Sashe 3
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata asabar ta tashi da nakuda gashi Mal Muhammadu yayi sammakon fita ranar yaran duka su ma basa nan. Tana cikin wannan yanayi ta rinka kiran Jume tana jinta tayi biris abinta. Cikin tsananin azaba Alheran ta soma yunkurin haihuwa abinda ke cikinta kansa ne kawai ya leko Allah Ya karbi ranta. Shima kuma wahala bata barshi ba bai jima ba ya koma. Jume ta ma manta da cewa ta ji Alheran tana kiranta wanda tasan haihuwa ce tayi kwanciyarta tana bacci. A yashe a kasa Mal Muhammadu ya dawo ya riski Alheran rai yayi halinsa. Yayi kukan rashinta ba kadan ba. Jume tayi rantsuwa kwando kwando kan cewa bata ji ko da tari daga dakin Alheran ba. To dayake abin da tayi ya dameta a rai shine ta dauki Zayyan ta rike. Riko ne dai irin na matar uba da bata son dan kishiya amma dai duk tsiya tana kulawa dashi. A haka ya taso gatansa daya mahaifinsa. Maikudi shine babban da namiji a gidan wanda ya kasance na uku a wurin Jume kuma tashin hankalin gidan gabadaya.
Shekara biyu kenan da rasuwar Mal Muhammadu, Jume da iyalinta suka tattare duk wani abin arziki suka boye. Dan wanda aka fitar shine aka raba musu tare harda Zayyan. Sauran Maikudi yaki fito dasu tun ‘yan uwansa suna magana har sun ja bakinsu sun rufe.
Bashi da kirki ko kadan Jumen ma tsoronsa take ji.
Dakin Jume ya fara shiga daga dawowarsa ya gaisheta. Kamar kullum amsar dai babu yabo babu fallasa. Haka ya tashi a sabule yana fatan kada ya gamu da Maikudi. Yayi babbar sa’a kuwa don kwanansa biyu basu hadu ba. A kwana na uku ne Kawunsa Ghoumar kanin Alheran yazo daga Nijar.
Kafin ya iso gidan ya aika aka kirawo masa Zayyan suka hadu a gidan wani abokin Mal Muhammadu wanda tare suka sansu a lokacin da suke zuwa fatauci Nijar din. Zayyan yayi murnar ganinsa sosai saboda ba kasafai yake samun ganin dangin mahaifiyar tasa ba. A gaban abokin Malam din Ghoumar ya dauko damin kudi ya mikawa Zayyan.
“Wannan shine kasonka na gadon Alheran. Sai da cutar ajali ta kama Baffanmu ya tuba ya dawo mana da dukiyar mahaifinmu. A ciki an fitar da kason Alheran shine aka raba muku kai da Mal Muhammadu bisa doron shari’a”
Kudin Zayyan ya shiga juyawa duk da bai kirga ba ya tabbatar suna da yawa. Ghoumar yayi murmushi “kasan mahaifinmu yana da rakuma da dabbobi sosai. Sune aka sayar aka raba naku saboda na sani babu abinda soja zaiyi da rakumi”
Dariya suka yi ya cigaba da yi musu bayanin cewa kason Mal Muhammadu da yake hannunsa kuma zai kai gidan a lokacin za’a raba shi ne tsakanin Jume da su yaransa dukkansu. Abokin Mal Muhammadu yace sun zabi bashi nasa a kebence ne saboda sanin halin Jume da Maikudi. Shawara suka bashi ya tabbatar ya boye domin sun sani wannan kudi ba karamin gata zai masa ba. A nan hannun aminin mahaifin nasa Mal Aminu ya bar kudin kafin yayi shawarar me zaiyi dasu. Daga nan suka wuce gidansu tare.
Kamar yadda ya sanar da Zayyan haka Ghoumar ya sake yi musu bayani. Liman aka kira da wasu malamai biyu suka kasafta kudin tsakanin Jume, ‘ya’yanta shida da Zayyan. Ana mikawa kowa nasa Maikudi ya tashi yana kumfar baka.
“Yanzu kuke cewa Zayyanu akwai nasa kason a matsayinsa na danta. To kuma banda tsantsar mugunta me zai sa rabon mahaifinmu a sake kasaftawa dashi?”
