Sashe 155
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motar na tsayawa a gurguje taje ya gaishe da iyayensa da su Baba Hadir ya tashi Mama tana zolayarsa bai iya cewa komai ba sai dariya ya taho gida. Yana kama handle din kofar kafin ya murda ta riga shi. Kallon kallo su ka tsaya yiwa juna shi ya kara yi mata kyau da cika. Awwab na yi mata kallon fuskarta ta fada duk da kyaun da tayi mai fizgarsa. Rungumeta yayi tun a bakin kofa ya saki jakarsa yana kissing dinta cike da kewa. A hannu ya shige daki da ita sai da ta ga da gaske yake ta dakatar dashi saboda jininta da bai dauke ba. Bai damu ba ya rungumeta kawai a jikinsa yana fada mata yadda yayi kewarta.
"Tashi kayi wanka kaci abinci Hammana" ta ja hancinsa.
Wasa yake da gashinta ya dago ta su ka zauna "babu ko daya da zanyi sai kin fada min abinda ake boye min baby. Me ya sameki 4 days ago?"
Babu hanyar guduwa ta sunkuyar da kai ta ce "Hammana miscarriage nayi"
Jikinsa a take ya soma rawa ya janyota ya kankame "Schatzi dama kina da ciki?"
Kuka ta saka a hankali "Ban tabbatar ba shine na siyo abin PT idan ka dawo mu duba"
Ya dago fuskarta yana kallo "was it painful?"
Ta gyada kai ya sake rungumeta yana bata hakuri da rashinsa a kusa lokaci irin wannan. Sabuwar jinya aka koma yi kamar yau abin ya faru ya hanata yin komai. Iya kwana ukun da suka yi kulawa yake bata sosai. Ranar juma'a da daddare su ka tashi zuwa France inda ya cinye hutunsa ita kuma tana zuwa makatanta amma da ta dawo sai yawo tare da su Arifa ko ita kadai da Awwab. Ranar da zai tafi kuka tayi da kyar Tante ta shawo kanta.
**********
A hankali kwanaki ke tafiya cikin Ummi ya shiga watan haihuwa ga jarabawarsu ta karshe da suke yi. Lokacin Fauziyya ta kusa arba'in din Sahla jaririyarta. Zahra kuma cikinta yana wata biyar.
Cikin ikon Allah sai bayan kwana takwas da gamawa ta tashi da nakuda. Allah Ya taimaketa yadda ta sha wahalar cikin sai haihuwar ta zo mata cikin sauki saboda ko minti talatin basuyi ba da zuwa asibiti aka fito musu da sankacecen saurayi kamar Radhiya tayi kakinsa har dimple din gefe dayan.
Farincikin Zayyan Tureta a wannan rana ba zai fadu ba. Mairama ta sha addu'a sosai a wurinsa sai da tayi kuka. Ya kira Malamijo yace a yiwa shanu uku kudi a garkensa a yanka ayiwa mabukata sadaka. Mami ce ta yi mata wanka saboda a ganinta duk girman Mairama bata da wani cikakken experience game da haihuwa. Mama kuma ta sille jariri aka yi masa hoto ana turawa yayyensa da ke nesa. Radhiya ji tayi kamar tayi tsuntsuwa ta iso gida wurin baby da Ummi amma tana da sauran jarabawa daya sati mai zuwa. Ita da Tante da Arifah mai tsohon ciki suke zuwa siyayyar kayan baby saboda su Mammee sun ce ta hado kayan barka na gani da fada. Akwati biyar tayi manya manya uku na baby biyu na maijego.
Emzee da Ibrahim su ma makaranta ta sarke musu wuya ana ta jarabawa. Su Fauziyya ke rokon alfarmar kada ayi suna babu su Ummi ta ce babu taron da zata yi. Mama da Mami su ka ce sai anyi. A zahiri Ummi bata son yi saboda rashin Radhiya da Emzee amma kunya ba zata bari ta fada ba. Ita dai burinta ace 'ya'yan da suka sha gwagwarmaya tare dasu za'ayi komai.a lokacin da Allah SWT Ya dube su. Shima uban gayyar mijin nata kasa fada masa tayi sai da hillata ya ganota.
"Su Fillo wasa wasa kina da son 'ya'ya fa" yace yana dora jaririn a kafadarsa.
Tayi dariya "Duk abuna na kai dan mutan Tureta ne?"
