Sashe 71
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ahaf, wannan tsakaninku ne ai. Kowa kawai ya dauki tasa fansar shine zan fi fahimta."
Baba Hadir sai da yayi dariya mai dan sauti yana ganin yadda mutumin nan ya dace da 'yan uwantaka da Zayyan saboda yanayin halinsa.
Murmushi shima yayi yana kallonsa "na baka dariya ko? Seriously ni yanzu ko Zayyan ne da kansa bai isa ya hanani kulle Maikudin nan ba so please a bar maganar. Zan sa a kira CP har gida za'a je a dauko min shi. Gobe idan an nuna masa maraya ba kudin maraya ba ma ko kallonsa bazai yi ba"
Ummi ma dai murmushi tayi tana jindadin ace hali nagarin da Zayyan ya nunawa wadannan bayin Allah shine yasa su tsayawa domin kula dasu. Addu'a take ta yi masa a zuciyarta na fatan dacewa da Rahamar Allah.
Hira sosai Excellency ya rinka jansu da ita yana cewa su saki jikinsu shi dasu zumunta ce mai karfi da Zayyan ya hada. Abinci aka rinka shigo dashi kala kala na alfarma yace kowa ya ci abinda yake so. Idan babu ra'ayinka ma ka fada a nemo.
"Arifah ga uwayenki ki kaisu wancan falon nasan zasu fi sakewa"
"Okay Dad" ta mike tsaye da fara'arta. Dauko musu abinci wani cikin guards din baban nata yayi aka kai musu inda yace. Kamar mahaifinta sai gata ta saki jiki dasu tana hira da tambayarsu sunayen yaransu mata su zama kawayenta.
Bayan sun gama ci a bangaren mazan Excellency ya nemi jin ko suna aiki. Major dama Daddy Haroun ne yake nema masa, to rabuwar yaransu ya sa yaji kunyar sake tuntubarsa. Shi kuma rashin samun wani abin kirki yasa baiyi masa magana ba.
"Major me zai hana in nema maka aiki a NITDA (national information technology development agency) tunda software engineer ne kai. Hadir kaima fa dole ne ka fita. Tunda jikinka yana motsi sai a nemi aikin da ba sai kayi magana ba. Rashin shiga mutane ma lalura ce mai zaman kanta "
"Your Excellency kada ka dorawa kanka nauyi daga haduwarmu yau don Allah" cewar Major.
"Wane irin nauyi? Bari na fada maka abinda baka sani ba. Ka ganni nan, ko da nayi retire amma har yanzu zuciyar tana tare da Army. Soja shine yasan soja. Mune muka san fadi tashin juna saboda haka dani daku bamu da zabin da ya wuce rungumar juna a matsayin 'yan uwa. Ko kuna ganin haduwar tamu anyita ne aci abinci a tashi ana shafa tumbi?"
Dariya yake yana maganar suma dole suka dara. Wannan mutum da saukin kai yake tamkar ba gwamna ba. Sai bayan la'asar suka kama hanyar komawa bayan yace zai sanar dasu ranar da zasu taho duka da iyalansu.
"Sannan a bawa Alheran numberta zan kirata da kaina ku tabbatar dai an fada mata matsayina gareta. Tana samun hutu a turo min ita don Allah."
Mota guda ya bayar aka mayar da Emzee makaranta bayan ya jikasu dukkansu da kyautar kudin da bai san adadinsu ba.
**********
Radhiya tasha bayani kala kala daga wurin dukkaninsu. Ranar itama kusan kwana tayi kuka tana tausayawa Umminta don sai da Nasara taji babu dadi an sa mata 'ya kuka.
Kwanaki kadan bayan haduwarsu sai ga offer din aiki har gida ga Major da Hadir. Kasar wa ka sani wa ya sanka kenan. Ba tare da bata lokaci ba an gama duk wani abu da ya kamata cikin sati guda. Major sai yayi wani course na wata uku a nan cikin sabuwar ma-aikatar tasu. Shi kuma Hadir an samar masa aiki mai sauki a Ministry of defence. Abu na karshe da yayi musu shine kama musu wasu gidaje flat a estate daya kusa da juna guda uku harda na Ummi wai idan tayi hutu ta taho ba sai ta takurawa kowa ba. Sai suka rasa da me zasu kwatanta karamcin wannan mutumi. A nasa bangaren kuwa yana musu kallon sun cancanci fiye da haka. Shine ya zauna da Zayyan a karshen rayuwarsa, shine suka ga kisa da mugunta tare zahiri suna kwantarwa juna hankali. Saboda haka nauyin iyalin Zayyan a wuyansa yafi cancanta.
