da macuta irinsa. A wannan daren ya bambance aya da tsakuwa, ya gane waye soja da hatsarin dake tattare da shiga hurumin sojoji ko da a bayan ransu ne. Mutane ne masu hadin kai da tsayawa juna domin kare martabarsu koda a bayan idanunsu ne. Abinda ya kara tunzura Captain Onomza shine takaicin ace dan uwa na jini ne da wannan muguntar. Kuma ya rasa wa zai ha'inta sai iyalin Zayyan dinsu.
**********
Matafiya suna ta shiri an gama wanka da cin abinci. Ummi da Mami ake jira basu gama hirar da suka dauko ba bayan wayar da suka gama da Mama Zainab. Zuwansu asibiti jiya likitan da suke gani ya gama bincike akan likitocin da ake kira neurosurgeons inda cikin sa'a ya sami wani kwararre da zai je Kuwait sati biyu masu zuwa. Likitan dan asalin kasar Philippines kusan yawo yake kasa kasa yana duba patients. Matsalar dai bata wuce samun shiga gurbin appointment dinsa ba karamin abu bane. Yini guda suna ta cuku cuku aka cusa Hadir a matsayin patient na karshe da zai gani a wani babban asibiti a Kuwait. Ba komai yaja hankalinsa ya karbe shi ba sai dadewar da Hadir yayi da lalurar da kuma jin cewa soja ne da ya sami rauni a filin daga. Tsananin rabo da addua suka sami alfarmar nan. Kudi dai Zainab zata kashe ba na wasa ba abu ya tasarwa miliyan tara. Zuciyarta ta karye hankalinta ya tashi. Idan ta bayar da wannan kudaden hakika zata tagayyara jarinta. Allah Ya taimaketa akwai kayan da tayi order daga China dake kan ruwa da basu sauka ba. Sune zasu riketa idan tayi sa'ar kasuwa.
Mami ta kwantar mata da hankali za ta sanar da Major domin nauyin ba nata bane ita kadai. Ummi bata bata lokaci ba itama wurin neman Innawuro a waya. Shanu biyar cikin abinda iyayen nata suka bata bayan ta koma hannunsu manya manya ta roki alfarmar a saka a kasuwa a ga nawa zasu samu. Dama ajiyarsu take saboda karatun 'ya'yanta da auren Radhiya idan ya taso.
"Abinda za'ayi Mami ku tafi da Karami domin su hadu da Ibrahim su taimaka mata. Bikin namu na kwana daya ne ana kai amaren washegari zamu tafi Kanon mu jira har su tashi"
"Baiwar Allah wallahi ina tausayin Zainab. Hadir ya godewa Allah bana jin zai taba haduwa da matar da zata kaunace shi rabi rabin yadda Zainab take yi"
Murmushi Mairama tayi ta bata labarin da Zayyan ya bata tun yana raye na ainihin waye saurayin Zainab din. Sun sha dariya su biyun yadda abotar su ta kasance.
Kowa ya shirya sun fara fitowa amma babu Radhiya har Mami sai da tayi cigiya.
"Tana kwance inda tayi sallar asuba tana bacci"
"Bacci kuma?" Mairama tace tana mamaki don Radhiya ba mai baccin safe bace musamman ma dai na yau da su Mami zasu koma.
"Taso ta Fauziyya tazo kuyi sallama"
Mami tayi saurin hanata "A'a wallahi ku dauko kayanku mu tafi. Nasan bai wuce gajiya ba"
Kusan kwana tayi tana kukan hotunan wayar Awwab. Duk da ya goge takaici take don me yasa ya tsaya har mace ta saka masa abinci a baki. Wannan ma salon ya jawo musu zagi ne ace yayanta bashi da kamun kai. Ko mutum nawa ne suka gani? Mata nawa ya bawa ko suka bashi abinci a baki? Alawar da ya bata ma sai da ta tuna ko sun taba yin haka da wata kafin ita. Wannan yafi tsaya mata a rai taci kuka ta godewa Allah shine fa bacci yayi awon gaba da ita da asuba.