"Ko kusa a bayana kike saboda haka ki rinka komawa gefe idan suna kusa ba ta ke nake yi ba"
"Naji amma ka bani jaririna don kasan shi dai bana jin kunyarsa kamar sauran"
Zama yayi kusa da ita ya ce "na rasa sunan da zan saka masa Fillo. Ga Major, Hadir da Baban Arifah cikinsu waye baiyi min halacci ba? Kinga ko da Hadir yake mai lalura nayi imanin da yana da hali kamarsu Mairama zai iya sadaukar da komai nasa domin iyalina."
"Na sani Sojana ko dai na haifo wasu ne a cike sunayen" ta ce tana dariya.
Ranar kwana hudu kenan da haihuwa nauyin 'yan uwan nasa rabin jiki yana damunsa ya rasa wa zaiyiwa takwara a cikinsu.
Washegari da aka kawo Mami tare da Daddy da Baba Hadir su ka zo. Daddy ya mika hannu ya karbi kyakyawan jaririn daga hannun Zayyan ya mikawa Hadir.
"Ni na yiwa Alheran yau kuma kaine da danka ka zaba masa suna don na rasa me yake damun abokinka sai wasa yake mana da hankali"
Murmushi Baba Hadir yayi ya duka ya yiwa yaron addu'a sannan ya dago kai yace "Allah Ya raya mana NASURULLAH"
Daddy yayi murmushi ya karbi yaron ya sumbace shi kumatun hagu da dama "hakika Allah mai kyauta da kari cikin nasarar da Ya bamu ne muka wayi gari mu ka ga wannan rana ace Zayyan ya dawo garemu har Allah Ya azurta shi da sake samun karuwa."
Kwalla ce ta taru a gefen idon Zayyan ya sa hannu yana kade ta Daddy yace "me nake gani haka? Are you still a Lady?"
Baba Hadir da Zayyan sai dariya yana cewa "wallahi namiji ne ranka ya dade"
Excellency Nasiruddeen Aliyu wanda ya sake samun kujerar gwamnan Plateau a daren ranar ya sauka a Abuja ganin wannan dan baiwa da za'a iya cewa alkawarin Allah Ya cika domin haihuwarsa baiwa ce. Sunansa da na Nasrullah daya ne duka daga nasara sai dai bambanci kadan shiyasa yace shi aka karrama aka yiwa takwara saboda haka gagarumar kyauta yayi masa wadda ta tsorata iyayensa sai dai yace babu abinda zai yiwa jinin Zayyan ya fadi domin ko me ya zama a rayuwa sanadiyar zubar jini da hawayen Tureta ne.
Kamar lokacin DK dan gidan Zayyan don babu abinda ya kware a fada irin Daada shima Nasrullah an dage taron sunansa sai yayyensa sun dawo nan da sati biyu ake sa ran kowa yana gida banda Zahra.
Tante ta tafi Nijar da kwana biyu Radhiya ta koma gidan Yousuf jiran Awwab yazo zasu tafi Abuja. Kafin.ya iso yayi booking hotel online daga airport ya gudu da matarsa sai washegari su ka hadu dasu Arifah a wurin convocation din Radhiyan. Kyaututtukan da ta samu ba kadan ba musamman saboda shirin Military Voice. An yaba mata sosai basu bar makarantar ba sai da a gaban shugaban makarantar tasu da Awwab ma'aikatan Aljazeera su ka kawo contract na shekara hudu wanda su ka bata tayi Military Voice Africa (MVA). Da amincewarta kuma anyi alkawarin acknowledging dinta a matsayin wadda ta samar da shirin suka nemi izinin yin Military Voice Asia da Europe. Kudin da zasu biyata ba na wasa bane bukatarsu duka kasashen Africa guda 53 taje ta gana da sojojinsu da matansu su kuma zasu ware lokaci domin sanya shirin sau daya a sati. Yadda za'a rinka dauka da gabatarwa duk yana cikin contract din. Awwab baiyi gaban kansa ba ya kira Daddy da Daada suka bashi goyon baya sannan ya yarda ta amince aka saka sunansa a matsayin wakilinta.
Kwana biyu su ka kara sai gida Nigeria da kwalinta na degree wanda ta fito da sakamako mai kyau. Iyaye da 'yan uwa an tayata murna. Da gudu ta shiga gida sai da ta dauki Nasrullah hankalinta ya kwanta. Kasa ta sauko dashi wurin Awwab ya rungumeta da babyn yana cewa Allah Ya nuna masa ranar da za ta haifa musu nasu.
**********
Shirye shiryen zuwa P.O.P din Emzee suke yi Daada yace Ummi babu inda zata saboda Nasrullah baiyi kwari ba. Sai da ta ajiye kunya ta dangana da hadashi da Daddy ya barta taje.