Daddy sunyi waya da Mami yana yi mata bayanin komai sai hamdala take tana jin kamar ta taho. Dama kuma Ummi bata iya shiru ba Mama tana yin pt ta tabbatar ciki gareta ta kirata ta fada mata. Kwanaki hudu a tsakani Zahra ta sunkuto jaririnta kyakkyawa tubarakallah. Mami sai dada godewa Allah take da aka amincewa aurenta da Raji. Dan zaman da tayi dasu ta kara sakankancewa ba karamin so yake yiwa diyarta ba. Da yake kuma ba bahaushe bane babu ruwansa a gaban kowa matarsa ce tauraruwarsa. Kullum Zahra tana cikin annashuwa babu ta inda mijinta ya rageta. Ranar da jariri ya cika kwana bakwai aka saka masa suna Olufemi Abubakar Assiddiq amma suna kiransa Femi. Maman Raji kusan ita take komai na gyara da kula da maijego shiyasa suna cika sati uku lokacin Mami ta wuce wata a garin tace ita dai gida zata dawo.
"Mami bazaki jira nayi arba'in mu tafi tare ba?"
"Lada ya isa haka nima a barni na tafi wurin mijina"
"Laaaaaa Mami" Zahra tace tana dariya.
"An fada miki ku kadai kuka san kula da miji, ki fadawa Raji ya dawo min da booking dina jibi Allah guduwa zanyi sai kun taho"
Mami fa da gaske ta tubure dole aka fara shirin komawarta. Shatara ta arziki Raji ya hada mata da alkawarin suna hanya da zarar Femi ya cika wata uku. Da Awwab yaji labari da kyar ya samu ta kara kwana hudu akan yadda tayi niyya don su koma tare. Ba karamin kewar gida yayi ba duk da shi ya zabi rashin son komawa lokuta da dama. A ganinsa kawai an hade masa kai an biyewa su Mummy anki aura masa Alheran. Har lokacin kuma yaki saukowa daga fushin da yayi da tace bata son aurensa. Ko yaya ya tuna sai yaji bacin rai.
Awwab mai sakin fuska da yawan wasa yanzu ya zama a lallaba. Ba wai fada yake yi ba, shiga sabgar mutane ce gabadaya ya ja baya da ita. Ya rasa walwalarsa daga ranar da Alheran tace bata son aurensa.
Siyayya sosai ya yiwa Femi kamar yadda ya yiwa Jawad dan Fauziyya. Munirat kanwar Raji ce ta kawo masa yaron Mami da Zahra suna zaune dashi an kawo masa abinci. Ya kara kyau da jiki ga wani gashin baki da gemu da ya hada ya zagaye kyakkawar fuskarsa sai gyara da ya sha an rage shi sosai ya kwanta a fatar fuskar ya sake fiddo kyaunsa. Rike yaron yayi yana jin inama nasa ne da Alheran...tsaki ya yi batare da ya sani ba da sunanta ya fado masa.
"Lafiyarka kuwa?"
"Mami gajiya ce kawai. Zahra ki barmin shi kawai ki haifi wani" yace yana shafa kwantacciyar sumar kan yaron gwanin sha'awa.
"Ba dai ka tsaya tuzuranci kake jira ya cimmaka ba. Allah Ya bada sa'a. Idan rabon ayi aurenku tare da 'ya'yan naka ne mu ai bamu da ta cewa" Mami ta fada tana kawar da kai. Wai shi zuciya sai tayi masa maganar Radhiya yace ai sune suka bata izinin tafiya shi bazai bita ba. Mami takan ce masa maji ma gani idan rabon ka ga katin auren Radhiya ne ba shikenan ba. Duk lokacin da tace haka a zuciyarsa sai yace ba amin ba.
'Yar halak sai ta zabi daidai wannan lokacin ta kira Zahra. Har wani dan murmushi Zahran tayi tana dauka ta saka wayar a speaker ta karbi Femi da yake kuka za ta shayar dashi. Mami ta tashi ta koma cigaba da hada kayanta.
Awwab bai san me tayi ba kawai sai jin zazzakar muryar Radhiya yayi "Adda please please ki saka min naji muryar babyna"
Zahra tana kallon yadda ya dauke wuta ko motsi ya kasa yi. Wani irin yanayi na shauki ya bakunce shi. Shekara guda da watanni rabon da ya sanyata a idanunsa ko yaji muryarta.
"Adda kina jina?" Tace tana karyar da murya.
