Sashe 118
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Thank you Nigeria you have given me 22years worth of love in a single night. Long live Nigeria, God bless my country"
Wani hawayen Mairaman Zayyan ta fitar batare da ta sani ba. A nan tsaye aka barshi shugaban kasa ya taso zai bashi award. Hularsa ya cire ya mika masa hannu sai da Mr President ya bawa kowa mamaki domin bai karbi hannun ba sai rungumar Zayyan da yayi sannan ya karbi award din daga hannun Chief of Army Staff ya mika masa.
Rahima babu inda take kallo sai Emzee da yake tsaye har lokacin a kame babu gajiyawa taji wata irin azababbiyar soyayyarsa tayi mata kamun in ba kai babu rayuwa. It was a moment da bazata taba mantawa ba a rayuwarta har abada.
Bayan Zayyan ya zauna ne su Emzee sun koma mazauninsu Chief of army staff din da kansa ya gabatar da shirin Military Voice yace suna alfahari da wannan yunkuri na sanar da duniya sadaukarwar da sojoji da iyalansu suke yi. Sannan gashi sun sake ganin inda yake bukatar a duba domin tallafi ga wadanda suke cikin mawuyacin hali.
Sake yin duhu wurin yayi sai ga Radhiya tana gabatar da shirin sannan aka nuna bangarori daban daban a ciki wanda ya janyo zubar hawayen mutane da dama a wurin. Iyayenta da mijinta were so proud haka ma 'yan uwa.
MC KDM sai cewa yayi Radhiya ta fito tace wani abu game da shirin nan nata. Dif tayi kamar ruwa ya cinyeta ta kasa motsi.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: A bangaren Yousuf da Arifah kwatancen hanya ta rinka yi masa a kunyace har su ka iso titin da zai sada su da gidan inda daga nan ya gane hanya. Ciki ya shiga tunda masu gadin sun gane motarta kuma tana ciki. Duk ta daburce saboda auren nasu yazo da wuri basu gama sabo sosai dashi ba. Ya san da hakan shima shiyasa yake kokarin dinki duk wata kofa kafin su fara rayuwar auren sosai.
"A love yanzu yaya zaki yi dani?"
Fasa bude kofar tayi ta waigo kadan "me ya faru?"
"Kin taho dani gashi bansan hanyar komawa ba kuma bani da ko cent a jikina da zan nemi taxi. Ga dare..." yace da wani irin yanayin da zaisa a tausaya masa.
"Kaine fa kace zaka rakoni in karbi motar. Yanzu yaya kake so ayi?"
Kwantar da kansa yayi baya ya jingina da kujerar yana kallonta "Nima ki rakani"
"Yanzu su Mom zasu dawo ace ina naje?"
Bude bangaren shi ta ga zaiyi cikin yanayin ko in kula yace "tunda haka ne muje kawai na kwana a dakinki kinga gobe sai mu shirya daga nan mu tafi zaifi sauki"
Idanu ta zaro tana kada hannu "wasa kake yi amma"
"Gadon naki karami ne? To ba sai ki kwanta a kasa ba ni ki bani gadon tunda nine bako"
Dariya ya bata ma yadda yake maganar tace "rufa min asiri...ko za ka kira Yayana yazo ya daukeka?"
"Ni bazan shiga rayuwar kanwata in hanata samun kulawa daga mijinta ba"
"Hmm Y love rigima kake ji naga alama"
"Ko daya" yace yana kamo hannunta ya rike yana murza yatsun.
"To ka dauki motar ka tafi da ita"
"In bata a hanya gobe ace ba'a ganni ba...naki"
"Bari na nemi dreba ya mayar da kai"
Bata rai yayi "bana so"
"Ya zamuyi to?" Tace tana tura baki don tsoronta daya kada iyayenta su dawo a gansu sai ace bata da kunya musamman Mom dinta. Bata san yaya akayi ba ya janyota rabin jikinta a cinyarsa ya rungumeta sosai yana shakar kamshin jikinta mai dadi. Kansa yana gefen wuyanta sai numfashinsa kawai take ji yace.
"Mhmmm mon amour" yana jin kamar su kwana a haka "...inata baki haske, inata baki haske kinki ganewa."
Yadda hausar tasa ke fita da abinda yace ne ya sakata dariyar dole "kana ta bani haske..."
"Eh mana amma baki gane ba....kowane ango yana tare da matarsa ni tawa tana nuna min halin hausawan Nigeria"
"Ban dau haske bane" tace a hankali tana kokarin zamewa sai gashi tar an hasko wata torchlight mai mugun haske sosai cikin motar ta barin da yake.
