Sashe 52
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashi tayi jin rikon Nenen yayi sauki ta suri hijabinta ta tafi kallon kwal uwar daka a tsakar gidan nasu. Nene ko bi ta kanta bata yi ba sai dogon nazarin da ta samu kanta da yi. Tabbas anyi haka amma tun lokacin bata jin wani yayi tunani a kai ma. Makantar Mairama farat daya tazo duk da an san tana ciwon ido. Bata mantawa ita Mairama ta bawa firinjinta ta sayar wani lokaci suka je asibiti akace babu komai a idon nata. Ko dai da hannun Salame tunda tafi kowa sanin abinda ya taba hadasu da marigayi Zayyan. Saurin kawar da tunanin tayi. Duk bakin halin Salame ace harda makanta kanwarta saboda namiji? Kasa nutsuwa tayi ta nemo yaro cikin yaran gidan ta bashi wayarta ya kira maigidanta. Tayi masa bayanin zarginta ne tace ya kamata a nemo kaikayi koma kan mashekiya.
"Haba Marka ina amfani wata ta warke wata ta makance? Yanzu dai tunda kin fara tunanin haka ki hadani da Mairama ko Radhiya din zan sanar dasu add'o'i da Ayatusshifa a karanta mata ana tofawa a ruwa tasha ta wanke idon. Zamu tsananta addu'a in Allah Ya yarda zamu sami makarin abin indai sihiri ne. Amma kada ki fada mata kada ki tada rigima idan zargi ne kawai. Ki bari mu gwada mu ga ikon Allah"
Godiya tayi masa ta ajiye wayar zuciyarta tana karfafa mata zarginta akan Salame.
***********
Washegari kuwa Nene bata yi kasa a gwiwa ba ta nemi Ayuba. Duk cikin yaran gidan shine ya tashi da ustazanci yana ma koyarwa a Islamiyya. Bayanin mijinta tayi masa shima ya hada da nasa ilimin da kansa ya siyo ruwan roba c'est bon babba yayi mata tofin nan yadda ya kamata. Ranar shi wuni tana sha tana shafe ido. Nene tace mata su gwada ko za'a dace ne ta karba da murnarta.
Bayan kwana biyu Ummi ta fara jin jikinta yana canjawa tafi jindadinsa sosai gashi ruwan tofin saura kadan. Radhiya ta nema saboda ta jiyo muryarta tana cewa Malamijo yau kwadayi take ji yana rantsuwar kada ta bishi gonar da zai tafi a lokacin.
"Kin raina min uba ko" ta tambayeta bayan ta amsa kiran.
Sanye take da riga da skirt na atampa ta gama shirinta da hijab ruwan madara wanda ya dace da kayan iya gwiwa za ta bishi gona tayi barna.
"Ummi balance dayet muke bukata"
"Allah Ya shirya min ke, zo ki dauki kudi ki siyo min ruwa irin wanda Ayuba yayi tofi a ciki. Ki siyo guda uku sai a ajiye"
Murmushi tayi "Ummi kin fara gani ko dan dishi dishi?"
"Ke dai ki sakani a addu'a ido ya bude na ganku ke da kaninki"
"Amin Ummi, wayyo dadi"
"To wuce ki tafi banda yawo" sai ana jaddada mata kamar karamar yarinya.
Tsokanar Ummin tayi tace "Ina zani ko azahar ba'ayi ba inje basu gama abinci ba balle na sa rai da balance dayet din"
Muryar Malamijo ta ji yana magana daga soro ta yi murmushin mugunta. Daga masa hankali zatayi tayi ta binshi yana fada ta dage gonar zata je tunda a kafa yake zuwa. Sai sun isa wurin shagon da zata je sannan zata rabu dashi.
Da dan gudunta ta taho kamshi da idanun da suka kafeta a gaban Malamijo suka kashe bakin da jikin nata baki daya.
Wani murmushi Awwab yayi mata ta mayar masa idanunsu sarke da na juna. Malamijo bai kula ba yana ganinta yace "Allah Ya taimakeni yau ga yayanku na Katsina yace sako ya kawo muku ke da Mairama. Idan kika sake kika biyoni zai koma da kayansa sai in ga karyar cin balanciye din"
Ficewa yayi ya barsu a tsaye. Wani irin kallo yake yi mata taji ta takura.
"Muje wurin Ummi din" tace bayan ta juya masa baya saboda wani nauyinsa da take ji.