"Ina jinki Radhiya...fushi muke ni da Femi yau kwana uku baki kiramu ba"
"Exams....gidan ma bana zama sosai fa. Yanzu dai ki dan zungure shi kadan yayi kuka naji"
Duk abin Awwab sai da yayi murmushi suna hada ido da Zahra ya cigaba da tsakurar abincin dake gabansa. Tana nan da halinta wato.
"Dan nawa zan zungura Radhiya? To ko dai balotellin kike so nayi miki? Ina da sabon scisssors mai kaifi"
Dariya tayi da tasa tsigar jikin Awwab tashi saboda yadda yaji muryarta har tsakar kansa. Dannewa yake kada Zahra ta sami damar tsokanar shi tace tayi galaba a kansa.
"To ni shikenan bazan ji muryarsa ba" ta fada cikin shagwaba.
Idanunta akan Awwab tana ganin wani annuri da yake bayyana gareshi a hankali tace "zan ga ranar da zaki girma. Anyway yaushe zaki je Nigeria?"
"Saura na exams biyu amma Yousuf yace na jira mu tafi tare nan da kamar two weeks I think. Zamu fara zuwa Agadez ne sannan mu taho"
"Yousuf dinnan yana ji dake" Zahra tace tana dage gira daya tare da kawar da kai daga kallon Awwab da ya tattaro hankalinsa garesu batare da niyya ba.
"Kawai yana da kirki ne. Kiyi min addu'ar exams"
"Allah Ya bada sa'a, ni dai ki tabbata kinzo lokacin da zani"
Muryar namiji Awwab yaji yana kiranta da Alheran ya tashi a fusace ya bar falon. Meyasa shi bazai kirata Radhiya ba kamar yadda kowa yake fada. Da takaicin wannan abu ya kwana. Washegari jirgin dare suka bi zuwa Abuja. A hanya ya rasa yadda zaiyi ya tambayi Mami waye Yousuf kada tace har yanzu ya damu da Radhiya. Shi ba damuwa da ita yayi ba kawai dai curiosity ne.
Dreban Daddy da Ibrahim ne suka je daukarsu. Mummy ta kasa boye murnarta da suka shiga estate din. Wai sune a gida irin wannan mai kyau kuma Major ya sami aiki. Awwab ma yayi murna sosai ya kuma yaba da unguwar da iyayen nasa suke.
Nata gidan da sauran gyara na kayayyakin da zasu saka saboda bata nan. Abubuwa kadan ta iya fadawa Daddy a dauko mata daga Katsina. Sauran kuwa sai tazo da kanta.
Baba Hadir sai da yayi dariya mai dan sauti yana ganin yadda mutumin nan ya dace da 'yan uwantaka da Zayyan saboda yanayin halinsa.
Murmushi shima yayi yana kallonsa "na baka dariya ko? Seriously ni yanzu ko Zayyan ne da kansa bai isa ya hanani kulle Maikudin nan ba so please a bar maganar. Zan sa a kira CP har gida za'a je a dauko min shi. Gobe idan an nuna masa maraya ba kudin maraya ba ma ko kallonsa bazai yi ba"
Ummi ma dai murmushi tayi tana jindadin ace hali nagarin da Zayyan ya nunawa wadannan bayin Allah shine yasa su tsayawa domin kula dasu. Addu'a take ta yi masa a zuciyarta na fatan dacewa da Rahamar Allah.
Hira sosai Excellency ya rinka jansu da ita yana cewa su saki jikinsu shi dasu zumunta ce mai karfi da Zayyan ya hada. Abinci aka rinka shigo dashi kala kala na alfarma yace kowa ya ci abinda yake so. Idan babu ra'ayinka ma ka fada a nemo.
"Arifah ga uwayenki ki kaisu wancan falon nasan zasu fi sakewa"
"Okay Dad" ta mike tsaye da fara'arta. Dauko musu abinci wani cikin guards din baban nata yayi aka kai musu inda yace. Kamar mahaifinta sai gata ta saki jiki dasu tana hira da tambayarsu sunayen yaransu mata su zama kawayenta.
Bayan sun gama ci a bangaren mazan Excellency ya nemi jin ko suna aiki. Major dama Daddy Haroun ne yake nema masa, to rabuwar yaransu ya sa yaji kunyar sake tuntubarsa. Shi kuma rashin samun wani abin kirki yasa baiyi masa magana ba.
"Major me zai hana in nema maka aiki a NITDA (national information technology development agency) tunda software engineer ne kai. Hadir kaima fa dole ne ka fita. Tunda jikinka yana motsi sai a nemi aikin da ba sai kayi magana ba. Rashin shiga mutane ma lalura ce mai zaman kanta "
"Your Excellency kada ka dorawa kanka nauyi daga haduwarmu yau don Allah" cewar Major.
