Sashe 62
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanye yake da wando chinos mai kyau coffee da shirt cream wadda ta dan kama shi. Idanunsa ya karesu da bakin glass wanda ya kara haska fuskarsa ya kuma boye bacin ran da yake kwana yake tashi dashi tun komawarsa Katsina. Umarnin Daddy yake son bi na kauracewa Radhiya har zuwa ayi bikin gidansu sati mai zuwa a gama sannan su sake tayar da maganarta. Yana ganin wayarta da text wanda bayan kwana biyu babu reply ta dena yi. A tunaninta ya koma ga Ghazalatu ne ya manta da ita shine take kishi tayi fushi ta share shi. Matsananciyar kewarta ce ta sanya shi cewa zaiyi musu rakiya batare da an nema ba. Daddy yasan dalilinsa kuma yana tausaya masa. Lokaci guda har ya soma rama ga maganganu sunki ci sunki cinyewa a dangi.
Salame dai sakin baki tayi tana mamakin wadannan kyawawan mutane mazansu da matansu da suke fitowa daga motocin alfarma irin wadannan wurin wa suka zo? Ko sunyi batan kai ne? Kila bakin Chairman ne ko gidan Hakimi.
***********
Su Alh Ghoumar tun kafin su iso cikin garin Katsina suka sanar da Major suna tafe. Da suka zo gabadayansu sun kwana a wani hotel ne da safe shi da Alh Sidi da mutum biyu cikin 'ya'yansu suka je gidan Rtd Major Mustapha. Yayi farinciki da zuwansu ya sake basu labarin duk yadda ta kasancewa Mairama da su Radhiya. Guda cikin wadanda aka je dasu wanda shine auta a 'ya'yan Alh Sidi mai suna Ridwan yace zai maka Maikudi a kotu domin ya ha'incesu ya fada musu karya game da iyalin dan uwansu.
Major baiyi yunkurin bada hakuri ba yace idan sun dawo daga ganinsu din sai su je Sakkwaton.
"Amma meyasa baku ce a kawo muku su ba kuka taho gabadayanku?" Ya tambayesu da murmyshi a fuskarsa.
"Domin mu nunawa duniya cewa Mairama, Alheran da Zayyan dangin mahafinsu suna kaunarsu. Waye zamu samu ya rakamu saboda drebobin namu biyu ne kawai 'yan kasar nan"
Awwab kamar jira yake dama yazo gaishesu ne da Mami tace sun iso shine yace zaije. Daddy bashi da niyar hana shi saboda tausayinsa yake ji yana mamakin irin wannan soyayya mai karfi da ta shigi dan nasa farat daya.
Fitarsu daga gidan ko awa daya ba'ayi ba Mummy Gambo da Hussainar Mami suka zo. Ba da mutumci suka zo ba su Fauziyya na gaishe su babu wadda ta amsa.
"Ina babar taku?" Hussaina ta tambaya a dakile.
"Hussaina kenan, gani...kai ku bamu wuri" tace dasu Zayyana, suka tashi kuwa suka yi daki da sauri.
Zama tayi domin su gaisa Mummy ta soma fadan da ya kawota.
"Saboda wata yarinya can bare da babu wata alaka tsakaninku Hassana kike neman bata mana zumunci? Awwab da bakinsa yace yana son auren Ghazalatu amma tashi daya zance ya sauya saboda kuna son ku burge wasu"
"To banda ma abinta akwai wani abu da ita yarinyar tafi Ghazalatu ne? Alh Baba da su Babanmu sunce basu yarda ba ba sai ku hakura ba. Amma ace da kanki kuka je har gabansa don ya amince a bar danki shafaffe da mai ya yi auren gata mata biyu lokaci guda"
Daurewa take yi suna ta caba mata maganganu a ganinsu ita ma bata son 'yan uwanta su rabeta ne.
"Banda naci irin na Ghazalatu nace mata ta hakura da yaron nan taki. Wallahi ba don tana son shi ba har yanzu bazaki sake ganina a gidan nan ba. Nayi zuwan karshe ne inji menene ya sanya baki son auren nan?"
"Gambo idan Hussaina bata fahimta ba ta biye miki kun hade min kai nayi zaton ke zaki fahimta tunda mun zauna tare kin kuma san komai game da iyalin Zayyan. Wallahi da munsan da batun Ghazalatu Daddy bazai taba zancen wannan hadi ba. Ku duba irin kunyar dake tattare da ya koma yace musu an fasa auren nan"
"Ke kuma gara a kuntatawa 'yar kanwarki da yaji kunyar cewa 'yan kauye an fasa auren 'yarsu. Na tabbata 'yar dubu hamsin aka mika musu magana ta mutu har abada" cewar Hussaina.
