Sashe 139
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ranar Mami itama da nata gayyar suka wuce Abuja. Abinda ya bata mamaki bai wuce biyosu da Fauziyya da Bilal suka yi ba. A take ta nunawa Fauziyya bata son yawo ta bari har sai ana gobe Bilal yace shine yake son su tafi saboda akwai abinda zasu yi da Raji da angwayen. Bata matsa son jin ko meye ba suka kama hanya.
**********
A Abuja azahar ta riskesu saboda sammakon da suka yi. Dan kwana biyun da babu Mairama Daada yaji jiki saboda har yau gani yake ko daya bisa dari na fanshe rashin matarsa baiyi ba. Yana falonsa na kasa suka iso Radhiya ta makalkale shi yana dariya. Ita kuma ta lura hakan na masa dadi sai yaji kamar bai rasa komai ba na rayuwar 'ya'yansa shiyasa take yi. Rahima na gefe tana murmushi ta gaisheshi ya sakar mata fuska fiye da yadda yake yi kwanakin baya da ta zo.
"Auta bakya laifi wannan daurin har ido na meye?"
Ummi ce tayi masa bayani Radhiya ta kwance ya ga idon ransa kuwa ya baci kamar ya ga Salame a gabansa ya saita mata fuska. Da kansa ya kira Emzee da ya bar gidan tun safe kuma saboda zuwan Rahiman ne yace yazo bayan la'asar ya kaisu asibiti. Bai ma san waye za'a kai ba amma dolensa ya amsa umarnin mahaifinsa.
Karfe hudu da rabi ya iso Ummi ta sauko sanye da riga da zani da hijab ta tura mai aiki kiran Rahima. Tamke fuska yayi bayan sun gaisa tunda yaji sunanta. Doguwar rigar atampa ce a jikinta ta dora rigar sanyi mai zip ta gaba mai dan fadi tare da hijabi fashion wanda ya zarta kafadunta da kadan. Idonta kuwa hankici tasa ta dafe shi bata son haske na ratsa shi.
"Ina wuni" tace da ta iso kusa da shi da Ummi.
Waya ya shiga dannawa baji ba gani yana a'uziyya a zuci wai kada a sake makalo shi da wani nau'in siddabarun a cikin muryarta da take masa dadi har yau.
"Baka ji ana gaisheka ne?" Ummi tace tana nufar kofa za ta fita.
Sai da ya harari Rahima mamaki ya sake kamata sannan yace "na amsa Ummi baki ji bane"
"Wai haka Rahima?"
"Ummi ya amsa" tace tana murmushi.
Emzee na ganin Ummi tayi waje ya dawo kusa da Rahima kamar gaske ya kuma daure fuska "babu kunya kike yi mata karya, ni nace ki rufa min asiri ne?"
Jikinta ne ya soma rawa saura kadan ta fashe da kuka tace kasa yayi hakuri kawai ta wuce. Da ta karasa bakin motar ma baya ya bude duka bangare biyun yana cewa wai su shiga baya tare zasu fi jindadi. Ummi bata ce komai ba tayi zamanta yaji dadin hakan saboda don bai san karyar da zaiyi mata ba idan ta tambayeshi.
Asibitin Samu Wadata su ka je inda suna zaune Ummi ta saka shi ya bada numbar katinsu aka dauko sannan suka yi zaman jiran a kira su. Basu jima ba kuwa aka kira Rahima da Ummi suka shiga wurin likitan. Bayan ya duba idon sosai yace musu wasu jijiyoyi ne suka toshe sakamakon jinin da ya daskare a ciki shi ya kawo kumburin idon. Magani ya rubuta mata na sha da digawa domin sace kumburin sannan zasu dawo bayan kwana biyar a auna lafiyar idon.
**********
Kwana biyun bayan dawowarsu an cigaba da gyara Radhiya sosai. Mama ce da aikin hadata da kayayakinsu na Sakkwatawa da kuma na wata kawarta Maman Farida. Sai kuma takunkuminta na hana Awwab ganin amarya. Tun ranar da su ka dawo daga Sumaila ta fada masa da kanta. Manufarta bai wuce samun lokaci da kyau a gyare mata 'ya ba. Sannan kuma tasan cewa idan ba haka tayi musu ba haka zaiyi ta zuwa kullum yana bata show tunda yasan matarsa ce. Idan kuwa sai da komai ya kammala ne dole ya fi ganin tasirin aikin.
