← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 157

Sashe 49

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kada kaje kayi min kwace kana wannan lumshe idanun da shan kamshi tace ta fasa na fiye surutu"

Emzee sai dariya suka shiga tsokanar juna irin yadda dai matasa sa'o'insu suke yi.

Tun daga ciki ya soma hangota tana tsaye suna magana da wani da sau biyu yana ganinsa a cikin gidan. Me yiwuwa dai shima kanin Umminta ne. Sallama Awwab yayi masa suka gaisa ya shige ciki.

"Emzee yace kana kirana kuma wai a waje"

Hannuwansa ya zura a aljihu yana kallonta "aikenki zanyi dama amma na fasa dare yayi" 

"Yo ni ina tsoron dare ne kamar ba soja ba"

Tafiya ya soma yi kawai batare da sanin inda zashi ba ta bishi suna tafe gefe da gefe. 

"Alheran" ya kira sunanta daga can kasan makoshi sai da taji a jikinta.  

"Uhmm"

"Bana son ki zama soja"

Bata ga alamun wasa ba a fuskarsa shiyasa taji gabadaya ya karyar mata da gabbai. Yau sau biyu yana cewa bazata yi soja ba. Na dazu haushi ya bata sosai amma yanzu da ya fada sai taji tana son sanin dalilinsa na fadin hakan. Me yasa shi da take tunanin zai taimaka mata ta sami biyan bukata zai rinka neman rabata da abinda ta girma dashi a ranta. Kafin ta tambaye shi ya cigaba da yi mata bayani.

"Ban taba tunanin zanyi wani karatun da bai shafi zama soja ba. Infact son da nake yiwa duk wata harka ta military ce tasa na zama pilot. Na rasa abubuwa da yawa saboda aikin soja. Mahaifina ya dawo gida da kafa daya da lalurar da taso dauke masa dukkan tunaninsa, Baba Hadir yana zaune a wheelchair babu motsi babu magana" tsayawa yayi ya juyo sosai yadda zasu fuskanci juna. Ba tsayinsu daya ba amma itama tana da tsaho daidai gwargwado, duk da haka sai taji kamar ta kankance a gabansa "na rasa mutum na biyu a rayuwata da na baiwa matsayin uba sannan kike tunanin Awwab zai iya bari ki zama soja?"

Tambayar ta soki zuciyarta kamar yadda maganganun suka yi tasirin da ya sanya taji kamar tayi kuka. Babu wani abu daya da zata iya tunawa game da mahaifinta idan ka cire kamaninsa na hoto. Amma labaran da take ji game dashi ya sa take da burin zama kamarsa. Tana so nan gaba ko me ta zama idan an tashi ace 'yar Zayyan Muhammad Tureta ce.

"I may be selfish Alheran amma daga jiya zuwa yau keman kin sani cewa bazan so wani abu da zai taba min ke ba."

Kallonsa tayi ta ga idanunsa kyam a kanta sai tayi murmushi "me kake so na karanta?"

"Are you serious? Kin hakura?"

"Ba dole ba kana yi kamar zaka yi min kuka" tace tana dariya. Hamma yafi karfin komai a wurinta zuciyarta ke sanar da ita.

Da sauri tayi hanyar gida dama ba nisa suka yi ba yabi bayanta yana murmushi har suka shiga soron. Tsayar da ita yayi ya koma mota ya dauko ledar tsarabarta ya damka mata.

"Ga naki kayan ledar Allah Yasa komai yayi miki"

Tayi murna sosai ta dauko takalmi daya ta gwada yana haskawa da wayarsa don ta gani saboda hasken soron bashi da yawan da zata gani da kyau. Guda uku ne takalman biyu da jakarsu sai turare biyu, dankunne da sarka da tarkacen kayan kwalliyar da bata san yaya zata yi dasu ba. 

Sai da ta gama godiyarta ta karbi wayarsa tace ya buda mata hotuna ta gani. Daya bayan daya take binsu wani tace yayi kyau wani ta tsokane shi. Da sannu ta iso wurin hotunansa da uniform dinsa. Nan fa ta rude tana ta yaba yadda kayan suka burgeta.

Murmushi yayi mata yace "ko dai ta kusa kare miki ne zaki hakura da dreba"

"Sai soja ko likita"

"Time will tell"

"Me kace?"

"Babu komai"

Cigaba da kallon tayi ta budo wani yana tsaye da members na cabin crew dinsa a wata tafiya da suka yi da ta dace da birthday dinsa. Shi ya ma manta kafin a budewa fasinja su shiga jirgin suka kawo masa cake da gifts saboda yadda suke jindadin aiki dashi. Yana sakewa da kowa ayi raha ya wuce. Kasa yin gaba tayi da hoton duk da yayi kyau sosai amma 'yan matan air hostess din sun wani saka shi a tsakiya. Tayi gaba a hankali sai da ta gwammace bata yi ba. Wata cikinsu ce take tura masa cake a baki sauran suna tafi aka dauka. Abinda bata taba ji bane a rayuwarta na tsananin kishi ya saukar mata a lokacin. Ji tayi ina ma Ghazalatu ce ke bashi akan wannan mai dan skirt din da tasha kwalliya kamar 'yar tsana.

Gani yayi tayi shiru ya fada mata lokacin da aka yi hoton. Daga murya tayi ba da niyya ba sai dai bacin ranta a lokacin ya kai makura "ita ma wannan matsayinsu daya da waccan ne?"

"Waccan?"

