Sashe 6
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su na tsaye ya barsu da kokonta sai gashi ya dawo da fara’arsa har babbar riga ya doro akan kayan jikinsa.
Tabarma aka shimfida musu a zure shi kuma yana daga kan wata kujerar karfe ya baza riga don ya cika ido. Gaishe shi suka sake yi Hadir yayi masa bayanin komai game da zuwansu da bukatar idan ‘yan matan sun amince ayi komai da wuri musamman saboda su basa samun damar fitowa daga barikin suyi dogowar tafiya batare da dalili ba. Yawonsu baya wuce cikin gari kada a nemesu sunyi nisa.
“Ku kwantar da hankalinku Kano dai ba bakuwata bace sannan a can birnin Shehun ma akwai wanda na sani don na taba zuwa garin. Kunsan wani mai kilishi a hanyar Dange shuni? Yana nan wani dan firit haka yace min asalinsa ma mutumin Zaria ne. Kila zai iya tuna ni don naji dadin kilishinsa na sayi da yawa lokacin…”
Duk sun dauka wata alaka zai ce tsakaninsu ko karin bayani sai suka ji zancen yakare, Zayyan sarkin dariya tunda yace mai kilishi dan firit ya daga kai ya kalli Malamijo sai kawai ya kunshe dariyarsa kada ya jawowa kansa. Sun ji dadi ya ce ya basu yaran sai su fara shiri. Tashi yayi yace su jira zai turo su ko gaisawa suyi tunda su Zayyan a ranar zasu koma Sakkwato.
Kusan a shirye Mairama take kira kawai take jira yayin da Salame ta nade akan katifa wai zazzabi ke damunta. Mairama tayi mata sannu ta bi bayan kanwarta da ta sanar da ita Malamijo yace taje wurin bakin.
Sai da tazo bakin kofar da zata sa da ta da zauren da suke, kunya ta hanata shiga. Da Hadir ya hangota, ya fara zolayarta cewa ko sune bata son gani bari su basu wuri. Kai a kasa ta rufe fuska ta shiga ta gaishesu. Salisu yana cigiyar gimbiya Salame ta sanar masa bata da lafiya. Yanayin fuskarsa ya nuna baiji dadi ba.
“Ki dai taimaka min naga alama so take ta saka min ciwon zuciya”
Zayyan da Hadir ne suke kwantar masa da hankali har suka fita don a bar Zayyan suyi magana da Mairama.
“Mairam tafiya ba sallama ko?”
Kanta a kasa ta amsa “kayi hakuri”
“Nayi tunda zuwan nawa ya haifar da da mai ido gashi an bani ke”
Wata matsananciyar kunya ce ta shigeta ta sake dukar da kai. Shima yasan a hanya suke shiyasa bai ja ta sosai ba yace zaiyi kokarin dawowa kafin magabantansa su zo. Yau a hanya suke suna sauri. Wata leda ya mika mata, yayi yayi, taki karba sai ya tashi ya barta a wurin. Iyakarta bakin kofa tayi musu sallama da kyakkyawar addu’ar tafiya.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: E
*TUN RAN GINI…*
Tana shiga daki ta sami Salame a tsaye sai safa da marwa take saboda zulumi. Yanzu shikenan abinda take so sai ta hakura dashi saboda Mairama. Gaskiya bazata iya ba domin son da take masa ba kadan bane. Kuma ma dai ai ita ce ya kamata yaso tunda danginta ne, Mairama kara kawai akayi mata. Ta nisa a cikin tunani taji Mairama tana mata magana.
“Adda jikin ne dai? Ko na sanar da Yadikko a fadawa Malamijo?”
Hade rai tayi ta koma ta zauna akan tabarma “ke yanzu banda rashin kamun kai me ya kaiki dadewa wurin saurayi daga zuwansa na farko? Mutumin da ba wani saninsa ki ka yi ba don iya zubar da aji.”
Kwarai Mairama tayi mamakin kalaman Salame don a iya sani da kuma shaidar da za’ayi mata a gidan tafi kowa saukin kai da dadin mu’amala. To amma meye ya kawo wannan zantuka haka? Kasa daurewa Mairama tayi ta koma bakin katifarsu ta zauna ita ma.
“Adda Salame wai me nayi miki ne haka don Allah? Kwana biyu kenan sai kiyi ta harara ta kina fada min maganganu”
“Ji rainin wayo ki min kwace kizo kina min dadin baki” tace a ranta amma a zahiri sai ta daure tayi mumushi “gani nayi daga yin saurayi kin haukace a kansa ko tunanin idan kin bar gidan nan da wa zan zauna ba kya yi?”