Arifah gabadaya ta gigice don kunya ta fasa guduwa sai ma kara kankame shi da tayi a kunyace bata son ko waye a tsaye ya ganta a haka. Yusouf kuwa ko a jikinsa sai ma sauke glass da yayi rabi har lokacin tana cikin jiikinsa. Security din yace da pidgin english "na Madam i dey find I never see her comot from the car"
Ko kalma daya bai fahimta ba sai ma kullewa da kansa yayi yace "pardon?" Sai kuma kawai ya dan taba kafadarta
"Ba fa na jin yaren nan ki kore shi kafin nayi masa ido daya na ganin matata"
Yadda yake bata rai ma abin dariya ne. Haka ta daure ta dago kanta kadan "Oga Sunday I dey come"
"No wahala" mutumin yace tunda ya tabbatar tana nan ya juya abinsa.
Kokarin tashi daga jikinsa ta soma yi "Y love bari na hadaka da driver please"
Sake riketa yayi ta kasa motsawa "ke kuwa ki dau haske mana A love, biyoki nayi fa don mu taya juna murnar aure"
Duk wasu dabarunsa ta gama ganewa. Ko Radhiya kanwarta ai tasan ta wuce ayi mata wannan wayon bare ita. Wace murnar aure zata yi a kofar gida. Hannunta ta mika masa na dama ya riko da nasa ta dan daga hannun sama da kasa tana jinjinawa "congratulations on your...."
"Rike kayarki tunda baki daukar haske ga abinda nake nufi" yace yana kai mata wani irin kiss da ya hanata motsawa.
Dirin motocin da suka ji daga waje ne ya tayar musu da hankali su duka ta tashi daga jikinsa da sauri.
"Yanzu ya zamuyi?"
Tashin hankali karara a fuskarsa yace "nima ban sani ba, ba gidanku bane"
A tsorace take amma dole tayi dariya don ya fita rikicewa. Shiyasa yaso ta dau haske tun dazu ya samu ya gudu saboda Yousuf mutum ne mai kunya sosai. Ko lokacin da yaso Radhiya wannan kunyar ita tayi ta cutarsa ya kasa fada da wuri ashe rabon Arifah Nasiruddeen ne. Saurin kiran Awwab yayi yace yazo ya dauke shi su tafi.
***********
Bayan fitar Radhiya daga falon da sauri ya biyo bayanta amma bai ga alamunta ba. Da gudu ta shiga cikin gidan tana ji kamar za'a gane me tayi. Awwab zai kirata kenan don shi bai ki yau ya kwana a gidan ba Yousuf ya kira.
"Ni gaskiya bazan zo ba rakiyar taka tayi kadan ni kuma yanzu na fara" yace masa yana dariya.
Yousuf ya kalli motocin su Baban Arifa "Kada muyi haka mana Awwab ni da na baka kanwata ya kamata ka kyautata min"
"Ni ba kanwar na baka ba"
Daga murya Yousuf yayi amma kana ji kasan kawai damuwa ce "kada kasa na dage bikin nan sai ta gama ècole"
"Daidai kenan, sai ayi bikin da baby dinmu mu shiga gida mu uku ko hudu" bai san me ya dami Yousuf din ba amma dadin tsokanarsa yake ji yana dariya lokacin da Raji da Bilal suka fito kowa da murmushi saman fuskokinsu.
"A love kiyi masa magana" Yousuf yace da Arifa kamar yayi kuka.
Tana karbar wayar ta soma magiya don tana iya hango kallon da Mom dinta take sakar mata bayan ta fito daga mota. Yousuf sai ji yayi wani gumi na neman saukar masa duk sanyin garin. Tare da Arifah suka matsa wurinsu suna musu barka da dawowa.
"Yousuf ba dai sawa tayi ka kawota ba ka biye mata kai kuma?" Cewar Mom tana musu kallon daidai.
Awwab na jin muryarta da hannu yayiwa su Raji alama suka shige mota yaja suna dariya yau sun sami abin tsokanarsa. Rakiyar yau bata yi ba sai dai ko gobe a sake.
Yousuf yace da Mom "na ga ta karbi motar ne ga dare. Su Awwab nake jira zamu tafi suna hanya"
"To babu damuwa bari na wuce"
Excellency da mutanensa yayi gefe suna magana yana yiwa ango da amarya murmushi yace su shiga ciki kafin Awwab din ya karaso. A ransa kuwa dariyar yadda Mom sarkin takura ta ritsa su yake yi. Tunda anyi aure ba shikenan ba, ko don tayi sa'a ba sai da safe ya dawo mata da 'yarta ba.