Ghoumar ya harare shi “rabon gado ba da ka ake yinsa ba malam. Abu ne da Allah Ya tsara da kanShi. Zayyan yaci rabon kasancewarsa danta sannan yana da rabo a kason mahaifinsa”
Rigima ce ta kaure inda Jume da yaranta musamman Maikudi suka dage akan baza’a raba da Zayyan ba. Da ya ga abin yaci tura yace ya yafe amma Ghoumar da Mal Aminu suka ce sam sai ya karba.
Tsiya tsiya aka rabu babu dadi. Ghoumar rai a bace yace idan ya kuskura ya basu wani abu a wancan kudin nasa na shi kadai bai yafe masa ba. Dariya ya bawa Zayyan ya dai yi masa nasiha da kuma horonsa da rikon zumunci duk da yasan yanayin aikinsa abin zaiyi wuya.
Suna tafiya kuwa Jume ta kira shi dakinta suna zaune ita da Maikudi sai kumburi yake shi kadai.
“Zayyanu munyi magana da yayanka tunda kai a bariki kake rayuwa ka bashi kasonka ya cigaba da juya maka”
Magana ce ta rainin hankali ya gode Allah da wayonsa sarai amma sai ya biye mata “to Jume amma da na riga na barwa Kawun ne ya yi min kiwon a can Nijar”
Tsuke fuska tayi “kana nufin kai ba kudi aka baka ba?”
“Rakuma ne da dabbobi”
Maikudi ya tashi kamar zai buge shi don zuciyarsa na fada masa karya Zayyan din yake. Wani kallo mai firgitarwa Zayyan ya watsa masa allurer soja ta motsa. Da kansa yayi lakwas ya koma ya zauna yana kallon Jume.
“Kina kallo a gabanki yaron nan yake min kallon banza ko Jume?”
Bata kula shi ba ta sake kallon Zayyan fuska babu walwala “abinda za’ayi sai ka kawo wanda aka baka a gabanmu ya hada ya juya muku din”
A ladabce yace “Gobe da safe in Allah Ya yarda zan je wurin Mal Aminu na karbosu.”
“Shi ka barwa don kana bakinciki da karuwata?” Maikudi yace yana kallonsa shekeke.
Bai tanka shi ba yana sauraron Jume tana fada masa gobe da sassafe yaje ya karbo kudin ya kawo mata. Daren ranar har bacci ya kwashe shi yana mamakin wannan karfin hali da iko da aka ki dena nuna masa duk da ya mallaki hankalinsa.
Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir.
[7/4, 7:38 PM] +234 806 334 4334: C
Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir.
***********
“Ka koma ka fadawa wadda ta aiko ka na fada na kara ‘yata bazata tafi kwadayi gidan kowa ba.” Cewar Malamijo yana karkada dan jikinsa duk don ya nuna da gaske fa yake.
Yaron wanda ya kasance kanin Salame da suka hada uwa ya tashi ya bar wurin Salame na zubar hawaye. Wata tsawa Malamijo ya daka mata ta shi babu shiri jiki na bari.
“Kwalamammiya tashi ki bani wuri. Ku babu mijin babu wata sana’ar kawo dari da kwabo sai dai aci a cika min shadda da bayan gari. Mtww Kallamu kwoi mugu, ya rinka rudata sai da na kaiku bokon banza bokon hofi gashi ban ga komai a kasa ba”
Mairama da ke wanki a tsakar gidan ya nuna da bakinsa da yake turawa saitinta “ke kuma sai bakin hali ba uhm ba uhmm uhmm kinbi kin tsaneni ina mahaifinki. Ko rokona abu ba kya yi. To duk jarabar mutum dai ba’a sake uba. Nine nan dai uban naki don ko makaho ya shafaki ya shafani yasan akwai jini. Da namiji kika fito ma sunana zan maida miki Yasin”
Wankinta ta cigaba tana yi hawaye na diga a cikin bokitin ta jiyo muryar Yadikko daga dakin girki.