Jikinta sai yayi sanyi ta sake matsowa kusa da Salamen “kai Adda me ya kaiki wannan tunanin? Shine kike ta fushi…ohh ni wallahi duk kin tayar min da hankali na damu. Kema ga Salisu ba sai mu bar gidan tare ba.”
Turo baki Salame tayi “dena min zancensa wallahi baiyi min ba, ke dai kinyi sa’ar Zayyan kawai kina murna”
Rarrashinta Mairama ta soma yi a zatonta da gaske tunanin rabuwarsu a gaba ke damunta. Sauran kannensu mata babu sa’anninsu, maza biyar ne su ke binsu. Koda Salisu ta shiga yi tare da bata sakon gaisuwarsa ta yi tsaki da gaske dai bata son zancensa.
“To na bar zancen nasa Allah Ya kawo wanda ya fishi alkhairi. Shima yace na gaisheki da jiki kuwa”
“Shi wa?” Salame ta fada cikin gatsali wanda Mairama duk ta sawa ranta duk a cikin rashin son su rabu ne.
Tambayar kunya ta bata ta soma inda-inda ba ta san da me za ta kira shi ba. Sunansa dai da wahala ta iya fada a yadda take matukar jin nauyinsa.
Zungurinta Salame tayi da kafa tana mata wani irin kallo mai tattare da kishin da ake kokarin sakayawa.
“Zayyan kike nufi?”
Kai ta gyada ga mamakinta sai ta ga fuskar Salame ta washe sosai tana murmushi “ashe bai manta ni ba. Me yace? Ina nufin da yaya ya baki sakon? Ki gaishe da Salame yace ko me?”
Dadi taji ganin sauyi a tare da yayarta ta kuwa biye mata tana fada mata yadda yace da zai bada sakon gaisuwar. Har dare ranar Salame motsi kadan sai ta tuna wai Zayyan yace a gaisheta, sai taji wani dadi yana ratsata.
**********
Matafiya sun sauka a cikin garin Sakkwato lafiya. Ba wata gajiya su ka yi ba don sun dade da fara sabawa da wahala suna jure mata sosai. Gidansu Zayyan su ka wuce zai dauki kayansa da ya bari sai su koma barrack dinsu.
Gidan yanzu dama daga Jume sai Maikudi, Rayyan da Badaru wadanda sune Zayyan yake bi dukkansu babu mai aure. Matan kuwa Fiddausi, Mubaraka da Hafsatu duk suna dakunansu. Kwasar tuwo Jume take yi Badaru yana zaune akan turmi da ya kifa sai Maikudi kwance a kofar daki yana faman firfita su ka ji sallamar Zayyan din.
Babu wanda ya amsa masa cikinsu sai harara da suke binsa da ita. Dakinsa ya wuce kai tsaye ya dauko jakar kayansa a ransa yana bakincikin halayyar ‘yan uwan nasa. Ba haka ya bar jakar ba alamu sun nuna an bude an yamutsa masa kaya wurin neman abin da yake zaton kudi ne, sai dai ko kwandala bai bari a ciki ba. Ratayo abarsa ya yi ya fito ya kulle dakin.
“Sai Allah Ya sake dawo damu ni zan wuce” yace daga tsaye yana dan rissinawa Jume.
Maikudi ya tashi zumbur yana kallonsa, ita ma Jume ta juyo da kujerar da take zaune a kai yadda za ta fuskance shi da kyau.
“Zayyanu ni zaka wulakanta a gidan nan? In baka umarni saboda ba uwarka bace sai kasa kafa ka take. Kwana nawa ina sawa a dubo ko gidan Aminun ka makale babu kai babu labari sai yau. Shine har kake da bakin cewa zaka wuce.”
Baya son ya kai ga yi mata abinda zai zo yana nadama nan gaba ga darajarta na matsayin wadda ta rike shi kuma matar babansa, da idan ya fada mata wata maganar ko hanyar da ya bi bazata so ta sake bi ba.
“Jume Kano naje biki ba maganarki naki ji ba”
Maikudi ya dawo kusa dashi ya miko hannu kamar wanda ya bawa ajiya “ina kudin da tace ka karbo a wurin wancan tsohon munafukin?”
“Yanzu aminin Baba kake kira munafuki?”