"Wane irin nauyi? Bari na fada maka abinda baka sani ba. Ka ganni nan, ko da nayi retire amma har yanzu zuciyar tana tare da Army. Soja shine yasan soja. Mune muka san fadi tashin juna saboda haka dani daku bamu da zabin da ya wuce rungumar juna a matsayin 'yan uwa. Ko kuna ganin haduwar tamu anyita ne aci abinci a tashi ana shafa tumbi?"
Dariya yake yana maganar suma dole suka dara. Wannan mutum da saukin kai yake tamkar ba gwamna ba. Sai bayan la'asar suka kama hanyar komawa bayan yace zai sanar dasu ranar da zasu taho duka da iyalansu.
"Sannan a bawa Alheran numberta zan kirata da kaina ku tabbatar dai an fada mata matsayina gareta. Tana samun hutu a turo min ita don Allah."
Mota guda ya bayar aka mayar da Emzee makaranta bayan ya jikasu dukkansu da kyautar kudin da bai san adadinsu ba.
**********
Radhiya tasha bayani kala kala daga wurin dukkaninsu. Ranar itama kusan kwana tayi kuka tana tausayawa Umminta don sai da Nasara taji babu dadi an sa mata 'ya kuka.
Kwanaki kadan bayan haduwarsu sai ga offer din aiki har gida ga Major da Hadir. Kasar wa ka sani wa ya sanka kenan. Ba tare da bata lokaci ba an gama duk wani abu da ya kamata cikin sati guda. Major sai yayi wani course na wata uku a nan cikin sabuwar ma-aikatar tasu. Shi kuma Hadir an samar masa aiki mai sauki a Ministry of defence. Abu na karshe da yayi musu shine kama musu wasu gidaje flat a estate daya kusa da juna guda uku harda na Ummi wai idan tayi hutu ta taho ba sai ta takurawa kowa ba. Sai suka rasa da me zasu kwatanta karamcin wannan mutumi. A nasa bangaren kuwa yana musu kallon sun cancanci fiye da haka. Shine ya zauna da Zayyan a karshen rayuwarsa, shine suka ga kisa da mugunta tare zahiri suna kwantarwa juna hankali. Saboda haka nauyin iyalin Zayyan a wuyansa yafi cancanta.
Daddy sunyi waya da Mami yana yi mata bayanin komai sai hamdala take tana jin kamar ta taho. Dama kuma Ummi bata iya shiru ba Mama tana yin pt ta tabbatar ciki gareta ta kirata ta fada mata. Kwanaki hudu a tsakani Zahra ta sunkuto jaririnta kyakkyawa tubarakallah. Mami sai dada godewa Allah take da aka amincewa aurenta da Raji. Dan zaman da tayi dasu ta kara sakankancewa ba karamin so yake yiwa diyarta ba. Da yake kuma ba bahaushe bane babu ruwansa a gaban kowa matarsa ce tauraruwarsa. Kullum Zahra tana cikin annashuwa babu ta inda mijinta ya rageta. Ranar da jariri ya cika kwana bakwai aka saka masa suna Olufemi Abubakar Assiddiq amma suna kiransa Femi. Maman Raji kusan ita take komai na gyara da kula da maijego shiyasa suna cika sati uku lokacin Mami ta wuce wata a garin tace ita dai gida zata dawo.
"Mami bazaki jira nayi arba'in mu tafi tare ba?"
"Lada ya isa haka nima a barni na tafi wurin mijina"
"Laaaaaa Mami" Zahra tace tana dariya.
"An fada miki ku kadai kuka san kula da miji, ki fadawa Raji ya dawo min da booking dina jibi Allah guduwa zanyi sai kun taho"
Mami fa da gaske ta tubure dole aka fara shirin komawarta. Shatara ta arziki Raji ya hada mata da alkawarin suna hanya da zarar Femi ya cika wata uku. Da Awwab yaji labari da kyar ya samu ta kara kwana hudu akan yadda tayi niyya don su koma tare. Ba karamin kewar gida yayi ba duk da shi ya zabi rashin son komawa lokuta da dama. A ganinsa kawai an hade masa kai an biyewa su Mummy anki aura masa Alheran. Har lokacin kuma yaki saukowa daga fushin da yayi da tace bata son aurensa. Ko yaya ya tuna sai yaji bacin rai.
Awwab mai sakin fuska da yawan wasa yanzu ya zama a lallaba. Ba wai fada yake yi ba, shiga sabgar mutane ce gabadaya ya ja baya da ita. Ya rasa walwalarsa daga ranar da Alheran tace bata son aurensa.