As expected Second Lieutenant Muhammad Zayyan Tureta ya fita da sakamako mafi kyau a wannan shekarar saboda kokari da kwazonsa musamman akan abinda ya shafi training dinsu. Ya sami lambar yabo kala kala iyayensa basu da abin cewa sai godiya ga Allah. A wannan rana Malamijo sai da yazo halartar taron sai dai ganin sojoji a kowace kusurwa rike da bindiga ya kada masa hanji. Tare su ka dunguma zuwa Abuja yau dai gashi a muhallin Mairama Daso. Yana rungume da karamin jikansa yana mai mika godiya ga Allah da Ya tsawaita kwanakinsa ya ga haduwar kan 'ya'yansa. Gida MashaAllah ya cika da 'yan uwa daga rugar Barkindo, Sakkwato, Nijar da Sumaila.
Sunan da ba'ayi ba aka hade da murnar kammala karatun Radhiya, Emzee, uwar gayya Mairama da bakon duniya Nasrullah. Major General Zayyan Tureta sai da yayi kukan farinciki a daki kafin ya sauko faefajiyar gidan inda ake taron. Yau shine Allah Ya yiwa arzikin ganin wannan rana wadda da sai dai ayi babu shi. Kyauttuka kam an sha su.
Ibrahim kamar ya lashe Zayyana don so shi kuwa Emzee da Rahima tsakaninsu sai satar kallon juna. Ta gama makaranta abinta tana jiran a fara karatu a school of nursing da ta sami gurbi. Emzee ya mamayeta yadda Awwab yace duk motsinta yana wurin amma babu yiwa juna magana. Ita ta sakawa ranta ta hakura dashi ne duk da tasan cewa yaudar zuciyarta take yi. Kullum sai ta jira text dinsa wanda babu kalmar soyayya sai nuna tarin kulawa.
Sai dare su Radhiya suka koma gida Awwab ya jikata da salon soyayyarsa. Washegari ya damka mata mukullin hadaddiyar motar da ya saya mata a matsayin graduation gift.
*********
SALLAMAR BANKWANA
Wata hudu bayan gama karatun Radhiya suka je gidan Daada da Awwab gaishesu. Emzee ya tafi wani training a Warri yanzu mukaminsa ya koma Lieutenant. A falo su ka yada zango tana yiwa Nasrullah uban 'yan kyuya wasa ya hade rai abinsa yana neman Ummi da idanu ta ce,
"Indai nice za ka zo ka sameni ne har gida kuma ba bari zanyi ka shigo ba"
"Ba dole ya rinka gudunki ba kina zare masa idanu" cewar Awwab ya karbe shi.
Kusa da Daada ta koma suna hira a hankali ta soma hade fuska tana sansana jikin kujera da su labule tana dagawa.
"Tashi kayi wanka kaci abinci Hammana" ta ja hancinsa.
Wasa yake da gashinta ya dago ta su ka zauna "babu ko daya da zanyi sai kin fada min abinda ake boye min baby. Me ya sameki 4 days ago?"
Babu hanyar guduwa ta sunkuyar da kai ta ce "Hammana miscarriage nayi"
Jikinsa a take ya soma rawa ya janyota ya kankame "Schatzi dama kina da ciki?"
Kuka ta saka a hankali "Ban tabbatar ba shine na siyo abin PT idan ka dawo mu duba"
Ya dago fuskarta yana kallo "was it painful?"
Ta gyada kai ya sake rungumeta yana bata hakuri da rashinsa a kusa lokaci irin wannan. Sabuwar jinya aka koma yi kamar yau abin ya faru ya hanata yin komai. Iya kwana ukun da suka yi kulawa yake bata sosai. Ranar juma'a da daddare su ka tashi zuwa France inda ya cinye hutunsa ita kuma tana zuwa makatanta amma da ta dawo sai yawo tare da su Arifa ko ita kadai da Awwab. Ranar da zai tafi kuka tayi da kyar Tante ta shawo kanta.
**********
A hankali kwanaki ke tafiya cikin Ummi ya shiga watan haihuwa ga jarabawarsu ta karshe da suke yi. Lokacin Fauziyya ta kusa arba'in din Sahla jaririyarta. Zahra kuma cikinta yana wata biyar.
Cikin ikon Allah sai bayan kwana takwas da gamawa ta tashi da nakuda. Allah Ya taimaketa yadda ta sha wahalar cikin sai haihuwar ta zo mata cikin sauki saboda ko minti talatin basuyi ba da zuwa asibiti aka fito musu da sankacecen saurayi kamar Radhiya tayi kakinsa har dimple din gefe dayan.