Ba wani damuwa yayi sosai ba saboda shima bashi da isasshen lokaci. Tun safe suke kulle gidan Mami idan ta fita shi da Bilal, Yousuf, Raji, Emzee da Ibrahim sai wani mutum guda daya da yake zuwa sai dare ya tafi. Mama tayi juyin duniya Mami ta fada mata me suke yi taki su ma kuma kowa ya rufe bakinsa. Yau da yake neman alfarmar son ganin Radhiya lallabowa yayi yana mata magiya. Wasa yake yiwa DK da yake hannunsa yana mata magana.
"Ko awa biyu bana jin zamuyi don muma abinda yake gabanmu akwai cin lokaci"
"Na yarda amma da sharadin sai ka fada min me kuke yi kai da 'yan uwanka"
Dariya yayi don kowa yasan tana binsu daidai suna zillewa ne.
"Big surprise ne Mamanmu ni dai a taimaka kada zuciyar......"
Da sauri tace "Ahhhh dena kiran zuciya yanzu zan kira na sanar da ita."
"Allah Ya ja da ran Mama. Nagode" yace tare da ajiye DK a cikin wani abun kwanciyar yara yana murmushi.
Bayan fitarsa ta kira Ummi ta fada mata gobe zai zo daukar Radhiya zasu je yin hotuna wanda za'ayi amfani dasu a wurin dinner din. A wurin Ummi Radhiya taji zancen ta kama yi masa mitar bai fada da wuri ba yanzu wane kaya zata saka yace ita kadai yake bukata goben komai is ready.
"Hammana da ya ka shirya komai ban sani ba?" Tace cikin jindadi.
Murmushi yayi mai sauti "ke dai ki shirya around 12 zan zo. Love you...sai munyi waya anjima ana jirana"
Saroro tayi da wayar a hannu tana tunanin me yake dauke masa hankali ne yanzu bashi da lokacin hirar kirki. Da dare kuma ba wani jimawa suke ba yake kwanciya. Washegari kafin ya iso ta gama shiri tun daren jiya sunyi magana da Arifah itama Yousuf ya fada mata zasu je kuma kada ta tanadi kayan sakawa. Zahra ce ta yi mata light make up mai kyau fuskarta kamar ka dauke ka dasa ga wani irin kamshi mai rikita kwakwalwa da sanyaya ruhi. A kitchen ta yiwa Ummi sallama saboda yace bazai shigo ba sai sun dawo gudun bata lokaci.
Awwab kasa dauke ido yayi daga kanta tun fitowarta har ta iso gaban motar inda yake tsaye rike da kofa ya bude mata. Murmushi tayi tana sunkuyar da kai haka kawai wani irin nauyinsa take ji. Tana shirin zama ya duko daidai kunnenta "you look sweet"
Fadada murmushin tayi ta rufe fuska da tafukan hannayenta. Sai da ya zauna ta soma gaishe shi idanunsa a kanta kamar zai cinyeta.
"Hammana ina wuni?" Tace da karamar murya tana jin faduwar gaba.
"Lafiya kalau my baby."
Yanzu ma murmushi kawai tayi kamar ba ita ba wani salihanci ne yayi mata dabaibayi yayin da kwanakin barin iyayenta da zama cikakkiyar matar Awwab suke gabatowa. Tayar da motar yayi ya kama hannunta ya rike yana magana a hankali amma idanunsa na kan titi.
Cikin muryarsa mai tafiya da zukata wadda har yau idan Radhiya taji sai ta sanyata cikin wani irin yanayi na tsanananin son mai muryar yace "kinsan wani abu?" Kai ta girgiza ya cigaba da magana "yau inspecting dinki zanyi"
Mantawa tayi da shiru shirun ta kwace hannunta da sauri tare da zare idanu, baki na rawa tace "me...me ne?"
Kin kallonta yayi har yanzu saboda ya san sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba "Inspection nace ko ban isa ba?"
Da rawar murya tace "ka isa amma ni ban taba jin anyi bane"
"To ke me kika sani game da aure dama. Kafin amarya ta tare ango yake yi domin tabbatar da cewa tana da tsafta."
Katse shi tayi da sauri "Hammana wallahi ina wanka kullum kuma ba ma sau daya ba"
"Dan kin fada da baki shikenan ni kuma sai na yarda?"