A cikin gidan ma kamar yana kan kaya hankalinsa bai kwanta ba saboda hawa da saukar da Mom ta rinka yi sai da Awwab ya kira shi. Da sauri ya fita daga gidan yana sauke ajiyar zuciya.
Kai daren ranar kamar yayi ihu saboda yadda su Awwab suka saka shi a gaba da tsokana. Mami tana jiyo hayaniya daga dakin Awwab inda suke kwana kamar wasu yara.
"Irin haka basarwa ake yi Yousuf" Awwab yace yana mike bayansa akan gado saboda gajiya.
"Zan rama duk kuyi ku gama. Kuma matsa min na kwanta yau nan nake so."
Ture Awwab yayi tsakiya dariya ta hana shi tabuka komai har Yousuf din ya kwanta a wurin mutum biyu don da gangan ya bude hannuwa wai baya son takura.
**********
Fauziyya da Zahra sun riga Radhiya shiga daki. Rahima da Zayyana wani dakin suke kwana a kasa yanzu saboda yayyensu dake saman a dakin Radhiya ga yara biyu.
Yadda take sauke numfashi Zahra ta tambayeta ko gudu tayi ta gyada kai.
"To dai mutum ya girma guje guje ba naki bane amaryarmu" Zahran tace mata.
"Kyaleta fa tayi abinta nan da sati biyu ko da kudi nasan da wuya ta iya daga kafa"
"Me zaisa Adda Fauzi?" Radhiya tace da iyaka gaskiyarta.
Zahra tace "Kyale wannan yayar taki kin santa sarai da tsokana"
Tawul ta dauko za ta cire kayanta ta shiga wanka Fauziyya ta fara yi mata kallon mara gaskiya saboda a takure take wanda ba halin ta bane.
"Amaryar Hamma kada kice min janbakin nan ya goge...gaskiya ina jin ba mai kyan kika saya ba. Ni fa shiyasa abu designer bai dameni ba, ance baya fita da wuri sai an goge shi amma ke lips dinki kamar baki shafa komai ba. Kalli ki gani" ta juya tana nunawa Zahra da tsokana.
Wani hawayen Mairaman Zayyan ta fitar batare da ta sani ba. A nan tsaye aka barshi shugaban kasa ya taso zai bashi award. Hularsa ya cire ya mika masa hannu sai da Mr President ya bawa kowa mamaki domin bai karbi hannun ba sai rungumar Zayyan da yayi sannan ya karbi award din daga hannun Chief of Army Staff ya mika masa.
Rahima babu inda take kallo sai Emzee da yake tsaye har lokacin a kame babu gajiyawa taji wata irin azababbiyar soyayyarsa tayi mata kamun in ba kai babu rayuwa. It was a moment da bazata taba mantawa ba a rayuwarta har abada.
Bayan Zayyan ya zauna ne su Emzee sun koma mazauninsu Chief of army staff din da kansa ya gabatar da shirin Military Voice yace suna alfahari da wannan yunkuri na sanar da duniya sadaukarwar da sojoji da iyalansu suke yi. Sannan gashi sun sake ganin inda yake bukatar a duba domin tallafi ga wadanda suke cikin mawuyacin hali.
Sake yin duhu wurin yayi sai ga Radhiya tana gabatar da shirin sannan aka nuna bangarori daban daban a ciki wanda ya janyo zubar hawayen mutane da dama a wurin. Iyayenta da mijinta were so proud haka ma 'yan uwa.
MC KDM sai cewa yayi Radhiya ta fito tace wani abu game da shirin nan nata. Dif tayi kamar ruwa ya cinyeta ta kasa motsi.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: A bangaren Yousuf da Arifah kwatancen hanya ta rinka yi masa a kunyace har su ka iso titin da zai sada su da gidan inda daga nan ya gane hanya. Ciki ya shiga tunda masu gadin sun gane motarta kuma tana ciki. Duk ta daburce saboda auren nasu yazo da wuri basu gama sabo sosai dashi ba. Ya san da hakan shima shiyasa yake kokarin dinki duk wata kofa kafin su fara rayuwar auren sosai.
"A love yanzu yaya zaki yi dani?"
Fasa bude kofar tayi ta waigo kadan "me ya faru?"