Farincikin Zayyan Tureta a wannan rana ba zai fadu ba. Mairama ta sha addu'a sosai a wurinsa sai da tayi kuka. Ya kira Malamijo yace a yiwa shanu uku kudi a garkensa a yanka ayiwa mabukata sadaka. Mami ce ta yi mata wanka saboda a ganinta duk girman Mairama bata da wani cikakken experience game da haihuwa. Mama kuma ta sille jariri aka yi masa hoto ana turawa yayyensa da ke nesa. Radhiya ji tayi kamar tayi tsuntsuwa ta iso gida wurin baby da Ummi amma tana da sauran jarabawa daya sati mai zuwa. Ita da Tante da Arifah mai tsohon ciki suke zuwa siyayyar kayan baby saboda su Mammee sun ce ta hado kayan barka na gani da fada. Akwati biyar tayi manya manya uku na baby biyu na maijego.
Emzee da Ibrahim su ma makaranta ta sarke musu wuya ana ta jarabawa. Su Fauziyya ke rokon alfarmar kada ayi suna babu su Ummi ta ce babu taron da zata yi. Mama da Mami su ka ce sai anyi. A zahiri Ummi bata son yi saboda rashin Radhiya da Emzee amma kunya ba zata bari ta fada ba. Ita dai burinta ace 'ya'yan da suka sha gwagwarmaya tare dasu za'ayi komai.a lokacin da Allah SWT Ya dube su. Shima uban gayyar mijin nata kasa fada masa tayi sai da hillata ya ganota.
"Su Fillo wasa wasa kina da son 'ya'ya fa" yace yana dora jaririn a kafadarsa.
Tayi dariya "Duk abuna na kai dan mutan Tureta ne?"
"Ko kusa a bayana kike saboda haka ki rinka komawa gefe idan suna kusa ba ta ke nake yi ba"
"Naji amma ka bani jaririna don kasan shi dai bana jin kunyarsa kamar sauran"
Zama yayi kusa da ita ya ce "na rasa sunan da zan saka masa Fillo. Ga Major, Hadir da Baban Arifah cikinsu waye baiyi min halacci ba? Kinga ko da Hadir yake mai lalura nayi imanin da yana da hali kamarsu Mairama zai iya sadaukar da komai nasa domin iyalina."
"Na sani Sojana ko dai na haifo wasu ne a cike sunayen" ta ce tana dariya.
Ranar kwana hudu kenan da haihuwa nauyin 'yan uwan nasa rabin jiki yana damunsa ya rasa wa zaiyiwa takwara a cikinsu.
Washegari da aka kawo Mami tare da Daddy da Baba Hadir su ka zo. Daddy ya mika hannu ya karbi kyakyawan jaririn daga hannun Zayyan ya mikawa Hadir.
"Ni na yiwa Alheran yau kuma kaine da danka ka zaba masa suna don na rasa me yake damun abokinka sai wasa yake mana da hankali"
Murmushi Baba Hadir yayi ya duka ya yiwa yaron addu'a sannan ya dago kai yace "Allah Ya raya mana NASURULLAH"
Daddy yayi murmushi ya karbi yaron ya sumbace shi kumatun hagu da dama "hakika Allah mai kyauta da kari cikin nasarar da Ya bamu ne muka wayi gari mu ka ga wannan rana ace Zayyan ya dawo garemu har Allah Ya azurta shi da sake samun karuwa."
Kwalla ce ta taru a gefen idon Zayyan ya sa hannu yana kade ta Daddy yace "me nake gani haka? Are you still a Lady?"
Baba Hadir da Zayyan sai dariya yana cewa "wallahi namiji ne ranka ya dade"
Excellency Nasiruddeen Aliyu wanda ya sake samun kujerar gwamnan Plateau a daren ranar ya sauka a Abuja ganin wannan dan baiwa da za'a iya cewa alkawarin Allah Ya cika domin haihuwarsa baiwa ce. Sunansa da na Nasrullah daya ne duka daga nasara sai dai bambanci kadan shiyasa yace shi aka karrama aka yiwa takwara saboda haka gagarumar kyauta yayi masa wadda ta tsorata iyayensa sai dai yace babu abinda zai yiwa jinin Zayyan ya fadi domin ko me ya zama a rayuwa sanadiyar zubar jini da hawayen Tureta ne.
Kamar lokacin DK dan gidan Zayyan don babu abinda ya kware a fada irin Daada shima Nasrullah an dage taron sunansa sai yayyensa sun dawo nan da sati biyu ake sa ran kowa yana gida banda Zahra.
