← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 157

Sashe 20

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta kwashe kusan awa shida tana fama banda wanda tayi a cikin gidanta kafin Allah Yasa ta sauka lafiya ta haifi danta tamkar Zayyan yayi khaki don yafi Radhiya kama dashi sosai.

Likitocin sun bata kulawa yadda ya dace sannan aka kaita dakin da zata huta saboda wahalar da tasha. Christie tace mata zata je gida tayi girki ta kawo mata don taji kwari. Matar akwai kirki sosai ita ma. Radhiya ta sake dauka dama da tana ciki wurin haihuwa ta siyo mata fanke a 'yar kasuwar gefen asibitin taci ta koshi ta debo ruwa a famfon waje ta bata. 

Suna fita ta sake daukan jaririn sai kawai tasa kuka. Yaron da tayi fatan zuwansa duniya mahaifinsa ya karbeshi yayi masa addu'a. Sai gashi ta haihu din a lokacin da bata da masaniyar halin da yake ciki. Karin kukanta yau ta haihu babu kowa nata sai Christie da ta tsaya mata tamkar 'yar uwa. Mami da Zainab suna can lalurar mazajensu ta saka su a gaba. Yanzu ita wa take dashi da zata tura a sanar da gidansu da gidan iyayen Zayyan. Tun tafiyarsa babu wanda ya tako ganinta cikin 'yan uwansa ko da wasa. Me ya ja mata nesanta da 'yan uwanta da na mijinta da rashin zama cikin mutanen da tasan sunyi tarayya a yare, addini da al'ada? Auren Soja ta bawa kanta amsa. Sojan ma Zayyan wanda idan za'a sake bata zabi tayi rantsuwa har ranta shi din a sojansa zata sake aure. Tana sonsa kuma tana alfahari da aikinsa kamar yadda yake yi shima.

Tunani ta zurfafa tana yi akan rashin sanin yaya zata yi labarin haihuwarta ya iske danginsu. Lokacin Radhiya shi yayi komai abinsa. Yanzu kuwa komai ya dawo gareta.

Kan jaririn ta shafa tana hawaye "Daadaa yaci burin ganin zuwanka duniya ko suna bai yarda mun zaba ba saboda yace yana son yayi yiwa jaririnsa huduba da kansa"

Yaro yana baccinsa cikin kwanciyar hankali ta kwantar dashi a gefenta daga jikin bango tana shafa shi a hankali.

"Sojana ka bar min amana mai nauyi. Baka fada min yaya zanyi ba idan baka dawo da wuri ba"

Kuka ta shiga rerawa a hankali tana jin wani matsanancin ciwon kai. Kwanciya ta gyara a gefen dan ta lumshe idanunta ta baiwa kofa baya.

Tana ji likitoci biyu suka shigo dukkansu sojoji da nos guda daya. Wanda ya karbi haihuwarta ya yiwa dayan bayanin cewa ta zubar da jini kuma jininta ya hau kada a sallameta sai gobe.

"Na fahimta Dr. Ina file din nata?" Ya tambayi Nos ta mika masa.

Zaro idanu yayi ya dago yana kallon wancan likitan.

"Matar Lt. Zayyan Tureta ce? Sune last week akace gabadaya unit dinsu...."

Wanda ya karbi haihuwar yayi saurin sa hannu akan lebensa yana magana a hankali harda juya harshe zuwa turanci a zatonsu bacci take, kuma kana yi mata kallo daya ka ga bafillatana wadda ake musu kallon basu da wani ilimin boko sai kiwon shanu.

"Shhh I don't think they know what has happened"

Mairama taji gabanta ya fadi wani abu yana mata yawo a jiki tun daga kai har tafin kafa, sai ta daure ko motsi bata yi ba. Nos din ta kalli bayanta da tausayawa a hankali tace.

"I pity their wives"

Basu san daga ina ba sai ganin Mairama suka yi rike da kafadun Nos din idanunta a rufe cikin karaji take tambayarta "what happened to my husband?"

Kallon kallo suke yi  sai taji gabadaya duniyar tana son kife mata. Durkushewa tayi gwiwoyi a kasa tana kallonsu tamkar wadda ta sami tabin kwakwalwa.

"Don Allah don Annabi ku fada min gaskiya"

Tashinta yazo musu a bazata haka fahimtar turancinta shiyasa suka kasa bata amsa kai tsaye. Shirunsu kadai ya isheta amsar da take nema da yanayin da taga sun shiga na tausayinta da tsoron fada mata gaskiya.

"Kinga ki kwantar da hankalinki idan kinji sauki za'a fada miki komai"

Murmushi tayi mai sauti tana ja da baya da baya har ta kai jikin bango ga hawaye tana zubarwa kamar ruwan famfo "da hankalina fa, nasan abinda nake tunani hakane. Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Ya Allah....ahhhh. ....kirjina..wayyo Allah.. Ka jikanka Sojana"

Likitan da yazo zai canji wancan aiki ya dan matso kadan "kizo ki zauna...uhmm"

Nos tace "Mairama"

"Ok Mairama ki zauna muyi magana kinji"

Jaririnta kawai ta dauka ta saka shi a kafada tana cigaba da kukanta tana cewa "tun yaushe ya rasu?"

Basu iya cewa komai ba tayi hanyar kofa suna kiranta taki tsayawa. Sai dai kafin ta fita jikinta ya soma rawa likitan da yafi kusa da ita yayi saurin karbe jaririn ta fara neman faduwa tana wata irin jijjiga ga jini ya balle mata. 