Gabanta ke matsanancin faduwa ta kwantar da murya tace "Kasan dai bazan yi maka karya ba...ka tambaya kaji"
Murmushi ya juya yayi mata sannan ya gyara muryarsa domin ta saki jiki yana dariyar yadda ta tsorata "na yarda dake Schatzi, kuma nima gaskiya da aka fada sai da naji kunya nace bazan iya ba...."
Wani irin numfashi yaji ta sauke saboda samun relief ta gyara zama harda kwantar da kanta akan seat. Murnar da ta fara bata yi dogon zango ba taji yace "..to amma kwanakin nan duk kin chanja I really miss my Alheran."
Wani abu taji har zuciyarta yana bin dukkan jikinta soyayyarsa tana karuwa a cikin ranta.
Idanu ta lumshe lokacin da ya dan kalleta yana yin kwanar gidansu Arifah domin a nan zasu dauki hotunan. Akan Radhiya ya gaskata soyayya ya kuma san dadin kasancewa da masoyi. Rabuwarsu ta shekaru ukun nan kuwa shine lokaci mafi radadi a zuciyarsa. Dawo dashi tayi daga duniyar da yake neman tafiya ya barta ta hanyar cewa "Chèri nice fa har yanzu"
Sun shiga gidan har yayi parking amma bai bude musu su fita ba ya zuba mata idanunsa "Gaskiya a'a shiyasa dole zanyi inspecting dinki na tabbarar ke din ce da gaske"
Baki ta shiga turawa kamar karamar yarinyar ya kasa hakuri sai da ya saka yatsansa yana shafar dimple dinta a sanyaye yake cewa "tawa Alheran din bata ganina ta kasa magana...I miss wannan 'yar kauyen me yawan kuka da dariya akan Hammanta, Schatzi dina da muke ci daga plate daya da spoon daya, muke shan abu mu ragewa juna. I miss 'Yar soja saboda ni ita ce wadda na kamu da sonta lokacin da na fara hada ido da ita. Idan zaki dawo min da ita yanzu I promise you babu wani inspection da zanyi....atleast for now" ya kare da kashe mata ido.
Kalamansa sun tsaya mata a rai taji kamar su dawwama a cikin wannan yanayin. Kallon da yake mata mai kashe jiki ne ta gaji dashi saboda yadda ta rasa sukuni gabadaya ta hura masa iskar bakinta daf da idonsa ya kifta idon tayi baya da sauri tana masa dariya.
"Gaskiya ta kare maka sosai Hammana"
"Na sani Alheran, daga ranar da na ganki da wannan kwal....."
**********
A Abuja azahar ta riskesu saboda sammakon da suka yi. Dan kwana biyun da babu Mairama Daada yaji jiki saboda har yau gani yake ko daya bisa dari na fanshe rashin matarsa baiyi ba. Yana falonsa na kasa suka iso Radhiya ta makalkale shi yana dariya. Ita kuma ta lura hakan na masa dadi sai yaji kamar bai rasa komai ba na rayuwar 'ya'yansa shiyasa take yi. Rahima na gefe tana murmushi ta gaisheshi ya sakar mata fuska fiye da yadda yake yi kwanakin baya da ta zo.
"Auta bakya laifi wannan daurin har ido na meye?"
Ummi ce tayi masa bayani Radhiya ta kwance ya ga idon ransa kuwa ya baci kamar ya ga Salame a gabansa ya saita mata fuska. Da kansa ya kira Emzee da ya bar gidan tun safe kuma saboda zuwan Rahiman ne yace yazo bayan la'asar ya kaisu asibiti. Bai ma san waye za'a kai ba amma dolensa ya amsa umarnin mahaifinsa.
Karfe hudu da rabi ya iso Ummi ta sauko sanye da riga da zani da hijab ta tura mai aiki kiran Rahima. Tamke fuska yayi bayan sun gaisa tunda yaji sunanta. Doguwar rigar atampa ce a jikinta ta dora rigar sanyi mai zip ta gaba mai dan fadi tare da hijabi fashion wanda ya zarta kafadunta da kadan. Idonta kuwa hankici tasa ta dafe shi bata son haske na ratsa shi.
"Ina wuni" tace da ta iso kusa da shi da Ummi.
Waya ya shiga dannawa baji ba gani yana a'uziyya a zuci wai kada a sake makalo shi da wani nau'in siddabarun a cikin muryarta da take masa dadi har yau.
"Baka ji ana gaisheka ne?" Ummi tace tana nufar kofa za ta fita.