“Kaga kafin ka fara dogon surutu bani kudin ka wuce bana son rigima da al’murun nan” Jume ta fada tana kara tamke fuska.
Dago idanu yayi ya zube mata a kanta sai gashi jikinta ya yi lakwas. Rayyan da Badaru ma kowa ya sha jinin jikinsa. Maikudi ne kawai hankalinsa bai kai wurin ba.
“Jume!”
“Eyye” ta amsa a dan tosrace.
“Kudi dai gadona ne ni kadai kamar yadda a gabana aka bawa kowa nasa...”
“Kai, rashin kunya za ka yi mata a gabanmu?” inji Maikudi.
“Idan na fahinceka Zayyanu kudin ne ba za ka bani ba saboda ban isa in nemi abu a wurinka in samu ba?”
Tausayi ta bashi yadda ta hakikance akan rashin gaskiyarta bata ko tunani sai son bukatarta ta biya. Hannu ya zura cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dari ‘yan ashirin guda biyar ya mika mata.
“Ga wannan ku kara cefane” yace cike da nutsuwa, bai kuma jira cewarta ba ya fice waje inda Hadir yake jiransa.
Yana fita Maikudi ya warce kudin a hannunta yana jaddada mata tasan yadda zata yi ta karbo musu ragowar idan ba haka ba shine zaiyi ajalin Zayyanu sai ya ga ta inda zaiyi amfani da kudin.
“Banza shashasha to sai ka dawo, kafin kayi ajalin nasa shi zaiyi naka. Har mamaki kake bani yadda kake manta zuciyar Zayyanu da kuma kasancewara soja. Yanzu idan yasa aka kamaka duk duniya bana jin kana da wanda zai fito da kai. Nima kaina tsoronsa nake ji dan jakar uba, daurewa kawai nake ina masa barazana. Amma muje zuwa sai na dawo dashi tafin hannuna. Uwarsa ma mai suna kamar na tsuntsaye bata iya karawa dani ba”
**********
Sati uku da dawowarsu a tsukun lokacin iyayen Hadir sun zo daga Kano an daidaita maganar aurensa da Zainab. Kullum ya dawo ya ishi Zayyan da labarin hirarsu ko maganar biki. Ranar da ya bishi kuwa yadda ya kula suna son juna musamman Zainab da duniya bata ganin kowa da gashi sai Hadir sai yaji muguwar kewar Mairama.
Tabarma aka shimfida musu a zure shi kuma yana daga kan wata kujerar karfe ya baza riga don ya cika ido. Gaishe shi suka sake yi Hadir yayi masa bayanin komai game da zuwansu da bukatar idan ‘yan matan sun amince ayi komai da wuri musamman saboda su basa samun damar fitowa daga barikin suyi dogowar tafiya batare da dalili ba. Yawonsu baya wuce cikin gari kada a nemesu sunyi nisa.
“Ku kwantar da hankalinku Kano dai ba bakuwata bace sannan a can birnin Shehun ma akwai wanda na sani don na taba zuwa garin. Kunsan wani mai kilishi a hanyar Dange shuni? Yana nan wani dan firit haka yace min asalinsa ma mutumin Zaria ne. Kila zai iya tuna ni don naji dadin kilishinsa na sayi da yawa lokacin…”
Duk sun dauka wata alaka zai ce tsakaninsu ko karin bayani sai suka ji zancen yakare, Zayyan sarkin dariya tunda yace mai kilishi dan firit ya daga kai ya kalli Malamijo sai kawai ya kunshe dariyarsa kada ya jawowa kansa. Sun ji dadi ya ce ya basu yaran sai su fara shiri. Tashi yayi yace su jira zai turo su ko gaisawa suyi tunda su Zayyan a ranar zasu koma Sakkwato.
Kusan a shirye Mairama take kira kawai take jira yayin da Salame ta nade akan katifa wai zazzabi ke damunta. Mairama tayi mata sannu ta bi bayan kanwarta da ta sanar da ita Malamijo yace taje wurin bakin.
Sai da tazo bakin kofar da zata sa da ta da zauren da suke, kunya ta hanata shiga. Da Hadir ya hangota, ya fara zolayarta cewa ko sune bata son gani bari su basu wuri. Kai a kasa ta rufe fuska ta shiga ta gaishesu. Salisu yana cigiyar gimbiya Salame ta sanar masa bata da lafiya. Yanayin fuskarsa ya nuna baiji dadi ba.
“Ki dai taimaka min naga alama so take ta saka min ciwon zuciya”
Zayyan da Hadir ne suke kwantar masa da hankali har suka fita don a bar Zayyan suyi magana da Mairama.