“Ka dai ji kunya Malamijo, kana abu yana damunka shine ka rasa da wadda zaka rinka wannan magana kamar wata sa’arka sai ‘yar cikinka. Rashin roko tayi min daidai. Masu yi din banda bakar magana me kake tsinana musu bayan sun gama keta billensu”
Hularsa ya turo gaban goshi a karkace “mutum dai ya shiga taitayinsa dani don ni dadewa bazata sa na kasa sallamar ‘yan hamayya ba”
Daidai nan Nene kanwarsa da ta kawo musu ziyara daga wani kauyen Gaya inda take aure ta idar da sallah. Magana take da niyyar yi masa akan yadda yake yi da gidansa duk da dai ba yau farau ba suka ji an banko kofar gidan.
Ta Madina ce babar Salame ta shigo ko sallama babu “gani nazo da kaina a bani ‘yata Malamijo ko in nuna maka ba kai kadai aka haifa a watan tijara ba”
Tuni tsakar gidan ta kaure da ‘ya’ya da matansa an fito kallo. Salame jikinta har bari yake tana kuka.
“Yanzu ke baki ji kunyar shigo min gida ba? Koda shike naji labarin yanzu ma zawarci kike kina neman mafaka”
Daga murya tayi cikin fada ta nuna shi da yatsa “Ali ba tsoronka nake ji ba. A bani ‘yata biki zamu na ‘ya’yan ‘yar uwata a Kano”
“Bazata ba” yace a takaice.
Fada Innar Salame ta soma yi Nene ta sa baki “Ke Salame wuce ki hado kaya kizo ki bi mahaifiyarki. Malamijo idan baka bari yaran nan suna rabar dangin iyayensu mata za’a sami matsala nan gaba”
Wani karkataccen kallo ya bita da shi kafin ya kada baki yace “ke da kika lallabo cin arziki ina ruwanki da iyalina bayan baki san zafin haihuwar ba?”
Jikinta ne yayi sanyi ta dukar da kai “Malamijo ni???”
Shima sai yaji nasa jikin ya saki don kuwa yana ji da Iyalle ko a cikin dangi “ba haka nake nufi ba. Ke Salame zo ki bi uwarki kuma sati guda na bada aka dara ban yafe ba”
Innar Salame tana tsaye tana karkada kafa daya tana jiranta ta fito. Mairama tana rakube a jikin bango wurin da suke shanya tana jin inama ita ce zata je wurin dangin tata mahaifiyar. Sai dai ina zata sami wannan damar. Mutanen da suke fulanin tashi basu nan basu can. Auren ma da Innarta anyi ne kawai saboda sauke bashin da Malamijo yake bin babanta a lokacin. Hangota Innar Salame tayi sai taji yarinyar ta bata tausayi.
“Mairama kema ko zaki bimu ne?”
Malamijo yayi wani tsalle sai gashi a gaban Mairama “wannan kuma kinyi tsararo Ta Madina, babu inda zata je”
Iyalle da kanta tazo taja hannunta ta kaita dakinsu “hada kayanki ki bisu zanyi maganin abin”
Shekara biyu kenan da rasuwar Mal Muhammadu, Jume da iyalinta suka tattare duk wani abin arziki suka boye. Dan wanda aka fitar shine aka raba musu tare harda Zayyan. Sauran Maikudi yaki fito dasu tun ‘yan uwansa suna magana har sun ja bakinsu sun rufe.
Bashi da kirki ko kadan Jumen ma tsoronsa take ji.
Dakin Jume ya fara shiga daga dawowarsa ya gaisheta. Kamar kullum amsar dai babu yabo babu fallasa. Haka ya tashi a sabule yana fatan kada ya gamu da Maikudi. Yayi babbar sa’a kuwa don kwanansa biyu basu hadu ba. A kwana na uku ne Kawunsa Ghoumar kanin Alheran yazo daga Nijar.
Kafin ya iso gidan ya aika aka kirawo masa Zayyan suka hadu a gidan wani abokin Mal Muhammadu wanda tare suka sansu a lokacin da suke zuwa fatauci Nijar din. Zayyan yayi murnar ganinsa sosai saboda ba kasafai yake samun ganin dangin mahaifiyar tasa ba. A gaban abokin Malam din Ghoumar ya dauko damin kudi ya mikawa Zayyan.