Sai da ya harari Rahima mamaki ya sake kamata sannan yace "na amsa Ummi baki ji bane"
"Wai haka Rahima?"
"Ummi ya amsa" tace tana murmushi.
Emzee na ganin Ummi tayi waje ya dawo kusa da Rahima kamar gaske ya kuma daure fuska "babu kunya kike yi mata karya, ni nace ki rufa min asiri ne?"
Jikinta ne ya soma rawa saura kadan ta fashe da kuka tace kasa yayi hakuri kawai ta wuce. Da ta karasa bakin motar ma baya ya bude duka bangare biyun yana cewa wai su shiga baya tare zasu fi jindadi. Ummi bata ce komai ba tayi zamanta yaji dadin hakan saboda don bai san karyar da zaiyi mata ba idan ta tambayeshi.
Asibitin Samu Wadata su ka je inda suna zaune Ummi ta saka shi ya bada numbar katinsu aka dauko sannan suka yi zaman jiran a kira su. Basu jima ba kuwa aka kira Rahima da Ummi suka shiga wurin likitan. Bayan ya duba idon sosai yace musu wasu jijiyoyi ne suka toshe sakamakon jinin da ya daskare a ciki shi ya kawo kumburin idon. Magani ya rubuta mata na sha da digawa domin sace kumburin sannan zasu dawo bayan kwana biyar a auna lafiyar idon.
**********
Kwana biyun bayan dawowarsu an cigaba da gyara Radhiya sosai. Mama ce da aikin hadata da kayayakinsu na Sakkwatawa da kuma na wata kawarta Maman Farida. Sai kuma takunkuminta na hana Awwab ganin amarya. Tun ranar da su ka dawo daga Sumaila ta fada masa da kanta. Manufarta bai wuce samun lokaci da kyau a gyare mata 'ya ba. Sannan kuma tasan cewa idan ba haka tayi musu ba haka zaiyi ta zuwa kullum yana bata show tunda yasan matarsa ce. Idan kuwa sai da komai ya kammala ne dole ya fi ganin tasirin aikin.
Ba wani damuwa yayi sosai ba saboda shima bashi da isasshen lokaci. Tun safe suke kulle gidan Mami idan ta fita shi da Bilal, Yousuf, Raji, Emzee da Ibrahim sai wani mutum guda daya da yake zuwa sai dare ya tafi. Mama tayi juyin duniya Mami ta fada mata me suke yi taki su ma kuma kowa ya rufe bakinsa. Yau da yake neman alfarmar son ganin Radhiya lallabowa yayi yana mata magiya. Wasa yake yiwa DK da yake hannunsa yana mata magana.
"Ko awa biyu bana jin zamuyi don muma abinda yake gabanmu akwai cin lokaci"
"Na yarda amma da sharadin sai ka fada min me kuke yi kai da 'yan uwanka"
Dariya yayi don kowa yasan tana binsu daidai suna zillewa ne.
"Big surprise ne Mamanmu ni dai a taimaka kada zuciyar......"
Da sauri tace "Ahhhh dena kiran zuciya yanzu zan kira na sanar da ita."
"Allah Ya ja da ran Mama. Nagode" yace tare da ajiye DK a cikin wani abun kwanciyar yara yana murmushi.
Bayan fitarsa ta kira Ummi ta fada mata gobe zai zo daukar Radhiya zasu je yin hotuna wanda za'ayi amfani dasu a wurin dinner din. A wurin Ummi Radhiya taji zancen ta kama yi masa mitar bai fada da wuri ba yanzu wane kaya zata saka yace ita kadai yake bukata goben komai is ready.
"Hammana da ya ka shirya komai ban sani ba?" Tace cikin jindadi.
Murmushi yayi mai sauti "ke dai ki shirya around 12 zan zo. Love you...sai munyi waya anjima ana jirana"
Saroro tayi da wayar a hannu tana tunanin me yake dauke masa hankali ne yanzu bashi da lokacin hirar kirki. Da dare kuma ba wani jimawa suke ba yake kwanciya. Washegari kafin ya iso ta gama shiri tun daren jiya sunyi magana da Arifah itama Yousuf ya fada mata zasu je kuma kada ta tanadi kayan sakawa. Zahra ce ta yi mata light make up mai kyau fuskarta kamar ka dauke ka dasa ga wani irin kamshi mai rikita kwakwalwa da sanyaya ruhi. A kitchen ta yiwa Ummi sallama saboda yace bazai shigo ba sai sun dawo gudun bata lokaci.