“Mairam tafiya ba sallama ko?”
Kanta a kasa ta amsa “kayi hakuri”
“Nayi tunda zuwan nawa ya haifar da da mai ido gashi an bani ke”
Wata matsananciyar kunya ce ta shigeta ta sake dukar da kai. Shima yasan a hanya suke shiyasa bai ja ta sosai ba yace zaiyi kokarin dawowa kafin magabantansa su zo. Yau a hanya suke suna sauri. Wata leda ya mika mata, yayi yayi, taki karba sai ya tashi ya barta a wurin. Iyakarta bakin kofa tayi musu sallama da kyakkyawar addu’ar tafiya.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: E
*TUN RAN GINI…*
Tana shiga daki ta sami Salame a tsaye sai safa da marwa take saboda zulumi. Yanzu shikenan abinda take so sai ta hakura dashi saboda Mairama. Gaskiya bazata iya ba domin son da take masa ba kadan bane. Kuma ma dai ai ita ce ya kamata yaso tunda danginta ne, Mairama kara kawai akayi mata. Ta nisa a cikin tunani taji Mairama tana mata magana.
“Adda jikin ne dai? Ko na sanar da Yadikko a fadawa Malamijo?”
Hade rai tayi ta koma ta zauna akan tabarma “ke yanzu banda rashin kamun kai me ya kaiki dadewa wurin saurayi daga zuwansa na farko? Mutumin da ba wani saninsa ki ka yi ba don iya zubar da aji.”
Kwarai Mairama tayi mamakin kalaman Salame don a iya sani da kuma shaidar da za’ayi mata a gidan tafi kowa saukin kai da dadin mu’amala. To amma meye ya kawo wannan zantuka haka? Kasa daurewa Mairama tayi ta koma bakin katifarsu ta zauna ita ma.
“Adda Salame wai me nayi miki ne haka don Allah? Kwana biyu kenan sai kiyi ta harara ta kina fada min maganganu”
“Ji rainin wayo ki min kwace kizo kina min dadin baki” tace a ranta amma a zahiri sai ta daure tayi mumushi “gani nayi daga yin saurayi kin haukace a kansa ko tunanin idan kin bar gidan nan da wa zan zauna ba kya yi?”
Jikinta sai yayi sanyi ta sake matsowa kusa da Salamen “kai Adda me ya kaiki wannan tunanin? Shine kike ta fushi…ohh ni wallahi duk kin tayar min da hankali na damu. Kema ga Salisu ba sai mu bar gidan tare ba.”
Turo baki Salame tayi “dena min zancensa wallahi baiyi min ba, ke dai kinyi sa’ar Zayyan kawai kina murna”
Rarrashinta Mairama ta soma yi a zatonta da gaske tunanin rabuwarsu a gaba ke damunta. Sauran kannensu mata babu sa’anninsu, maza biyar ne su ke binsu. Koda Salisu ta shiga yi tare da bata sakon gaisuwarsa ta yi tsaki da gaske dai bata son zancensa.
“To na bar zancen nasa Allah Ya kawo wanda ya fishi alkhairi. Shima yace na gaisheki da jiki kuwa”
“Shi wa?” Salame ta fada cikin gatsali wanda Mairama duk ta sawa ranta duk a cikin rashin son su rabu ne.
Tambayar kunya ta bata ta soma inda-inda ba ta san da me za ta kira shi ba. Sunansa dai da wahala ta iya fada a yadda take matukar jin nauyinsa.
Zungurinta Salame tayi da kafa tana mata wani irin kallo mai tattare da kishin da ake kokarin sakayawa.
“Zayyan kike nufi?”
Kai ta gyada ga mamakinta sai ta ga fuskar Salame ta washe sosai tana murmushi “ashe bai manta ni ba. Me yace? Ina nufin da yaya ya baki sakon? Ki gaishe da Salame yace ko me?”
Dadi taji ganin sauyi a tare da yayarta ta kuwa biye mata tana fada mata yadda yace da zai bada sakon gaisuwar. Har dare ranar Salame motsi kadan sai ta tuna wai Zayyan yace a gaisheta, sai taji wani dadi yana ratsata.
**********
Matafiya sun sauka a cikin garin Sakkwato lafiya. Ba wata gajiya su ka yi ba don sun dade da fara sabawa da wahala suna jure mata sosai. Gidansu Zayyan su ka wuce zai dauki kayansa da ya bari sai su koma barrack dinsu.