Ghazalatu dama jira take kowa ya fita daga dakin ta zauna kamar tana gyara daurin dankwali. Zahra na fita ta fiddo wayarta taje ta zame hijabin Radhiya da babu dankwali ta kasansa a hankali wani bangare na kan ta ya bayyana tayi saurin daukarta a hoto tana kunshe dariyarta. Awwab zata nunawa kawai don ta rage karfin alakarsu duk ta yadda ya samu.
Awwab da yasan yadda ya rabu da kanwar tasa ya shigo tsakar gidan ya kai sau biyar ko zai ga gilmawarta. Da yaji ance bacci take yi hankalinsa tashi yayi fiye da zatonsa. Ta yaya zai tafi bai sake ganinta ba sai nan da sati biyu. Walwalar fuskarsa gabadaya ta bace yana jin kansa sukuku suka fito. Rakiya harda Malamijo shima yana cigiyar jikarsa mai fitina akace tana bacci.
"Kun taba jikinta kuwa lafiya take babu zazzabi? 'Yar sojan ce zata yi bacci har goma na safe indai ba kwaya ta soma sha ba". Dariya ya basu sosai.
"Mami ko dai bata da lafiyar? Hancinta na gani yayi swelling da saman idonta" inji Zayyana.
Ummi tace "ko ma meye ku bari su tafi a taso ta don yanzu tana zuwa sai ta bata musu lokaci"
Ba dai kukan ta sake yi ba Awwab ya tambayi zuciyarsa. Tamkar kada su tafi haka ya rinka ji. Ghazalatu motarsu ta koma Zahra ta shiga wadda su Mami suka zo don kada a barta ita daya.
Kusan awa daya da tafiyarsu bayan Radhiya ya soma damunta saboda kwanciyar kasa ta bude ido tana mika. Dakin shiru babu kowa ta tashi da sauri babu jakunkunansu sun gyare dakin da katifar. Nauyin bacci gareta shiyasa bata ji motsinsu ba. Gabanta na dukan uku-uku ta garzaya dakin Hajjo wurin Ummi.
"Ummi sun tafi ne?" Tace cikin tashin hankali.
"Ina hankalinki ne, babu sallama babu gaisuwa"
Fita tayi ta dawo cikin sauri ta gyara kuskurenta sannan ta maimaita tambayar da ta riga tasan amsarta tunda bata ga Mami ba kuma babu kayanta.
"Sun tafi kina can kina bacci. Ko baki da lafiya ne?"
Hawaye ne ya taho mata tayi kokarin boyewa "shine basu tashe ni ba?"
"Kiji dadin isarsu da surutu ba. Sun wuce da Karami zai zauna a Kano..."
Alamun kukan Radhiyan taji ta dakata tare da mika hannu inda take jin sautin tun yana tashi a hankali har yayi karfi. Wani irin kunci da bacin rai take ji hade da gagarumar kewar Hamma Awwab. Me yasa bai ce a tasheta ba sunyi sallama. Me yasa daga zuwansa zuciyarta take shiga mabambantan yanayi daga tsananin farinciki sai bacin rai irin na jiya da ta ganshi da mata. Yau kuma don bai damu da ita ba yayi tafiyarsa.
"Ke menene?"
"Ummi ba komai" ta amsa muryarta na sake karyewa. Ta dauki kanta jarumar mace mai dauriya amma lokaci kalilin ta zubar da hawaye fiye da tunaninta. Ita kanta bata san me ya sameta ba sai an mata karin bayani.
Tun Ummin ta na rarrashi har ta koma fada amma taki cewa komai sai kuka. Daga karshe karamar wayar da Mami ta bar mata ta dauko. Ba kudin sayen bane dama ta rasa sai dai karancin wadanda zata kira. Emzee da Radhiya kuwa taki saya musu ne duk da tasan ana yayinta sosai tana jiran su gama sakandire.
"Ungo ki kira Mami da sauran 'yan uwanki ku gaisa kiyi musu sallama kinji 'Yar sojan Daaadaa"