Sashe 11
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“An sayar da rakuman naka ne?” Maikudi ya tambayeshi da zumudi.
“Eh, zasu taho min da kudin, jibi nake sa ran isowarsu” ya bashi amsa.
Sai ga Maikudi ya tashi jiki na rawa “Bari na kira yayyenka malalatan banza su zo a fara gyara gidan nan, mu gidanmu da yake da wadatar dakuna kamar ramin bera, Jume yaushe zaki ce sai ya nemi su Kawu don iya tonawa kai asiri”
Matsowa tayi kusa da Zayyan tana dariya “shima yasan wasa nake yi masa. Ka nemi masu fentin su zo ayi a gama da wuri sai a share dakunan ayi shimfida.”
Mayar da kansa wawa yayi suna ta bidirinsu yana biye musu. Maikudi da son banza harda cewa an hutar dasu yin fenti tunda su ma baifi wata uku ya rage dukkansu su ukun zasuyi aure ba.
**********
Cikin ikon Allah baki sun iso an kaisu masauki, washegari za’ayi taron suna. Zayyan ya wadata iyalinsa da duk abin da ya dace. Wani hadin kai da ga bangaren sojojin su ma sun hada masa gudunmawa sannan matayensu sun zage dasu ake komai kamar yadda su ka saba idan dayarsu ta haihu ko wani taro ya tashi. Salame da Nene Marka kanwar Malamijo a gidan zasu kwana sauran kuma duka suna gidansu Zayyan.
Su Nene sun riga isowa ga yamma jama’ar gidan sun watse sai ita da Mairama da Zainab. Mami ta wuce gida Fauziyya tana fama da zazzabi. Salisu na tsayar da mota a harabar gidajen da suke jere a wurin ta fito da sauri gabanta yana faduwa ta barshi yana yiwa security din da yayi musu rakiya zuwa gidan godiya.
Ciki ta shige tana fatan yin tozali da Zayyan. Sai dai idanunta akan na Mairama su ka sauka tana shayar da jaririyarta. Wani kululun bakinciki ya taso ya tsaya mata a wuya. Mairama tayi wani mugun kyau ta ciko ko ta ina. Kallo daya zaka yi mata kasan cewa hankalinta a kwance yake. Da sauri ta cire yarinyar da ga bakin abincinta ta tashi ta fada jikin Salame tana murna da tsalle sai da Yadikko tace tayi a hankali saboda yanayin jikin haihuwa.
“Wayyo Adda Salame nayi kewarki sosai ashe kina hanya. Ina yayan namu?”
Da kyar ta amsa “yana waje, ki tura mijinki ya bashi masauki”
Tsabar murna duk ta rude ma tayi hanyar daki neman mayafi sai ta jiyo muryar Zayyan din suna magana da Salisu. Salame cikin zakuwa ta juya “bari naje mu gaisa da angon karni”
Nene ce ta dakatar da ita “wa yake ta angon karni baki ga ‘yar taki ba, dawo kiyi zamanki nasan zasu shigo”
Ba haka taso ba amma dolente ta zauna. Mairama ta gabatar da Zainab wadda ta tashi tana tayata hadowa su Salame abinci da sha.
Daga nan Zainab din tayi sallama ta tafi Yadikko kuma ta shiga wanka. Baby tana kwance akan wani bargon yara mai kyau Mairama ta sake komawa kitchen ta soma kuka. Har wannan lokacin Salame dama bata yi karar cewa a bata ita ba bare ta dauketa saboda bata ma son ganinta har ranta. Kukan ya tsananta Mairama tana ji ta kasa cewa ta dauketa tunda ai ba kurma bace sannan tana jin nauyin ta fito ta dauketa a ga tayi rashin kunya.
Nene tana da ga bandaki kukan ya isheta tana tunanin me ya sami yarinyar. Harara Salame ta jefa mata sannan tasa hannu tana dan taba gefen jikinta wai rarrashi. Daga sama ta bayan kujerar ta ga an zuro hannuwa an dauketa.
Waigawa tayi da sauri idanunta su ka gane mata Zayyan Tureta. Sanye yake da khakinsa ya zura hularsa cikin wani abu da aka yiwa maballi daga kafadar rigar. Yayi matukar kyau da haske aure ya sake gyara shi. A kafada ya dora ‘yarsa yana shafa mata baya.
“Waye ya taba min mamana? Sojoji basa kuka fa ‘Yar soja”
“Zayyan ina wuni?” Salame tace cikin sanyin jiki. Bata san zai shigo ba da ko don ta burge shi ta dauki ‘yar.
Tamkar bai ga mutum ba ya shareta ya shiga kwalawa Mairama kira. Tana tsaye dama daga kofar kitchen din duk abinda Salame tayi ta gani tunda kujerar ta bata baya ne. Mamakin wannan mummunan canjin daga ‘yar uwarta take yi. Ashe ko me ya hadasu tun kafin suyi aure bai kare ba har yana son shafar ‘ya’ya. Hawaye taji ya soma sauko mata tana kallon bayan Salame a inda take zaune kamar gunki saboda yadda taji kunyar abinda ta yiwa jaririyar a gaban babanta.