Tante ta tafi Nijar da kwana biyu Radhiya ta koma gidan Yousuf jiran Awwab yazo zasu tafi Abuja. Kafin.ya iso yayi booking hotel online daga airport ya gudu da matarsa sai washegari su ka hadu dasu Arifah a wurin convocation din Radhiyan. Kyaututtukan da ta samu ba kadan ba musamman saboda shirin Military Voice. An yaba mata sosai basu bar makarantar ba sai da a gaban shugaban makarantar tasu da Awwab ma'aikatan Aljazeera su ka kawo contract na shekara hudu wanda su ka bata tayi Military Voice Africa (MVA). Da amincewarta kuma anyi alkawarin acknowledging dinta a matsayin wadda ta samar da shirin suka nemi izinin yin Military Voice Asia da Europe. Kudin da zasu biyata ba na wasa bane bukatarsu duka kasashen Africa guda 53 taje ta gana da sojojinsu da matansu su kuma zasu ware lokaci domin sanya shirin sau daya a sati. Yadda za'a rinka dauka da gabatarwa duk yana cikin contract din. Awwab baiyi gaban kansa ba ya kira Daddy da Daada suka bashi goyon baya sannan ya yarda ta amince aka saka sunansa a matsayin wakilinta.
Kwana biyu su ka kara sai gida Nigeria da kwalinta na degree wanda ta fito da sakamako mai kyau. Iyaye da 'yan uwa an tayata murna. Da gudu ta shiga gida sai da ta dauki Nasrullah hankalinta ya kwanta. Kasa ta sauko dashi wurin Awwab ya rungumeta da babyn yana cewa Allah Ya nuna masa ranar da za ta haifa musu nasu.
**********
Shirye shiryen zuwa P.O.P din Emzee suke yi Daada yace Ummi babu inda zata saboda Nasrullah baiyi kwari ba. Sai da ta ajiye kunya ta dangana da hadashi da Daddy ya barta taje.
As expected Second Lieutenant Muhammad Zayyan Tureta ya fita da sakamako mafi kyau a wannan shekarar saboda kokari da kwazonsa musamman akan abinda ya shafi training dinsu. Ya sami lambar yabo kala kala iyayensa basu da abin cewa sai godiya ga Allah. A wannan rana Malamijo sai da yazo halartar taron sai dai ganin sojoji a kowace kusurwa rike da bindiga ya kada masa hanji. Tare su ka dunguma zuwa Abuja yau dai gashi a muhallin Mairama Daso. Yana rungume da karamin jikansa yana mai mika godiya ga Allah da Ya tsawaita kwanakinsa ya ga haduwar kan 'ya'yansa. Gida MashaAllah ya cika da 'yan uwa daga rugar Barkindo, Sakkwato, Nijar da Sumaila.
Sunan da ba'ayi ba aka hade da murnar kammala karatun Radhiya, Emzee, uwar gayya Mairama da bakon duniya Nasrullah. Major General Zayyan Tureta sai da yayi kukan farinciki a daki kafin ya sauko faefajiyar gidan inda ake taron. Yau shine Allah Ya yiwa arzikin ganin wannan rana wadda da sai dai ayi babu shi. Kyauttuka kam an sha su.
Ibrahim kamar ya lashe Zayyana don so shi kuwa Emzee da Rahima tsakaninsu sai satar kallon juna. Ta gama makaranta abinta tana jiran a fara karatu a school of nursing da ta sami gurbi. Emzee ya mamayeta yadda Awwab yace duk motsinta yana wurin amma babu yiwa juna magana. Ita ta sakawa ranta ta hakura dashi ne duk da tasan cewa yaudar zuciyarta take yi. Kullum sai ta jira text dinsa wanda babu kalmar soyayya sai nuna tarin kulawa.
Sai dare su Radhiya suka koma gida Awwab ya jikata da salon soyayyarsa. Washegari ya damka mata mukullin hadaddiyar motar da ya saya mata a matsayin graduation gift.
*********
SALLAMAR BANKWANA
Wata hudu bayan gama karatun Radhiya suka je gidan Daada da Awwab gaishesu. Emzee ya tafi wani training a Warri yanzu mukaminsa ya koma Lieutenant. A falo su ka yada zango tana yiwa Nasrullah uban 'yan kyuya wasa ya hade rai abinsa yana neman Ummi da idanu ta ce,
"Indai nice za ka zo ka sameni ne har gida kuma ba bari zanyi ka shigo ba"
"Ba dole ya rinka gudunki ba kina zare masa idanu" cewar Awwab ya karbe shi.
Kusa da Daada ta koma suna hira a hankali ta soma hade fuska tana sansana jikin kujera da su labule tana dagawa.