Nos da daya likitan ne suka kamata aka dora akan gado suna neman ceto rayuwarta.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Kwana biyu da rabin wuni Mairama tayi kafin ta gane inda take da babbar jarabawar da ta tunkaro rayuwarta. Ta farfado da misalin uku na rana washegarin ranar da ta haihu. Idanunta a rufe suke amma tana iya jiyo maganganu kamar ana fada. A hankali ta fara fuskantar me ake cewa wanda yayi sanadin fitowar hawaye daga idanunta, kuma har lokacin a rufe suke.

"Ni dai na fada miki gobe zan tura Rayyanu yaje garinsu ya sanar da iyayenta su zo su dauketa don bazan iya jigila ba."

"Haba Maikudi kai kuwa baka ganin ga danyen jego ga rashin lafiya. A barta ta huta mana"

Gwaggo Ladi da tayi maganar ya kalla darajar mijinta Mal Aminu ya kasa bata amsar da yayi niyya. Wani dan tunani yayi ya kara tabbatarwa gara yabi komai a hankali don samun biyan bukata.

"To naji sai ta zauna har sai ta gama takaba an raba gado. Ince ko hakan yayi" ya mayar da kallonsa ga Mal.Aminu da ya dauke kansa saboda takaicin halin Maikudi. Yaron ya fita zakka tamkar ba jinin Mal Muhammadu ba.

Mal Aminu da ya gama tofe jariri da addu'a ya dago kansa "bana son hauka Maikudi. Takaba dai tana haihuwa ta fita. Sannan tun muna shaida juna kada inji kada in gani, kaf abinda Zayyanu ya bari na matarsa ne da 'ya'yansa tunda yana da da namiji."

A fusace ya juyo "inji uban wa?"

"Inji ubanka"

Mamaki kamar ya kashe shi saboda Jume ce ta bashi wannan amsar. Akan tabarma take tana bawa Radhiya abinci. Daga jiya zuwa yau tayi wuri-wuri da ita. Rasuwar Zayyan ta tabata fiye da zato da tsammaninta. Duk wata mugunta da ta taba yiwa mahaifiyarsa dashi kansa sune suka yi mata dabaibayi. Cikinsu babu wanda ya taba nufinta da sharri gashi sun bar mata duniyar tayi yadda take so. Nadama ce ta gaske take nukurkusar zuciyarta. Ga Maikudu don abin kunya daga jiya zuwa yau banda rashin mutumci babu abinda yake zubawa a dakin. Daure fuska ta sake yi

"Saboda baka san me kake yi ba ace kaninka ya rasu amma ko a jikinka?"

"Kina ji fa aka ce yayi wata guda harda dorin kwanaki, duk dacin mutuwa ai yaci ace tayi sauki an fara fuskantar gaba"

Mairamu ta kasa boye kukan zucin ta koma yi a fili. Ashe har yafi wata da rasuwa bata da masaniya. Shine take ci tasha har tayi wasa da dariya? Ashe Sojanta ya koma ga Allah take ta tunanin dawowarsa. Yanzu shikenan nata mijin saboda soja ne ko kabarinsa babu wani danginsa da zai sani? Anyi masa wankan gawa? An sallace shi? Wace irin mutuwa yayi duk basu sani ba.

Kukanta ya tsananta Gwaggo Ladi ta tashi ta matsa kusa da ita ta tsaya a gefen gadon.

"Mairama hakuri zakiyi da yawaita yi masa addu'a"

Rarrashinta suke ta yi ita da Jume sannan Mal Aminu ya fita saboda ance ta shayar da jaririn.

Maikudi yayi qiqam kamar sanda sai da Jume tace ya fita, yayi waje yana surutai.

Yaron ta karba wanda rabonta dashi tun jiya. Yaji yunwa kuwa sai ruwa aka rinka bashi da tana kwance. 

Gwaggo Ladi tace Malam yayi masa huduba da Muhammad Zayyan. Ina fata hakan yayi miki" 

Hawayen Mairama har fuskar jaririn tayi murmushi "Sojana Allah Ya raya min kai."

**********

"Wai Zayyanu dai Zayyanu soja mijin 'yata Mairama kake nufi?" Malamijo yayi maganar kamar zaiyi kuka.

"Shi nake nufi. Allah Yayi masa rasuwa a kasar da suka je" Rayyanu ya bashi amsa. Shi da Badaru da 'yan uwansu mata kaf mutuwar Zayyan ta shigesu sosai. Mutum mai barkwanci da saurin manta bacin rai. Duk yadda su ke bata masa bai hana shi kyakyawan zumunci dasu ba ko da su bazasu yi masa kallon arziki ba.

Malamijo ya daga hannu ya dora a ka "Laaaaahhhh ha'ila ha ilallahu, kaico Mairama, 'yar marainiyata ta rasa miji kuma"

Lokaci kankani a tsakani zance ya bazu ko ina mijin Mairama ya rasu a filin daga. Mutane suka fara zuwa yiwa Malamiji ta'aziyya yana cewa nan da kwana biyu zai wuce Sakkwato. 

A cikin gidan ma jikinsu duk yayi sanyi. Ba wani haduwa suke yi sosai ba saboda nisan garuruwansu amma duk da haka a iya lokutan da su ka ganshi anyi masa shaidar arziki. Malamijo yasa a dafa abincin sadaka ya saki bakin aljihu abinda basu saba gani ba. Cikin yaransa maza ya tura babban mai bin Mairama a shekaru yaje Balan ya sanar da Nene Marka. Idan zata bisu ta'aziyya ta taho washegari su wuce jibi. Sannan ya tura mai bi masa Kano gidan Salame.

Suna zaune shi da 'yan gaisuwa wani yake tambayar yaya Zayyan din ya rasu don shi ma akwai dan uwansa soja a kudu, yana tsoron a tura shi yaki. Malamijo bai tashi bada amsa ba sai da yaga Rayyanu ya tashi zai zaga ya soma jawabi.
Chapter 20 · 0% Book details