"Wait"
A nutse ya tako ya dawo gabanta ya tsaya. Jeans navy blue da layin fari da ya dusashe daga tsakiya ta gaba da shirt mai maballai ruwan toka ya lankwashe dogon hannunta zuwa rabin hannun. Fuskarsa a gyare sai hancinsa ya kara fitowa. Kanta ta sunkuyar ta ma kasa kallonsa.
Da wannan muryar tasa mai kauri da tafiya da hankalinta yace "baki tambayeni me ya dawo dani ba, ko dama kinji a jikinki zan zo?"
"Ba wurin Ummi kazo ba?"
"Basarwar ce?" yayi tambayar yana son sake hada ido da ita.
Hijabinta ta janyo gaban fuskarta zata rufe ya girgiza mata kai.
"Ahhh" yace yana mata alamar ta bude baki.
Kafada ta noke tare da murmushi.
"Please Alheran"
Sake nokewa tayi yace "dadin abin tare muke da My G tana mota"
"Ahhhhhh" tace da sauri har tana bashi dariya domin kuwa ya gama tabbatarwa ba shi kadai bane ya fada wannan kogin da baya fatan fita.
Irin sweet din rannan ce dai wadda ya taho da ita daga Germany ya fito da ita daga bakinsa ya kankance ido yana kallonta "See what you did. Kin cikani da surutu kinsa na kusa shanyewa"
A bakinta ya saka mata kunya tasa ta rufe ido da tafin hannunta.
"Kinsan wani abu" ya bijiro da maganar don kawar da hankalinsa daga kallon bakinta da take shan sweet din dimple dinta da yake matukar burgeshi yana ta sake shigewa ciki.
Kai ta girgiza masa ya dawo gefenta ya tsaya "ta kare miki Alheran auren dreba ya tabbata a gareki"
"Ni dai a'a"
"Are you sure? Ko da dreban mutumin da kike shan sweet din bakinsa ne?"
"Ya Allah" tace yadda yake yi idan yaga abin mamaki tana jin wani irin farinciki mara misaltuwa.
"Na sani ai bazaki so kada ta kare miki ba in dai shine"
Kokarin saita kanta tayi ga murmushinta yaki bacewa "inji wa"
"Ba sai munje nan ba kawai ki amince kamar yadda na amince"
Cike da shagwaba tace "Ni dai wallahi...."
"Me? Ba haka bane?"
"Alawar ce ta kare" tace tare da yi masa gwalo ta soma tafiya da sauri.
"Zaki aureni?"
Ita ce tambayar da taji ya jefa mata a daidai lokacin da kafarta daya ta fita daga soron. Tsayawa tayi a wurin ta kasa gaba ta kasa baya har ya karaso inda take ya rabe ta gefenta ya wuce har cikin tsakar gidan da sallama yana kiran Ummi.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Ummi kamar daga sama ta tsinkayi muryar Awwab. Yadikko ce ta amsa masa suka gaisa ta nuna masa dakin Hajjo.
"Shiga tana ciki"
Radhiya ta hango tsaye ta kasa yanke shawarar komawa taje aiken da akayi mata ko ta bi bayansa.
"Ji min shirme Radhiya kina tsaye ashe kina kallonsa maimakon ki kaishi wurin Mairaman. Dauko filas din wajenta in zuba masa kunun nan da zafinsa"
Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki haka ta shiga dakin. Yana zaune daga gaban Mairama tana tambayarsa mutan gida da hanya.
"Mamaki nayi da naji muryarka fa. Amma dai kowa lafiya ko?"
"Ummi kada ki damu lafiya kalau."
Dagowa yayi yana kallon Radhiya tana neman flask din ruwan zafi. Yana gabanta amma da yake hankalinta yayi nisa bata kula ba. Ummi ce tace "wai har kin dawo ne?"
"Ban je ba, Yadikko ce tace na dauko flas za ta zubawa Hamma kunu"
"Yi maza ki kai mata kije ki siyo min in samu yayi tofin kafin ya fita"
Ita Awwab ya tsare da ido yana tambayar Ummi "aikenta kika yi?"
Bayani Ummin tayi masa yaji dadi yana fatan Allah Yasa a dace. Da ido ya kalli Radhiya yana nuna mata ta zauna ta girgiza kai.