Hawayen nata Zayyan ya gani ya matsa gareta da dayan hannun da yake shafa babyn ya janyota jikinsa da karfi ya rungume da hannu daya.
“Kada na sake ganin kin bar min yarinya ita kadai a falo. Idan babu kowa ki goyata ki shiga kitchen din…kinji”
“Kayi hakuri baza’a kuma ba, na ga Adda tana wurin ne” tace tana karbarta daga hannunsa. Salame ta juyo kamar mai ciwon wuya tana neman kalaman wanke kanta.
Kamar bai ji ba sai cewa yayi “Taimaka ki hada min abinci da zan tafi dashi inda zamu kwana da Salisu. Zan kaishi yayi sallah da wanka na dawo na dauka. Amma ki fara cikawa wannan sojar ciki”
Hannunta daya ta dora a gefen ido tayi masa salute “Yes Sir”
Matsowa yayi yana neman sumbatarta ta goce tana dariya. Mutuwar zaune Salame tayi. Shi kuwa Zayyan da biyu yake yi don ji yayi ya kara tsanarta. Ba don ta hada jini da Mairamansa ba da sai ya saka ta a guardroom ko na sa’a daya ne ya huce kukan ‘yarsa.
Da ya fita Mairama ta kawo mata sauran kayan abincin batare da ta sake yi mata magana ba ta zauna bawa ‘yar nono.
“Ki kwashe ba ci zanyi ba don yanzu ba komai ke zauna min a ciki ba”
Wai nan so take ta sanar da ita itama tana da cikin. Sai Mairama ta gwada mata halin matar soja da ta fara koyon yadda yake juya zance musamman idan ya fuskanci abu kake son sanar dashi da dabara don ka bashi haushi.
"Adda yaya hanya? Ya zaman Kano?"
Sai da Salame ta kara kallonta irin baki ji me nace dinnan ba sannan ta chanja zancen tace lafiya. Zaman kurame su ka koma har Nene ta fito tana tambayar me ya sami baby dazu take kuka. Babu wadda ta amsa mata a cikinsu duk sun daure fuska sai ta kyale su ta sa tv a gaba tana kallon tashar NTA.
Zaman ne ya ishi Salame ta tashi ta shiga daki wai zata yi wanka. Mairama ta bi bayanta taji ko akwai abin da zata bukata. A tsaye ta sameta tana karewa dakin kallo tana tabe baki.
"Af...ke fa gadon da Malamijo yayi mana dashi aka kawoki ko? Amma naga labulayen kamar sababbi ga TV ma a falon da firij. Kin fara sana'a ne ko Zayyan din kike tatikewa?"
"Yo Allah na tuba Adda mace da mijinta har sai kinji yaya ake kudi ke fita har a gyara mata gida? Dadin zama ne kawai da iya tafiyar da miji"
Ta fadi haka ne saboda gorin da Salamen ke shirin yi mata. Ita kuma Salame sai ta dauka cin fuska ne ko ta gane ta son sa.
"Ki dai bi a hankali maza basu da tabbas. Canja mace a wurinsu ba wata tsiya bace"
Zaro idanu Mairama tayi da mamaki. Har fatan aurenta ya mutu kuma Salame take yi? Indai haka ne dole ta kama kanta don bata ga me ta tsare mata ba da take nuna mata hassada irin haka. Kowa ya shaida mijinta yana da kudi ta rasa gane bakincikin na meye.
Karfe goma na safe a gidansu Zayyan tayi musu. Anyi taron suna na kayatarwa don Zayyan ya sakar musu yadda zasu fita kunya. 'Yan uwansa mutan Agadas sunyi masa halacci duk da rashin mahaifiyarsa sun zo da yawansu tare da gudunmawa mai yawa. A cewarsu basu sami bikinsa ba dole a fanshe yanzu. Gashi jaririya ta gaji sunan 'yar uwarsu.
Mutan Sumaila ma sun sha kallo ganin irin suturar da Zayyan ya wadata Mairama da su na fitar suna. Abin nasu ya burge sosai musamman da wata kanwar innar Zayyan ta kawo kayansu na gargajiya na kabilarsu ta Tamasheq ta bawa Mairama.
" 'Yata ga wannan ku saka ke da maigidanki da jikarmu ayi hoto. Dashi nake son tafiya saboda wadanda basu zo ba su ganku."