Siyayya sosai ya yiwa Femi kamar yadda ya yiwa Jawad dan Fauziyya. Munirat kanwar Raji ce ta kawo masa yaron Mami da Zahra suna zaune dashi an kawo masa abinci. Ya kara kyau da jiki ga wani gashin baki da gemu da ya hada ya zagaye kyakkawar fuskarsa sai gyara da ya sha an rage shi sosai ya kwanta a fatar fuskar ya sake fiddo kyaunsa. Rike yaron yayi yana jin inama nasa ne da Alheran...tsaki ya yi batare da ya sani ba da sunanta ya fado masa.
"Lafiyarka kuwa?"
"Mami gajiya ce kawai. Zahra ki barmin shi kawai ki haifi wani" yace yana shafa kwantacciyar sumar kan yaron gwanin sha'awa.
"Ba dai ka tsaya tuzuranci kake jira ya cimmaka ba. Allah Ya bada sa'a. Idan rabon ayi aurenku tare da 'ya'yan naka ne mu ai bamu da ta cewa" Mami ta fada tana kawar da kai. Wai shi zuciya sai tayi masa maganar Radhiya yace ai sune suka bata izinin tafiya shi bazai bita ba. Mami takan ce masa maji ma gani idan rabon ka ga katin auren Radhiya ne ba shikenan ba. Duk lokacin da tace haka a zuciyarsa sai yace ba amin ba.
'Yar halak sai ta zabi daidai wannan lokacin ta kira Zahra. Har wani dan murmushi Zahran tayi tana dauka ta saka wayar a speaker ta karbi Femi da yake kuka za ta shayar dashi. Mami ta tashi ta koma cigaba da hada kayanta.
Awwab bai san me tayi ba kawai sai jin zazzakar muryar Radhiya yayi "Adda please please ki saka min naji muryar babyna"
Zahra tana kallon yadda ya dauke wuta ko motsi ya kasa yi. Wani irin yanayi na shauki ya bakunce shi. Shekara guda da watanni rabon da ya sanyata a idanunsa ko yaji muryarta.
"Adda kina jina?" Tace tana karyar da murya.
"Ina jinki Radhiya...fushi muke ni da Femi yau kwana uku baki kiramu ba"
"Exams....gidan ma bana zama sosai fa. Yanzu dai ki dan zungure shi kadan yayi kuka naji"
Duk abin Awwab sai da yayi murmushi suna hada ido da Zahra ya cigaba da tsakurar abincin dake gabansa. Tana nan da halinta wato.
"Dan nawa zan zungura Radhiya? To ko dai balotellin kike so nayi miki? Ina da sabon scisssors mai kaifi"
Dariya tayi da tasa tsigar jikin Awwab tashi saboda yadda yaji muryarta har tsakar kansa. Dannewa yake kada Zahra ta sami damar tsokanar shi tace tayi galaba a kansa.
"To ni shikenan bazan ji muryarsa ba" ta fada cikin shagwaba.
Idanunta akan Awwab tana ganin wani annuri da yake bayyana gareshi a hankali tace "zan ga ranar da zaki girma. Anyway yaushe zaki je Nigeria?"
"Saura na exams biyu amma Yousuf yace na jira mu tafi tare nan da kamar two weeks I think. Zamu fara zuwa Agadez ne sannan mu taho"
"Yousuf dinnan yana ji dake" Zahra tace tana dage gira daya tare da kawar da kai daga kallon Awwab da ya tattaro hankalinsa garesu batare da niyya ba.
"Kawai yana da kirki ne. Kiyi min addu'ar exams"
"Allah Ya bada sa'a, ni dai ki tabbata kinzo lokacin da zani"
Muryar namiji Awwab yaji yana kiranta da Alheran ya tashi a fusace ya bar falon. Meyasa shi bazai kirata Radhiya ba kamar yadda kowa yake fada. Da takaicin wannan abu ya kwana. Washegari jirgin dare suka bi zuwa Abuja. A hanya ya rasa yadda zaiyi ya tambayi Mami waye Yousuf kada tace har yanzu ya damu da Radhiya. Shi ba damuwa da ita yayi ba kawai dai curiosity ne.
Dreban Daddy da Ibrahim ne suka je daukarsu. Mummy ta kasa boye murnarta da suka shiga estate din. Wai sune a gida irin wannan mai kyau kuma Major ya sami aiki. Awwab ma yayi murna sosai ya kuma yaba da unguwar da iyayen nasa suke.
Nata gidan da sauran gyara na kayayyakin da zasu saka saboda bata nan. Abubuwa kadan ta iya fadawa Daddy a dauko mata daga Katsina. Sauran kuwa sai tazo da kanta.