Awwab kasa dauke ido yayi daga kanta tun fitowarta har ta iso gaban motar inda yake tsaye rike da kofa ya bude mata. Murmushi tayi tana sunkuyar da kai haka kawai wani irin nauyinsa take ji. Tana shirin zama ya duko daidai kunnenta "you look sweet"
Fadada murmushin tayi ta rufe fuska da tafukan hannayenta. Sai da ya zauna ta soma gaishe shi idanunsa a kanta kamar zai cinyeta.
"Hammana ina wuni?" Tace da karamar murya tana jin faduwar gaba.
"Lafiya kalau my baby."
Yanzu ma murmushi kawai tayi kamar ba ita ba wani salihanci ne yayi mata dabaibayi yayin da kwanakin barin iyayenta da zama cikakkiyar matar Awwab suke gabatowa. Tayar da motar yayi ya kama hannunta ya rike yana magana a hankali amma idanunsa na kan titi.
Cikin muryarsa mai tafiya da zukata wadda har yau idan Radhiya taji sai ta sanyata cikin wani irin yanayi na tsanananin son mai muryar yace "kinsan wani abu?" Kai ta girgiza ya cigaba da magana "yau inspecting dinki zanyi"
Mantawa tayi da shiru shirun ta kwace hannunta da sauri tare da zare idanu, baki na rawa tace "me...me ne?"
Kin kallonta yayi har yanzu saboda ya san sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba "Inspection nace ko ban isa ba?"
Da rawar murya tace "ka isa amma ni ban taba jin anyi bane"
"To ke me kika sani game da aure dama. Kafin amarya ta tare ango yake yi domin tabbatar da cewa tana da tsafta."
Katse shi tayi da sauri "Hammana wallahi ina wanka kullum kuma ba ma sau daya ba"
"Dan kin fada da baki shikenan ni kuma sai na yarda?"
Gabanta ke matsanancin faduwa ta kwantar da murya tace "Kasan dai bazan yi maka karya ba...ka tambaya kaji"
Murmushi ya juya yayi mata sannan ya gyara muryarsa domin ta saki jiki yana dariyar yadda ta tsorata "na yarda dake Schatzi, kuma nima gaskiya da aka fada sai da naji kunya nace bazan iya ba...."
Wani irin numfashi yaji ta sauke saboda samun relief ta gyara zama harda kwantar da kanta akan seat. Murnar da ta fara bata yi dogon zango ba taji yace "..to amma kwanakin nan duk kin chanja I really miss my Alheran."
Wani abu taji har zuciyarta yana bin dukkan jikinta soyayyarsa tana karuwa a cikin ranta.
Idanu ta lumshe lokacin da ya dan kalleta yana yin kwanar gidansu Arifah domin a nan zasu dauki hotunan. Akan Radhiya ya gaskata soyayya ya kuma san dadin kasancewa da masoyi. Rabuwarsu ta shekaru ukun nan kuwa shine lokaci mafi radadi a zuciyarsa. Dawo dashi tayi daga duniyar da yake neman tafiya ya barta ta hanyar cewa "Chèri nice fa har yanzu"
Sun shiga gidan har yayi parking amma bai bude musu su fita ba ya zuba mata idanunsa "Gaskiya a'a shiyasa dole zanyi inspecting dinki na tabbarar ke din ce da gaske"
Baki ta shiga turawa kamar karamar yarinyar ya kasa hakuri sai da ya saka yatsansa yana shafar dimple dinta a sanyaye yake cewa "tawa Alheran din bata ganina ta kasa magana...I miss wannan 'yar kauyen me yawan kuka da dariya akan Hammanta, Schatzi dina da muke ci daga plate daya da spoon daya, muke shan abu mu ragewa juna. I miss 'Yar soja saboda ni ita ce wadda na kamu da sonta lokacin da na fara hada ido da ita. Idan zaki dawo min da ita yanzu I promise you babu wani inspection da zanyi....atleast for now" ya kare da kashe mata ido.
Kalamansa sun tsaya mata a rai taji kamar su dawwama a cikin wannan yanayin. Kallon da yake mata mai kashe jiki ne ta gaji dashi saboda yadda ta rasa sukuni gabadaya ta hura masa iskar bakinta daf da idonsa ya kifta idon tayi baya da sauri tana masa dariya.
"Gaskiya ta kare maka sosai Hammana"
"Na sani Alheran, daga ranar da na ganki da wannan kwal....."