"Bari naje na siyo Ummi ina zuwa"
"Daga zuwanka, barta ba nisa bane da wurin"
Tashi yayi ya sake cewa shi zaije. Ummi tace to ya bari ko ruwa yasha kafin ya fita. So yake kawai ya tashi ya samu kebewa da Radhiya don ba da niyar kwana yazo ba. Gabadaya ya shagala da kallonta. Takwanshe kafafu yayi ya tallabe kansa da hannuwansa da ya dora akan cinyoyinsa ya zuba mata ido. Hanata sakat yayi ta kasa dago kai saboda tsoron idanunsa take yi yadda suke matukar tasiri a kanta.
Wayar Ummi da ta soma ringing ce ta sa ya dena kallon nata na dan lokaci ta tashi da sauri ta fita. Shi ya mikawa Ummin wayar ganin sunan Mami shima ya tashi ya gudu yana dariya bayan ya amsa mata kiran ya saka mata a kunne.
"Dana kika biyo da kiran nan ko? Yanzu ya iso bai yi rabin awa a gidan nan ba"
Sai da Mami tayi dariya tace "nifa ina jin mu saka ranmu a inuwa kawai yaran nan sun gama mana komai sai dai ma su jira mu"
Labarin yadda suka kwashe dashi bayan ya dawo daga sallar asuba tare da Major ta bata suka rinka dariya. Yana shiga gidan yayi sa'a tana falo shine yake fada mata zaije Sumaila. Da ta tambayeshi ko lafiya shine yace wai Alheran bata da waya kuma ya san cewa irin haka ne yake sa 'yan mata su ji babu dadi sa'anninsu suna da abu su basu da shi.
"Akwai waya a hannun Ummin taku ai"
Ita ce amsar da ta bashi.
Sosa keya yayi yace "So nayi na bata a matsayin gift na gama secondary school"
"Ina ta Karami da Ibrahim? Duka tare suka gama"
"Ibrahim yana da waya. Emzee kuma zan saya masa. Tunda ita ce babba shiyasa zan fara bata"
"Ba sai kaje Sumailan ba, nan da 'yan kwanaki zaka gansu sun zo biki"
Fuskarsa tamkar zaiyi kuka yadda ta dage tana neman kure shi. Tsokanarsa ta cigaba da yi daga karshe dai yace mata wai kewar Ummi ke damunsa.
"Kewar Umminka kuwa duk gidan nan banga mai cike maka gurbinta ba. Sai ince a dawo lafiya ko"
Amsar tayi yadda yake so amma kuma ta makale masa a rai. Ko dai Mami ta gane wani abu ne? Kai da wuya shi yasan baya yin yadda kowa zai san yana yiwa Alheran zazzafar soyayyar da take nukurkusar zuciyarsa.
Daya motar ya dauko Mami tana korafin ranar zai takura mata yace tayi hakuri bazai kwana ba. Jinsa kawai tayi sai kace Katsina zuwa Sumailan tafiyar awa daya ce. To gashi dai a gidan Malamijo tare da Alheran Radhiya.
"Haba Marka ina amfani wata ta warke wata ta makance? Yanzu dai tunda kin fara tunanin haka ki hadani da Mairama ko Radhiya din zan sanar dasu add'o'i da Ayatusshifa a karanta mata ana tofawa a ruwa tasha ta wanke idon. Zamu tsananta addu'a in Allah Ya yarda zamu sami makarin abin indai sihiri ne. Amma kada ki fada mata kada ki tada rigima idan zargi ne kawai. Ki bari mu gwada mu ga ikon Allah"
Godiya tayi masa ta ajiye wayar zuciyarta tana karfafa mata zarginta akan Salame.
***********
Washegari kuwa Nene bata yi kasa a gwiwa ba ta nemi Ayuba. Duk cikin yaran gidan shine ya tashi da ustazanci yana ma koyarwa a Islamiyya. Bayanin mijinta tayi masa shima ya hada da nasa ilimin da kansa ya siyo ruwan roba c'est bon babba yayi mata tofin nan yadda ya kamata. Ranar shi wuni tana sha tana shafe ido. Nene tace mata su gwada ko za'a dace ne ta karba da murnarta.
Bayan kwana biyu Ummi ta fara jin jikinta yana canjawa tafi jindadinsa sosai gashi ruwan tofin saura kadan. Radhiya ta nema saboda ta jiyo muryarta tana cewa Malamijo yau kwadayi take ji yana rantsuwar kada ta bishi gonar da zai tafi a lokacin.
"Kin raina min uba ko" ta tambayeta bayan ta amsa kiran.
Sanye take da riga da skirt na atampa ta gama shirinta da hijab ruwan madara wanda ya dace da kayan iya gwiwa za ta bishi gona tayi barna.