"Ki barta tunda Umma tace mu kyalesu mu zuba musu ido daga ita har yaya Mustapha din. Saboda rashin sanin darajar zumunci kun shirya batawa da kowa..."
"Ke har zaki fada min zumunci Gambo" Mami tace rai a bace su Fauziyya suna jiyota daga daki kamar yadda Daddy yake jiyota daga falonsa da bai taso ba bayan tafiyar su Awwab.
"Kinsan me na rasa saboda zumunci? Farincikin 'yata, irin wanda kike nemawa taki 'yar amma saboda zumunci, saboda bin umarnin iyaye, saboda kada nayi sanadin rushewar ginin da iyayenmu suka fara nasa kafa na take farincikin Zahra"
Daga cikin dakin nasu Fauziyya ta zubawa yayarta ido yayin da Zahran ta fashe da matsanancin kuka.
Mami kanta hawaye take yi yadda 'yan uwanta suka gagara fahimtarta da mijinta. Komai suna yi ne domin dabbaka zumuncin amma yanzu saboda fitinar Gambo Ummansu ma ta soma fushi da ita.
"Ni Hassana banfi kowa cikinku ko cikin dangi ma haka ma 'ya'yana amma nasan cewa munyi kokari sosai wurin basu tarbiya duk da sun tashi nesa da gida. Zahra tana da wanda take so amma rana tsaka Alh Baba ya kiramu yace yayi musu mazaje ita da Fauziyya. Nafi kowa sanin irin soyayyar dake tsakanin Zahra da Raji amma na tausasheta nace tayi hakuri ta farantawa kakaninta zaiyi daidai da mune muka farantawa iyayenmu. Babu wani sabo, shakuwa ko soyayya yaran nan suka amince amma duk baku gani ba. Kullum kwanan duniya ina tashi da zulumin rayuwar da Zahra zata yi a gidan mijin da bata so. Ni da ya kamata na tayata neman farinciki nice na dage kada ta fitar da maganar ko mahaifinta bai sani ba balle 'yan uwanta. Ku har zaku fada min sanin darajar zumunci?"
Shiru suka yi aka rasa me magana a cikinsu. Basu taba ganin fushin Mami irin wannan ba. Major yana tsaye basu sani ba yana jin abinda take fada.
"Na gaji da cin kashin da kuke yi min daga ke har Hussaina akan auren Awwab. Babu wadda ta haifa min dan kuma na fada bazan taba hana shi auren wadda yake so ba. Idan yace zai iya hada duka su biyun Allah Ya dafa masa."
"Gara ki fadi abinda kike son fada zaki nuna mana kece uwar Awwab"
"Kamar yadda ke uwar Ghazalatu kike wanke kafa kika taho gidana domin taki 'yar ba. Wai ma me kuke so nayi muku ne? Ince Awwab ya zama silar kunyata mahaifinsa? Har abada bazan ce ba. Ni na san waye Zayyan a rayuwar Daddy kuma in sha Allahu bazamu ji kunyar iyalinsa ba."
"Dangin dangiro sun fimu" Gambo tace rai a matukar bace.
"Hussaina, Gambo. Ya isa haka kuzo ku wuce gidajenku"
Major ne yayi maganar idanunsa sun kankance ya fito musu a rikakken sojansa. Basu iya sake tankawa ba suka fita suka bar Mami Hassana tana zubar da hawaye.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Sabon salon make murya yayi don ya ga alamun larabawa ne mutanen nan "Assalam alaikum ya 'yan uwa. Kaifal durus wa ayna kaifal amal"
Allah Yasa akwai hayaniya a wurin kuma ya make murya ba kowa yaji ba sai Ummi da Radhiya. Kunya kamar Ummi ta nutse Radhiya kuwa juyawa tayi zata bar wurin saboda kunya ga dariya na cin ta. Malamijo ko a kwalarsa ya rinka mika hannu ana gaisawa. Ya sha mamaki ashe Zayyan yana da wannan dangi masu arziki haka amma yaron nan Maikudi ko tsinanne wallahi. Yayi musu tsakani da arziki irin wannan.