“Wannan shine kasonka na gadon Alheran. Sai da cutar ajali ta kama Baffanmu ya tuba ya dawo mana da dukiyar mahaifinmu. A ciki an fitar da kason Alheran shine aka raba muku kai da Mal Muhammadu bisa doron shari’a”
Kudin Zayyan ya shiga juyawa duk da bai kirga ba ya tabbatar suna da yawa. Ghoumar yayi murmushi “kasan mahaifinmu yana da rakuma da dabbobi sosai. Sune aka sayar aka raba naku saboda na sani babu abinda soja zaiyi da rakumi”
Dariya suka yi ya cigaba da yi musu bayanin cewa kason Mal Muhammadu da yake hannunsa kuma zai kai gidan a lokacin za’a raba shi ne tsakanin Jume da su yaransa dukkansu. Abokin Mal Muhammadu yace sun zabi bashi nasa a kebence ne saboda sanin halin Jume da Maikudi. Shawara suka bashi ya tabbatar ya boye domin sun sani wannan kudi ba karamin gata zai masa ba. A nan hannun aminin mahaifin nasa Mal Aminu ya bar kudin kafin yayi shawarar me zaiyi dasu. Daga nan suka wuce gidansu tare.
Kamar yadda ya sanar da Zayyan haka Ghoumar ya sake yi musu bayani. Liman aka kira da wasu malamai biyu suka kasafta kudin tsakanin Jume, ‘ya’yanta shida da Zayyan. Ana mikawa kowa nasa Maikudi ya tashi yana kumfar baka.
“Yanzu kuke cewa Zayyanu akwai nasa kason a matsayinsa na danta. To kuma banda tsantsar mugunta me zai sa rabon mahaifinmu a sake kasaftawa dashi?”
Ghoumar ya harare shi “rabon gado ba da ka ake yinsa ba malam. Abu ne da Allah Ya tsara da kanShi. Zayyan yaci rabon kasancewarsa danta sannan yana da rabo a kason mahaifinsa”
Rigima ce ta kaure inda Jume da yaranta musamman Maikudi suka dage akan baza’a raba da Zayyan ba. Da ya ga abin yaci tura yace ya yafe amma Ghoumar da Mal Aminu suka ce sam sai ya karba.
Tsiya tsiya aka rabu babu dadi. Ghoumar rai a bace yace idan ya kuskura ya basu wani abu a wancan kudin nasa na shi kadai bai yafe masa ba. Dariya ya bawa Zayyan ya dai yi masa nasiha da kuma horonsa da rikon zumunci duk da yasan yanayin aikinsa abin zaiyi wuya.
Suna tafiya kuwa Jume ta kira shi dakinta suna zaune ita da Maikudi sai kumburi yake shi kadai.
“Zayyanu munyi magana da yayanka tunda kai a bariki kake rayuwa ka bashi kasonka ya cigaba da juya maka”
Magana ce ta rainin hankali ya gode Allah da wayonsa sarai amma sai ya biye mata “to Jume amma da na riga na barwa Kawun ne ya yi min kiwon a can Nijar”
Tsuke fuska tayi “kana nufin kai ba kudi aka baka ba?”
“Rakuma ne da dabbobi”
Maikudi ya tashi kamar zai buge shi don zuciyarsa na fada masa karya Zayyan din yake. Wani kallo mai firgitarwa Zayyan ya watsa masa allurer soja ta motsa. Da kansa yayi lakwas ya koma ya zauna yana kallon Jume.
“Kina kallo a gabanki yaron nan yake min kallon banza ko Jume?”
Bata kula shi ba ta sake kallon Zayyan fuska babu walwala “abinda za’ayi sai ka kawo wanda aka baka a gabanmu ya hada ya juya muku din”
A ladabce yace “Gobe da safe in Allah Ya yarda zan je wurin Mal Aminu na karbosu.”
“Shi ka barwa don kana bakinciki da karuwata?” Maikudi yace yana kallonsa shekeke.
Bai tanka shi ba yana sauraron Jume tana fada masa gobe da sassafe yaje ya karbo kudin ya kawo mata. Daren ranar har bacci ya kwashe shi yana mamakin wannan karfin hali da iko da aka ki dena nuna masa duk da ya mallaki hankalinsa.
Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir.
[7/4, 7:38 PM] +234 806 334 4334: C
Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir.
***********
“Ka koma ka fadawa wadda ta aiko ka na fada na kara ‘yata bazata tafi kwadayi gidan kowa ba.” Cewar Malamijo yana karkada dan jikinsa duk don ya nuna da gaske fa yake.