"Ummi balance dayet muke bukata"
"Allah Ya shirya min ke, zo ki dauki kudi ki siyo min ruwa irin wanda Ayuba yayi tofi a ciki. Ki siyo guda uku sai a ajiye"
Murmushi tayi "Ummi kin fara gani ko dan dishi dishi?"
"Ke dai ki sakani a addu'a ido ya bude na ganku ke da kaninki"
"Amin Ummi, wayyo dadi"
"To wuce ki tafi banda yawo" sai ana jaddada mata kamar karamar yarinya.
Tsokanar Ummin tayi tace "Ina zani ko azahar ba'ayi ba inje basu gama abinci ba balle na sa rai da balance dayet din"
Muryar Malamijo ta ji yana magana daga soro ta yi murmushin mugunta. Daga masa hankali zatayi tayi ta binshi yana fada ta dage gonar zata je tunda a kafa yake zuwa. Sai sun isa wurin shagon da zata je sannan zata rabu dashi.
Da dan gudunta ta taho kamshi da idanun da suka kafeta a gaban Malamijo suka kashe bakin da jikin nata baki daya.
Wani murmushi Awwab yayi mata ta mayar masa idanunsu sarke da na juna. Malamijo bai kula ba yana ganinta yace "Allah Ya taimakeni yau ga yayanku na Katsina yace sako ya kawo muku ke da Mairama. Idan kika sake kika biyoni zai koma da kayansa sai in ga karyar cin balanciye din"
Ficewa yayi ya barsu a tsaye. Wani irin kallo yake yi mata taji ta takura.
"Muje wurin Ummi din" tace bayan ta juya masa baya saboda wani nauyinsa da take ji.
"Wait"
A nutse ya tako ya dawo gabanta ya tsaya. Jeans navy blue da layin fari da ya dusashe daga tsakiya ta gaba da shirt mai maballai ruwan toka ya lankwashe dogon hannunta zuwa rabin hannun. Fuskarsa a gyare sai hancinsa ya kara fitowa. Kanta ta sunkuyar ta ma kasa kallonsa.
Da wannan muryar tasa mai kauri da tafiya da hankalinta yace "baki tambayeni me ya dawo dani ba, ko dama kinji a jikinki zan zo?"
"Ba wurin Ummi kazo ba?"
"Basarwar ce?" yayi tambayar yana son sake hada ido da ita.
Hijabinta ta janyo gaban fuskarta zata rufe ya girgiza mata kai.
"Ahhh" yace yana mata alamar ta bude baki.
Kafada ta noke tare da murmushi.
"Please Alheran"
Sake nokewa tayi yace "dadin abin tare muke da My G tana mota"
"Ahhhhhh" tace da sauri har tana bashi dariya domin kuwa ya gama tabbatarwa ba shi kadai bane ya fada wannan kogin da baya fatan fita.
Irin sweet din rannan ce dai wadda ya taho da ita daga Germany ya fito da ita daga bakinsa ya kankance ido yana kallonta "See what you did. Kin cikani da surutu kinsa na kusa shanyewa"
A bakinta ya saka mata kunya tasa ta rufe ido da tafin hannunta.
"Kinsan wani abu" ya bijiro da maganar don kawar da hankalinsa daga kallon bakinta da take shan sweet din dimple dinta da yake matukar burgeshi yana ta sake shigewa ciki.
Kai ta girgiza masa ya dawo gefenta ya tsaya "ta kare miki Alheran auren dreba ya tabbata a gareki"
"Ni dai a'a"
"Are you sure? Ko da dreban mutumin da kike shan sweet din bakinsa ne?"
"Ya Allah" tace yadda yake yi idan yaga abin mamaki tana jin wani irin farinciki mara misaltuwa.
"Na sani ai bazaki so kada ta kare miki ba in dai shine"
Kokarin saita kanta tayi ga murmushinta yaki bacewa "inji wa"
"Ba sai munje nan ba kawai ki amince kamar yadda na amince"
Cike da shagwaba tace "Ni dai wallahi...."
"Me? Ba haka bane?"
"Alawar ce ta kare" tace tare da yi masa gwalo ta soma tafiya da sauri.
"Zaki aureni?"
Ita ce tambayar da taji ya jefa mata a daidai lokacin da kafarta daya ta fita daga soron. Tsayawa tayi a wurin ta kasa gaba ta kasa baya har ya karaso inda take ya rabe ta gefenta ya wuce har cikin tsakar gidan da sallama yana kiran Ummi.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Ummi kamar daga sama ta tsinkayi muryar Awwab. Yadikko ce ta amsa masa suka gaisa ta nuna masa dakin Hajjo.