Magariba har ta kawo kai suka tashi aka rako su waje. Mammee tana kallon Ummi da murmushi tace "ni kuwa ina wani yaro nan lokacin taron sunan Alheran wanda baya son kowa ya tabata. Har yanzu ina da hotonku tare"
Ummi ta kalli Awwab tana dariya lokacin ya gane dashi ake ya zubawa Radhiya ido aka rinka dariya da Mammee tana fadin irin rigimar da aka rinka yi dashi da masu son daukar baby.
"Ina fata dashi zamu yi bikin ko?" Alh Sidi yace yana riko hannun Radhiya da ta dukar da kai.
Malamijo sai dariya "au, au, ashe anata abu bani da labari. Kai abu kyau"
Awwab ya kurawa Radhiya idanu fuskarsa dauke da murmushi ko kunya, yadda kowa sai da ya fuskanci akwai wani abu a tsakaninsu. Iyaye sai murna don abin yayi musu dadi. Sun fadawa Ummi zasu shigar da kara akan Maikudi amma sai bayan sunje musu tukunna. Bayan tafiyarsu Radhiya da wasu suka je suna kwashe kwanuka a can gefe kuma Ummi ce ta zaunar dashi da plate din abinci.
"Na kula ba ka son cin abinci Awwab. Ko yanayin aikinka ne yasa ka zama haka? Ace mutum da ance abinci sai yace baya jin yunwa"
Janyo plate din yayi yana kallon inda Radhiya ta duka tana daukar food flask. Ummi ta kawar da kai tana murmushi har sai da ya gama cin abincin sannan ta nutsu ta fara magana.
''Awwab akwai abinda yake faruwa ne a Katsina?"
Da sauri ya dago don da fari wata 'yar kunyarta yake ji.
"Me kika ji?"
"Ka fada min dai idan akwai abinda ke faruwa wanda ya kamata na sani. Gobe in sha Allah zamu bika mu tafi tare don yadda naji kukan Fauziyya hankalina ya tashi"
Wayarsa ta ga yana lalube a aljihu hankalinsa duk a tashe ta mika masa saboda ya manta ya bata dazu da aka kira. Ita kuma bata son boye masa saboda iyaye ba abin wasa bane. Ta yiwu zai iya magance matsalar a matsayinsa na babba. Yana karba ya shiga kiran Fauziyya wayarta tana chaji bata ji ba.
"Ummi akwai bayanin da nake son yi miki"
A raunane yayi maganar shiyasa kafin ya fara hankalinta ya sake tashi. Bai boye mata komai ba dangane da Ghazalatu da Radhiya da yake son hadasu.
"Ita wannan din ce take tayar maka da hankali akan bazata zauna da Ghazalatu din ba ko yaya?"
Dukar da kansa yayi nauyin maganar yasa bai iya bude bakinsa yayi mata gaskiyar bayani ba.
"A'a Ummi ta amice"
Salame dai sakin baki tayi tana mamakin wadannan kyawawan mutane mazansu da matansu da suke fitowa daga motocin alfarma irin wadannan wurin wa suka zo? Ko sunyi batan kai ne? Kila bakin Chairman ne ko gidan Hakimi.
***********
Su Alh Ghoumar tun kafin su iso cikin garin Katsina suka sanar da Major suna tafe. Da suka zo gabadayansu sun kwana a wani hotel ne da safe shi da Alh Sidi da mutum biyu cikin 'ya'yansu suka je gidan Rtd Major Mustapha. Yayi farinciki da zuwansu ya sake basu labarin duk yadda ta kasancewa Mairama da su Radhiya. Guda cikin wadanda aka je dasu wanda shine auta a 'ya'yan Alh Sidi mai suna Ridwan yace zai maka Maikudi a kotu domin ya ha'incesu ya fada musu karya game da iyalin dan uwansu.
Major baiyi yunkurin bada hakuri ba yace idan sun dawo daga ganinsu din sai su je Sakkwaton.
"Amma meyasa baku ce a kawo muku su ba kuka taho gabadayanku?" Ya tambayesu da murmyshi a fuskarsa.
"Domin mu nunawa duniya cewa Mairama, Alheran da Zayyan dangin mahafinsu suna kaunarsu. Waye zamu samu ya rakamu saboda drebobin namu biyu ne kawai 'yan kasar nan"
Awwab kamar jira yake dama yazo gaishesu ne da Mami tace sun iso shine yace zaije. Daddy bashi da niyar hana shi saboda tausayinsa yake ji yana mamakin irin wannan soyayya mai karfi da ta shigi dan nasa farat daya.