"Kin taho dani gashi bansan hanyar komawa ba kuma bani da ko cent a jikina da zan nemi taxi. Ga dare..." yace da wani irin yanayin da zaisa a tausaya masa.
"Kaine fa kace zaka rakoni in karbi motar. Yanzu yaya kake so ayi?"
Kwantar da kansa yayi baya ya jingina da kujerar yana kallonta "Nima ki rakani"
"Yanzu su Mom zasu dawo ace ina naje?"
Bude bangaren shi ta ga zaiyi cikin yanayin ko in kula yace "tunda haka ne muje kawai na kwana a dakinki kinga gobe sai mu shirya daga nan mu tafi zaifi sauki"
Idanu ta zaro tana kada hannu "wasa kake yi amma"
"Gadon naki karami ne? To ba sai ki kwanta a kasa ba ni ki bani gadon tunda nine bako"
Dariya ya bata ma yadda yake maganar tace "rufa min asiri...ko za ka kira Yayana yazo ya daukeka?"
"Ni bazan shiga rayuwar kanwata in hanata samun kulawa daga mijinta ba"
"Hmm Y love rigima kake ji naga alama"
"Ko daya" yace yana kamo hannunta ya rike yana murza yatsun.
"To ka dauki motar ka tafi da ita"
"In bata a hanya gobe ace ba'a ganni ba...naki"
"Bari na nemi dreba ya mayar da kai"
Bata rai yayi "bana so"
"Ya zamuyi to?" Tace tana tura baki don tsoronta daya kada iyayenta su dawo a gansu sai ace bata da kunya musamman Mom dinta. Bata san yaya akayi ba ya janyota rabin jikinta a cinyarsa ya rungumeta sosai yana shakar kamshin jikinta mai dadi. Kansa yana gefen wuyanta sai numfashinsa kawai take ji yace.
"Mhmmm mon amour" yana jin kamar su kwana a haka "...inata baki haske, inata baki haske kinki ganewa."
Yadda hausar tasa ke fita da abinda yace ne ya sakata dariyar dole "kana ta bani haske..."
"Eh mana amma baki gane ba....kowane ango yana tare da matarsa ni tawa tana nuna min halin hausawan Nigeria"
"Ban dau haske bane" tace a hankali tana kokarin zamewa sai gashi tar an hasko wata torchlight mai mugun haske sosai cikin motar ta barin da yake.
Arifah gabadaya ta gigice don kunya ta fasa guduwa sai ma kara kankame shi da tayi a kunyace bata son ko waye a tsaye ya ganta a haka. Yusouf kuwa ko a jikinsa sai ma sauke glass da yayi rabi har lokacin tana cikin jiikinsa. Security din yace da pidgin english "na Madam i dey find I never see her comot from the car"
Ko kalma daya bai fahimta ba sai ma kullewa da kansa yayi yace "pardon?" Sai kuma kawai ya dan taba kafadarta
"Ba fa na jin yaren nan ki kore shi kafin nayi masa ido daya na ganin matata"
Yadda yake bata rai ma abin dariya ne. Haka ta daure ta dago kanta kadan "Oga Sunday I dey come"
"No wahala" mutumin yace tunda ya tabbatar tana nan ya juya abinsa.
Kokarin tashi daga jikinsa ta soma yi "Y love bari na hadaka da driver please"
Sake riketa yayi ta kasa motsawa "ke kuwa ki dau haske mana A love, biyoki nayi fa don mu taya juna murnar aure"
Duk wasu dabarunsa ta gama ganewa. Ko Radhiya kanwarta ai tasan ta wuce ayi mata wannan wayon bare ita. Wace murnar aure zata yi a kofar gida. Hannunta ta mika masa na dama ya riko da nasa ta dan daga hannun sama da kasa tana jinjinawa "congratulations on your...."
"Rike kayarki tunda baki daukar haske ga abinda nake nufi" yace yana kai mata wani irin kiss da ya hanata motsawa.
Dirin motocin da suka ji daga waje ne ya tayar musu da hankali su duka ta tashi daga jikinsa da sauri.
"Yanzu ya zamuyi?"
Tashin hankali karara a fuskarsa yace "nima ban sani ba, ba gidanku bane"
A tsorace take amma dole tayi dariya don ya fita rikicewa. Shiyasa yaso ta dau haske tun dazu ya samu ya gudu saboda Yousuf mutum ne mai kunya sosai. Ko lokacin da yaso Radhiya wannan kunyar ita tayi ta cutarsa ya kasa fada da wuri ashe rabon Arifah Nasiruddeen ne. Saurin kiran Awwab yayi yace yazo ya dauke shi su tafi.