Da gatse tace "Matar da zaka aura ba"

"Abokan aikina ne fa"

"To" tace muryarta tana rawa. Duk yada taso boyewa kasawa tayi hawaye kamar famfo suka shiga sintiri a kumatunta. Karbe wayar yayi ya haske mata fuska tayi saurin rufewa da tafin hannunta da kasan hijab din tana kara sautin kukan.

"Ya Allah, me nayi miki kuma?"

"Babu komai"

Hankalinsa a tashe yace "amma kike wannan kukan, akwai abinda yake damunki ne?"

"Nima ban sani ba" ta sake bare baki kukan yana karuwa.

Hoton ya kula tana kallo ya dawo da wayar saitin da zata gani sosai. Gabadaya hotunan ranar birthday din nasa akan idonta yayi marking ya gogesu. Babu kunya murmushi ya bayyana a saman labbanta.

Dage gira yayi yana mata wani irin kallo "silly girl! Kishi ko?  Ko dai ta kare miki dinne ban sani ba?"

Dinke fuska ta sake yi ta tashi. Yayi ta kiranta haushin kanta da kukan da tayi yasa taki amsa masa. Samun kansa yayi da sakin murmushi shima yaji dadi ta damu dashi. Girgiza kai yayi lokaci guda yana kwabar kansa da cewa ya kiyayi wuce gona da iri akan kanwar tasa. Duk abinda yake yi mata 'yan uwantaka da shakuwa ce

**********
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Rtd Major Mustapha tun a hanya suna ta waya da Baffa Habubakari da babban dansa da ya rako shi wan Zakari. Da kuma wannan soja wanda a yanzu yake rike da mukamin Captain shima kansa. Rikon amana da cigaban zamani yasa bai taba gazawa a wurin karbar sakon Major ba. 

A harabar Giginya Hotel inda suke sa ran yin masauki suka hadu. Da motoci biyu hilux cike da sojiji majiya karfi wanda kallo daya zaka yi musu duk wani burbudin fitsara da rashin kunya su kama gabansu Captain Onomza ya zo wurin.

Ya gaisa dasu Daddy ransa a matukar bace yace a yanzu fa zasu wuce a kamo mutumin.

"Calm down Captain, muyi hakuri zuwa wayewar gari"

"I am sorry Sir, I cannot wait Sir" ce amsar da ya bayar yana 'yar dariya saboda har yanzu yana girmama Major.

Major ma burinsa ya ga Maikudi a hannu. Tunanin wadanda suka zo dasu yayi ga gajiya ga kuma firgicin ganin sojojin. To su ma sunyi na'am da a tafin shiyasa babu bata lokaci suka wuce gidan.

Jume ce tsaye jikin bango domin baiwa kanta kariya kada ta fadi saboda zafin kalaman Maikudi.

"Kannenka kayi musu tsawa nima kayi min tsawa ina mahaifiyarka?"

"Idan bakya so sai ki bar wannan magana. Abinda ya faru ya riga ya faru amma sai tado zancen kike. To wa zaki burge cikinsu? 'Yan uwan matar nan suna da arzikin kula da ita da yaranta, meye don nima naci daga arzikinsu. Ba wan ubansu nake ba?"

"Hakkinka ne da zaka ci?"

"Ho Jume, kin ma manta lokacin da ki ka matsawa Zayyanun da kanki akan ya baki kudin gadonsa."

Sai da taji ba dadi da ta tuna irin abubuwan da ta rinka yi wa Zayyan a wancan lokacin. Gashi ya tafi ya bar mata duniyar dan cikinta ya zame mata kadangaren bakin tulu.

"Kinga ni tashi zanyi daga gidannan nan da sati guda zaki huta da ganina. Gobe zan zo da masu aikin kwashe kaya" yana kaiwa nan yasa kai ya fita ya bar mahaifiyarsa da kunar rai.

Majalisarsu yaje ya zauna gefen wani gida inda suke wuni suna buga karta, gulmar duk mai wucewa da kallon 'yan mata. Hira suke gasu dai magidanta amma babu mutumci a tare dasu sai kyakyata dariya suke abinsu. Da yake lungun motoci bazasu iya shiga ba daga gefen titi suka yi parking sojoji suka rinka durowa daga motar harda masu bindigogi kirar AK47. Hankulan jama'a tuni suka tashi ana tunanin yau ko lafiya unguwar. Da karfinsu suke tafiya Baffa Habubakari da dansa Manu nadamar biyo wannan zugar sojoji suke yi. Tsoro suke kada su manta cewa tare suke a kafta musu hancin bindiga.

Su Maikudi sai gani suka yi mutane na shigewa gida da sauri ga sojoji suna tafe da sassarfa. Wasu cikinsu zasu tashi ya ce su zauna.

"Meye abin tsoro a soja, kanina ma har ya rasu soja ne. Ko wane mai tsautsayin suka biyo har cikin unguwa don jaraba wa ya sani"

Kamar ance ya kalli tsakiya ya hango wani mutum cikin shadda dinkin tazarce ya karkace hula yana rike da sanda ruwan kasa daga samanta da yake a lankwashe kasan kuma baki ne. Dogo ne kakkaura mai cikar haiba da zati.

"Banten uba" Maikudi yace da ya tabbatar wannan mutumin ne da suka zo neman Radhiya da uwarta kwanakin baya. Jikinsa har mazari yake don tsoro garin sauri ya bar wurin ya cambala kafa a cikin kwatar gabansa. Bai ko damu ba ya soma sauri. Captain Onomza ya gane shi da sauri ya bada dokar a damko masa shi.

"Don't let him get away" yace da karfi.

Mutum daya ne yayi kukan kura ya kwaso Maikudi gabadayansa sai gashi kwance a gaban Captain Onomza.
Chapter 49 · 0% Book details