Fitarsu daga gidan ko awa daya ba'ayi ba Mummy Gambo da Hussainar Mami suka zo. Ba da mutumci suka zo ba su Fauziyya na gaishe su babu wadda ta amsa.
"Ina babar taku?" Hussaina ta tambaya a dakile.
"Hussaina kenan, gani...kai ku bamu wuri" tace dasu Zayyana, suka tashi kuwa suka yi daki da sauri.
Zama tayi domin su gaisa Mummy ta soma fadan da ya kawota.
"Saboda wata yarinya can bare da babu wata alaka tsakaninku Hassana kike neman bata mana zumunci? Awwab da bakinsa yace yana son auren Ghazalatu amma tashi daya zance ya sauya saboda kuna son ku burge wasu"
"To banda ma abinta akwai wani abu da ita yarinyar tafi Ghazalatu ne? Alh Baba da su Babanmu sunce basu yarda ba ba sai ku hakura ba. Amma ace da kanki kuka je har gabansa don ya amince a bar danki shafaffe da mai ya yi auren gata mata biyu lokaci guda"
Daurewa take yi suna ta caba mata maganganu a ganinsu ita ma bata son 'yan uwanta su rabeta ne.
"Banda naci irin na Ghazalatu nace mata ta hakura da yaron nan taki. Wallahi ba don tana son shi ba har yanzu bazaki sake ganina a gidan nan ba. Nayi zuwan karshe ne inji menene ya sanya baki son auren nan?"
"Gambo idan Hussaina bata fahimta ba ta biye miki kun hade min kai nayi zaton ke zaki fahimta tunda mun zauna tare kin kuma san komai game da iyalin Zayyan. Wallahi da munsan da batun Ghazalatu Daddy bazai taba zancen wannan hadi ba. Ku duba irin kunyar dake tattare da ya koma yace musu an fasa auren nan"
"Ke kuma gara a kuntatawa 'yar kanwarki da yaji kunyar cewa 'yan kauye an fasa auren 'yarsu. Na tabbata 'yar dubu hamsin aka mika musu magana ta mutu har abada" cewar Hussaina.
"Ki barta tunda Umma tace mu kyalesu mu zuba musu ido daga ita har yaya Mustapha din. Saboda rashin sanin darajar zumunci kun shirya batawa da kowa..."
"Ke har zaki fada min zumunci Gambo" Mami tace rai a bace su Fauziyya suna jiyota daga daki kamar yadda Daddy yake jiyota daga falonsa da bai taso ba bayan tafiyar su Awwab.
"Kinsan me na rasa saboda zumunci? Farincikin 'yata, irin wanda kike nemawa taki 'yar amma saboda zumunci, saboda bin umarnin iyaye, saboda kada nayi sanadin rushewar ginin da iyayenmu suka fara nasa kafa na take farincikin Zahra"
Daga cikin dakin nasu Fauziyya ta zubawa yayarta ido yayin da Zahran ta fashe da matsanancin kuka.
Mami kanta hawaye take yi yadda 'yan uwanta suka gagara fahimtarta da mijinta. Komai suna yi ne domin dabbaka zumuncin amma yanzu saboda fitinar Gambo Ummansu ma ta soma fushi da ita.
"Ni Hassana banfi kowa cikinku ko cikin dangi ma haka ma 'ya'yana amma nasan cewa munyi kokari sosai wurin basu tarbiya duk da sun tashi nesa da gida. Zahra tana da wanda take so amma rana tsaka Alh Baba ya kiramu yace yayi musu mazaje ita da Fauziyya. Nafi kowa sanin irin soyayyar dake tsakanin Zahra da Raji amma na tausasheta nace tayi hakuri ta farantawa kakaninta zaiyi daidai da mune muka farantawa iyayenmu. Babu wani sabo, shakuwa ko soyayya yaran nan suka amince amma duk baku gani ba. Kullum kwanan duniya ina tashi da zulumin rayuwar da Zahra zata yi a gidan mijin da bata so. Ni da ya kamata na tayata neman farinciki nice na dage kada ta fitar da maganar ko mahaifinta bai sani ba balle 'yan uwanta. Ku har zaku fada min sanin darajar zumunci?"
Shiru suka yi aka rasa me magana a cikinsu. Basu taba ganin fushin Mami irin wannan ba. Major yana tsaye basu sani ba yana jin abinda take fada.
"Na gaji da cin kashin da kuke yi min daga ke har Hussaina akan auren Awwab. Babu wadda ta haifa min dan kuma na fada bazan taba hana shi auren wadda yake so ba. Idan yace zai iya hada duka su biyun Allah Ya dafa masa."