"Shiga tana ciki"
Radhiya ta hango tsaye ta kasa yanke shawarar komawa taje aiken da akayi mata ko ta bi bayansa.
"Ji min shirme Radhiya kina tsaye ashe kina kallonsa maimakon ki kaishi wurin Mairaman. Dauko filas din wajenta in zuba masa kunun nan da zafinsa"
Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki haka ta shiga dakin. Yana zaune daga gaban Mairama tana tambayarsa mutan gida da hanya.
"Mamaki nayi da naji muryarka fa. Amma dai kowa lafiya ko?"
"Ummi kada ki damu lafiya kalau."
Dagowa yayi yana kallon Radhiya tana neman flask din ruwan zafi. Yana gabanta amma da yake hankalinta yayi nisa bata kula ba. Ummi ce tace "wai har kin dawo ne?"
"Ban je ba, Yadikko ce tace na dauko flas za ta zubawa Hamma kunu"
"Yi maza ki kai mata kije ki siyo min in samu yayi tofin kafin ya fita"
Ita Awwab ya tsare da ido yana tambayar Ummi "aikenta kika yi?"
Bayani Ummin tayi masa yaji dadi yana fatan Allah Yasa a dace. Da ido ya kalli Radhiya yana nuna mata ta zauna ta girgiza kai.
"Bari naje na siyo Ummi ina zuwa"
"Daga zuwanka, barta ba nisa bane da wurin"
Tashi yayi ya sake cewa shi zaije. Ummi tace to ya bari ko ruwa yasha kafin ya fita. So yake kawai ya tashi ya samu kebewa da Radhiya don ba da niyar kwana yazo ba. Gabadaya ya shagala da kallonta. Takwanshe kafafu yayi ya tallabe kansa da hannuwansa da ya dora akan cinyoyinsa ya zuba mata ido. Hanata sakat yayi ta kasa dago kai saboda tsoron idanunsa take yi yadda suke matukar tasiri a kanta.
Wayar Ummi da ta soma ringing ce ta sa ya dena kallon nata na dan lokaci ta tashi da sauri ta fita. Shi ya mikawa Ummin wayar ganin sunan Mami shima ya tashi ya gudu yana dariya bayan ya amsa mata kiran ya saka mata a kunne.
"Dana kika biyo da kiran nan ko? Yanzu ya iso bai yi rabin awa a gidan nan ba"
Sai da Mami tayi dariya tace "nifa ina jin mu saka ranmu a inuwa kawai yaran nan sun gama mana komai sai dai ma su jira mu"
Labarin yadda suka kwashe dashi bayan ya dawo daga sallar asuba tare da Major ta bata suka rinka dariya. Yana shiga gidan yayi sa'a tana falo shine yake fada mata zaije Sumaila. Da ta tambayeshi ko lafiya shine yace wai Alheran bata da waya kuma ya san cewa irin haka ne yake sa 'yan mata su ji babu dadi sa'anninsu suna da abu su basu da shi.
"Akwai waya a hannun Ummin taku ai"
Ita ce amsar da ta bashi.
Sosa keya yayi yace "So nayi na bata a matsayin gift na gama secondary school"
"Ina ta Karami da Ibrahim? Duka tare suka gama"
"Ibrahim yana da waya. Emzee kuma zan saya masa. Tunda ita ce babba shiyasa zan fara bata"
"Ba sai kaje Sumailan ba, nan da 'yan kwanaki zaka gansu sun zo biki"
Fuskarsa tamkar zaiyi kuka yadda ta dage tana neman kure shi. Tsokanarsa ta cigaba da yi daga karshe dai yace mata wai kewar Ummi ke damunsa.
"Kewar Umminka kuwa duk gidan nan banga mai cike maka gurbinta ba. Sai ince a dawo lafiya ko"
Amsar tayi yadda yake so amma kuma ta makale masa a rai. Ko dai Mami ta gane wani abu ne? Kai da wuya shi yasan baya yin yadda kowa zai san yana yiwa Alheran zazzafar soyayyar da take nukurkusar zuciyarsa.
Daya motar ya dauko Mami tana korafin ranar zai takura mata yace tayi hakuri bazai kwana ba. Jinsa kawai tayi sai kace Katsina zuwa Sumailan tafiyar awa daya ce. To gashi dai a gidan Malamijo tare da Alheran Radhiya.