Gidan yanzu dama daga Jume sai Maikudi, Rayyan da Badaru wadanda sune Zayyan yake bi dukkansu babu mai aure. Matan kuwa Fiddausi, Mubaraka da Hafsatu duk suna dakunansu. Kwasar tuwo Jume take yi Badaru yana zaune akan turmi da ya kifa sai Maikudi kwance a kofar daki yana faman firfita su ka ji sallamar Zayyan din.
Babu wanda ya amsa masa cikinsu sai harara da suke binsa da ita. Dakinsa ya wuce kai tsaye ya dauko jakar kayansa a ransa yana bakincikin halayyar ‘yan uwan nasa. Ba haka ya bar jakar ba alamu sun nuna an bude an yamutsa masa kaya wurin neman abin da yake zaton kudi ne, sai dai ko kwandala bai bari a ciki ba. Ratayo abarsa ya yi ya fito ya kulle dakin.
“Sai Allah Ya sake dawo damu ni zan wuce” yace daga tsaye yana dan rissinawa Jume.
Maikudi ya tashi zumbur yana kallonsa, ita ma Jume ta juyo da kujerar da take zaune a kai yadda za ta fuskance shi da kyau.
“Zayyanu ni zaka wulakanta a gidan nan? In baka umarni saboda ba uwarka bace sai kasa kafa ka take. Kwana nawa ina sawa a dubo ko gidan Aminun ka makale babu kai babu labari sai yau. Shine har kake da bakin cewa zaka wuce.”
Baya son ya kai ga yi mata abinda zai zo yana nadama nan gaba ga darajarta na matsayin wadda ta rike shi kuma matar babansa, da idan ya fada mata wata maganar ko hanyar da ya bi bazata so ta sake bi ba.
“Jume Kano naje biki ba maganarki naki ji ba”
Maikudi ya dawo kusa dashi ya miko hannu kamar wanda ya bawa ajiya “ina kudin da tace ka karbo a wurin wancan tsohon munafukin?”
“Yanzu aminin Baba kake kira munafuki?”
“Kaga kafin ka fara dogon surutu bani kudin ka wuce bana son rigima da al’murun nan” Jume ta fada tana kara tamke fuska.
Dago idanu yayi ya zube mata a kanta sai gashi jikinta ya yi lakwas. Rayyan da Badaru ma kowa ya sha jinin jikinsa. Maikudi ne kawai hankalinsa bai kai wurin ba.
“Jume!”
“Eyye” ta amsa a dan tosrace.
“Kudi dai gadona ne ni kadai kamar yadda a gabana aka bawa kowa nasa...”
“Kai, rashin kunya za ka yi mata a gabanmu?” inji Maikudi.
“Idan na fahinceka Zayyanu kudin ne ba za ka bani ba saboda ban isa in nemi abu a wurinka in samu ba?”
Tausayi ta bashi yadda ta hakikance akan rashin gaskiyarta bata ko tunani sai son bukatarta ta biya. Hannu ya zura cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dari ‘yan ashirin guda biyar ya mika mata.
“Ga wannan ku kara cefane” yace cike da nutsuwa, bai kuma jira cewarta ba ya fice waje inda Hadir yake jiransa.
Yana fita Maikudi ya warce kudin a hannunta yana jaddada mata tasan yadda zata yi ta karbo musu ragowar idan ba haka ba shine zaiyi ajalin Zayyanu sai ya ga ta inda zaiyi amfani da kudin.
“Banza shashasha to sai ka dawo, kafin kayi ajalin nasa shi zaiyi naka. Har mamaki kake bani yadda kake manta zuciyar Zayyanu da kuma kasancewara soja. Yanzu idan yasa aka kamaka duk duniya bana jin kana da wanda zai fito da kai. Nima kaina tsoronsa nake ji dan jakar uba, daurewa kawai nake ina masa barazana. Amma muje zuwa sai na dawo dashi tafin hannuna. Uwarsa ma mai suna kamar na tsuntsaye bata iya karawa dani ba”
**********
Sati uku da dawowarsu a tsukun lokacin iyayen Hadir sun zo daga Kano an daidaita maganar aurensa da Zainab. Kullum ya dawo ya ishi Zayyan da labarin hirarsu ko maganar biki. Ranar da ya bishi kuwa yadda ya kula suna son juna musamman Zainab da duniya bata ganin kowa da gashi sai Hadir sai yaji muguwar kewar Mairama.