***********
Bayan fitar Radhiya daga falon da sauri ya biyo bayanta amma bai ga alamunta ba. Da gudu ta shiga cikin gidan tana ji kamar za'a gane me tayi. Awwab zai kirata kenan don shi bai ki yau ya kwana a gidan ba Yousuf ya kira.
"Ni gaskiya bazan zo ba rakiyar taka tayi kadan ni kuma yanzu na fara" yace masa yana dariya.
Yousuf ya kalli motocin su Baban Arifa "Kada muyi haka mana Awwab ni da na baka kanwata ya kamata ka kyautata min"
"Ni ba kanwar na baka ba"
Daga murya Yousuf yayi amma kana ji kasan kawai damuwa ce "kada kasa na dage bikin nan sai ta gama ècole"
"Daidai kenan, sai ayi bikin da baby dinmu mu shiga gida mu uku ko hudu" bai san me ya dami Yousuf din ba amma dadin tsokanarsa yake ji yana dariya lokacin da Raji da Bilal suka fito kowa da murmushi saman fuskokinsu.
"A love kiyi masa magana" Yousuf yace da Arifa kamar yayi kuka.
Tana karbar wayar ta soma magiya don tana iya hango kallon da Mom dinta take sakar mata bayan ta fito daga mota. Yousuf sai ji yayi wani gumi na neman saukar masa duk sanyin garin. Tare da Arifah suka matsa wurinsu suna musu barka da dawowa.
"Yousuf ba dai sawa tayi ka kawota ba ka biye mata kai kuma?" Cewar Mom tana musu kallon daidai.
Awwab na jin muryarta da hannu yayiwa su Raji alama suka shige mota yaja suna dariya yau sun sami abin tsokanarsa. Rakiyar yau bata yi ba sai dai ko gobe a sake.
Yousuf yace da Mom "na ga ta karbi motar ne ga dare. Su Awwab nake jira zamu tafi suna hanya"
"To babu damuwa bari na wuce"
Excellency da mutanensa yayi gefe suna magana yana yiwa ango da amarya murmushi yace su shiga ciki kafin Awwab din ya karaso. A ransa kuwa dariyar yadda Mom sarkin takura ta ritsa su yake yi. Tunda anyi aure ba shikenan ba, ko don tayi sa'a ba sai da safe ya dawo mata da 'yarta ba.
A cikin gidan ma kamar yana kan kaya hankalinsa bai kwanta ba saboda hawa da saukar da Mom ta rinka yi sai da Awwab ya kira shi. Da sauri ya fita daga gidan yana sauke ajiyar zuciya.
Kai daren ranar kamar yayi ihu saboda yadda su Awwab suka saka shi a gaba da tsokana. Mami tana jiyo hayaniya daga dakin Awwab inda suke kwana kamar wasu yara.
"Irin haka basarwa ake yi Yousuf" Awwab yace yana mike bayansa akan gado saboda gajiya.
"Zan rama duk kuyi ku gama. Kuma matsa min na kwanta yau nan nake so."
Ture Awwab yayi tsakiya dariya ta hana shi tabuka komai har Yousuf din ya kwanta a wurin mutum biyu don da gangan ya bude hannuwa wai baya son takura.
**********
Fauziyya da Zahra sun riga Radhiya shiga daki. Rahima da Zayyana wani dakin suke kwana a kasa yanzu saboda yayyensu dake saman a dakin Radhiya ga yara biyu.
Yadda take sauke numfashi Zahra ta tambayeta ko gudu tayi ta gyada kai.
"To dai mutum ya girma guje guje ba naki bane amaryarmu" Zahran tace mata.
"Kyaleta fa tayi abinta nan da sati biyu ko da kudi nasan da wuya ta iya daga kafa"
"Me zaisa Adda Fauzi?" Radhiya tace da iyaka gaskiyarta.
Zahra tace "Kyale wannan yayar taki kin santa sarai da tsokana"
Tawul ta dauko za ta cire kayanta ta shiga wanka Fauziyya ta fara yi mata kallon mara gaskiya saboda a takure take wanda ba halin ta bane.
"Amaryar Hamma kada kice min janbakin nan ya goge...gaskiya ina jin ba mai kyan kika saya ba. Ni fa shiyasa abu designer bai dameni ba, ance baya fita da wuri sai an goge shi amma ke lips dinki kamar baki shafa komai ba. Kalli ki gani" ta juya tana nunawa Zahra da tsokana.