Yaron wanda ya kasance kanin Salame da suka hada uwa ya tashi ya bar wurin Salame na zubar hawaye. Wata tsawa Malamijo ya daka mata ta shi babu shiri jiki na bari.
“Kwalamammiya tashi ki bani wuri. Ku babu mijin babu wata sana’ar kawo dari da kwabo sai dai aci a cika min shadda da bayan gari. Mtww Kallamu kwoi mugu, ya rinka rudata sai da na kaiku bokon banza bokon hofi gashi ban ga komai a kasa ba”
Mairama da ke wanki a tsakar gidan ya nuna da bakinsa da yake turawa saitinta “ke kuma sai bakin hali ba uhm ba uhmm uhmm kinbi kin tsaneni ina mahaifinki. Ko rokona abu ba kya yi. To duk jarabar mutum dai ba’a sake uba. Nine nan dai uban naki don ko makaho ya shafaki ya shafani yasan akwai jini. Da namiji kika fito ma sunana zan maida miki Yasin”
Wankinta ta cigaba tana yi hawaye na diga a cikin bokitin ta jiyo muryar Yadikko daga dakin girki.
“Ka dai ji kunya Malamijo, kana abu yana damunka shine ka rasa da wadda zaka rinka wannan magana kamar wata sa’arka sai ‘yar cikinka. Rashin roko tayi min daidai. Masu yi din banda bakar magana me kake tsinana musu bayan sun gama keta billensu”
Hularsa ya turo gaban goshi a karkace “mutum dai ya shiga taitayinsa dani don ni dadewa bazata sa na kasa sallamar ‘yan hamayya ba”
Daidai nan Nene kanwarsa da ta kawo musu ziyara daga wani kauyen Gaya inda take aure ta idar da sallah. Magana take da niyyar yi masa akan yadda yake yi da gidansa duk da dai ba yau farau ba suka ji an banko kofar gidan.
Ta Madina ce babar Salame ta shigo ko sallama babu “gani nazo da kaina a bani ‘yata Malamijo ko in nuna maka ba kai kadai aka haifa a watan tijara ba”
Tuni tsakar gidan ta kaure da ‘ya’ya da matansa an fito kallo. Salame jikinta har bari yake tana kuka.
“Yanzu ke baki ji kunyar shigo min gida ba? Koda shike naji labarin yanzu ma zawarci kike kina neman mafaka”
Daga murya tayi cikin fada ta nuna shi da yatsa “Ali ba tsoronka nake ji ba. A bani ‘yata biki zamu na ‘ya’yan ‘yar uwata a Kano”
“Bazata ba” yace a takaice.
Fada Innar Salame ta soma yi Nene ta sa baki “Ke Salame wuce ki hado kaya kizo ki bi mahaifiyarki. Malamijo idan baka bari yaran nan suna rabar dangin iyayensu mata za’a sami matsala nan gaba”
Wani karkataccen kallo ya bita da shi kafin ya kada baki yace “ke da kika lallabo cin arziki ina ruwanki da iyalina bayan baki san zafin haihuwar ba?”
Jikinta ne yayi sanyi ta dukar da kai “Malamijo ni???”
Shima sai yaji nasa jikin ya saki don kuwa yana ji da Iyalle ko a cikin dangi “ba haka nake nufi ba. Ke Salame zo ki bi uwarki kuma sati guda na bada aka dara ban yafe ba”
Innar Salame tana tsaye tana karkada kafa daya tana jiranta ta fito. Mairama tana rakube a jikin bango wurin da suke shanya tana jin inama ita ce zata je wurin dangin tata mahaifiyar. Sai dai ina zata sami wannan damar. Mutanen da suke fulanin tashi basu nan basu can. Auren ma da Innarta anyi ne kawai saboda sauke bashin da Malamijo yake bin babanta a lokacin. Hangota Innar Salame tayi sai taji yarinyar ta bata tausayi.
“Mairama kema ko zaki bimu ne?”
Malamijo yayi wani tsalle sai gashi a gaban Mairama “wannan kuma kinyi tsararo Ta Madina, babu inda zata je”
Iyalle da kanta tazo taja hannunta ta kaita dakinsu “hada kayanki ki bisu zanyi maganin abin”