"Gara ki fadi abinda kike son fada zaki nuna mana kece uwar Awwab"
"Kamar yadda ke uwar Ghazalatu kike wanke kafa kika taho gidana domin taki 'yar ba. Wai ma me kuke so nayi muku ne? Ince Awwab ya zama silar kunyata mahaifinsa? Har abada bazan ce ba. Ni na san waye Zayyan a rayuwar Daddy kuma in sha Allahu bazamu ji kunyar iyalinsa ba."
"Dangin dangiro sun fimu" Gambo tace rai a matukar bace.
"Hussaina, Gambo. Ya isa haka kuzo ku wuce gidajenku"
Major ne yayi maganar idanunsa sun kankance ya fito musu a rikakken sojansa. Basu iya sake tankawa ba suka fita suka bar Mami Hassana tana zubar da hawaye.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Sabon salon make murya yayi don ya ga alamun larabawa ne mutanen nan "Assalam alaikum ya 'yan uwa. Kaifal durus wa ayna kaifal amal"
Allah Yasa akwai hayaniya a wurin kuma ya make murya ba kowa yaji ba sai Ummi da Radhiya. Kunya kamar Ummi ta nutse Radhiya kuwa juyawa tayi zata bar wurin saboda kunya ga dariya na cin ta. Malamijo ko a kwalarsa ya rinka mika hannu ana gaisawa. Ya sha mamaki ashe Zayyan yana da wannan dangi masu arziki haka amma yaron nan Maikudi ko tsinanne wallahi. Yayi musu tsakani da arziki irin wannan.
Magariba har ta kawo kai suka tashi aka rako su waje. Mammee tana kallon Ummi da murmushi tace "ni kuwa ina wani yaro nan lokacin taron sunan Alheran wanda baya son kowa ya tabata. Har yanzu ina da hotonku tare"
Ummi ta kalli Awwab tana dariya lokacin ya gane dashi ake ya zubawa Radhiya ido aka rinka dariya da Mammee tana fadin irin rigimar da aka rinka yi dashi da masu son daukar baby.
"Ina fata dashi zamu yi bikin ko?" Alh Sidi yace yana riko hannun Radhiya da ta dukar da kai.
Malamijo sai dariya "au, au, ashe anata abu bani da labari. Kai abu kyau"
Awwab ya kurawa Radhiya idanu fuskarsa dauke da murmushi ko kunya, yadda kowa sai da ya fuskanci akwai wani abu a tsakaninsu. Iyaye sai murna don abin yayi musu dadi. Sun fadawa Ummi zasu shigar da kara akan Maikudi amma sai bayan sunje musu tukunna. Bayan tafiyarsu Radhiya da wasu suka je suna kwashe kwanuka a can gefe kuma Ummi ce ta zaunar dashi da plate din abinci.
"Na kula ba ka son cin abinci Awwab. Ko yanayin aikinka ne yasa ka zama haka? Ace mutum da ance abinci sai yace baya jin yunwa"
Janyo plate din yayi yana kallon inda Radhiya ta duka tana daukar food flask. Ummi ta kawar da kai tana murmushi har sai da ya gama cin abincin sannan ta nutsu ta fara magana.
''Awwab akwai abinda yake faruwa ne a Katsina?"
Da sauri ya dago don da fari wata 'yar kunyarta yake ji.
"Me kika ji?"
"Ka fada min dai idan akwai abinda ke faruwa wanda ya kamata na sani. Gobe in sha Allah zamu bika mu tafi tare don yadda naji kukan Fauziyya hankalina ya tashi"
Wayarsa ta ga yana lalube a aljihu hankalinsa duk a tashe ta mika masa saboda ya manta ya bata dazu da aka kira. Ita kuma bata son boye masa saboda iyaye ba abin wasa bane. Ta yiwu zai iya magance matsalar a matsayinsa na babba. Yana karba ya shiga kiran Fauziyya wayarta tana chaji bata ji ba.
"Ummi akwai bayanin da nake son yi miki"
A raunane yayi maganar shiyasa kafin ya fara hankalinta ya sake tashi. Bai boye mata komai ba dangane da Ghazalatu da Radhiya da yake son hadasu.
"Ita wannan din ce take tayar maka da hankali akan bazata zauna da Ghazalatu din ba ko yaya?"
Dukar da kansa yayi nauyin maganar yasa bai iya bude bakinsa yayi mata gaskiyar bayani ba.
"A'a Ummi ta amice"