Mairama sai godiya take su Zainab suna tayata. Riga ce fara kamar buba ta zarta gwiwa da kadan gaban ta sha aiki da shudin zare sai zani shudi. Ga kuma sarkoki da yari duka irin nasu da abubuwan sakawa a ka. Mami ce ta karbi Radhiya yayin da wasu 'yan mata biyu kusan sa'annin Mairama su ka ja ta dakin da su ka kwana. Da taimakonsu ta shirya komai su suka yi mata. Abin hannu da na wuya da kunne harda hanci kowanne yayi mata cif. Na gashin kuwa sai da daya ta yi mata kalba kananu guda uku-uku a gefe da gefen kunnenta ta zubo mata dogon gashin irin nasu sannan aka dora mata shi ya zauna daga gaba kai kace wata sarauniya ce. Hatta fuskarta kwalliyarsu aka yi mata leben nan ya sha fenti yayi baki. Da yake fara ce ba karamin kyau tayi ba ta saje dasu. Wata guda ta soma ji daga tsakar gidan aka dora mata shudin yadi irin na zanin wani irin yafawa yadda suke yi sannan su ka rike mata hannuwa aka fito da ita.
Turus tayi ga wata irin kunya kamar sabon aure da su ka hada idanu da Zayyan. Yayi kyau har bata san yadda za ta kwatanta ba. Shima kayan gargajiyar ne a jikinsa na ciki farare babbar rigar da kuma rawani duka shudi.
Kanta a kasa shi kuwa ya zuba mata idanu, manya cikin 'yan uwan nasu suna ta guda. Da shirinsu suka zo da sunan yi masa nasu bikin. Taro ya kayatar da jama'a ba kadan ba duk da iyakarsu cikin gidan. Salame tamkar ta bude ido ta ganta a matsayin Mairama. Ganinsa cikin wannan kaya ba karamin sake fama mata ciwon son sa da yake nukurkusarta yayi ba.
“Eh, zasu taho min da kudin, jibi nake sa ran isowarsu” ya bashi amsa.
Sai ga Maikudi ya tashi jiki na rawa “Bari na kira yayyenka malalatan banza su zo a fara gyara gidan nan, mu gidanmu da yake da wadatar dakuna kamar ramin bera, Jume yaushe zaki ce sai ya nemi su Kawu don iya tonawa kai asiri”
Matsowa tayi kusa da Zayyan tana dariya “shima yasan wasa nake yi masa. Ka nemi masu fentin su zo ayi a gama da wuri sai a share dakunan ayi shimfida.”
Mayar da kansa wawa yayi suna ta bidirinsu yana biye musu. Maikudi da son banza harda cewa an hutar dasu yin fenti tunda su ma baifi wata uku ya rage dukkansu su ukun zasuyi aure ba.
**********
Cikin ikon Allah baki sun iso an kaisu masauki, washegari za’ayi taron suna. Zayyan ya wadata iyalinsa da duk abin da ya dace. Wani hadin kai da ga bangaren sojojin su ma sun hada masa gudunmawa sannan matayensu sun zage dasu ake komai kamar yadda su ka saba idan dayarsu ta haihu ko wani taro ya tashi. Salame da Nene Marka kanwar Malamijo a gidan zasu kwana sauran kuma duka suna gidansu Zayyan.
Su Nene sun riga isowa ga yamma jama’ar gidan sun watse sai ita da Mairama da Zainab. Mami ta wuce gida Fauziyya tana fama da zazzabi. Salisu na tsayar da mota a harabar gidajen da suke jere a wurin ta fito da sauri gabanta yana faduwa ta barshi yana yiwa security din da yayi musu rakiya zuwa gidan godiya.
Ciki ta shige tana fatan yin tozali da Zayyan. Sai dai idanunta akan na Mairama su ka sauka tana shayar da jaririyarta. Wani kululun bakinciki ya taso ya tsaya mata a wuya. Mairama tayi wani mugun kyau ta ciko ko ta ina. Kallo daya zaka yi mata kasan cewa hankalinta a kwance yake. Da sauri ta cire yarinyar da ga bakin abincinta ta tashi ta fada jikin Salame tana murna da tsalle sai da Yadikko tace tayi a hankali saboda yanayin jikin haihuwa.
“Wayyo Adda Salame nayi kewarki sosai ashe kina hanya. Ina yayan namu?”
Da kyar ta amsa “yana waje, ki tura mijinki ya bashi masauki”
Tsabar murna duk ta rude ma tayi hanyar daki neman mayafi sai ta jiyo muryar Zayyan din suna magana da Salisu. Salame cikin zakuwa ta juya “bari naje mu gaisa da angon karni”
Nene ce ta dakatar da ita “wa yake ta angon karni baki ga ‘yar taki ba, dawo kiyi zamanki nasan zasu shigo”
Ba haka taso ba amma dolente ta zauna. Mairama ta gabatar da Zainab wadda ta tashi tana tayata hadowa su Salame abinci da sha.
Daga nan Zainab din tayi sallama ta tafi Yadikko kuma ta shiga wanka. Baby tana kwance akan wani bargon yara mai kyau Mairama ta sake komawa kitchen ta soma kuka. Har wannan lokacin Salame dama bata yi karar cewa a bata ita ba bare ta dauketa saboda bata ma son ganinta har ranta. Kukan ya tsananta Mairama tana ji ta kasa cewa ta dauketa tunda ai ba kurma bace sannan tana jin nauyin ta fito ta dauketa a ga tayi rashin kunya.
Nene tana da ga bandaki kukan ya isheta tana tunanin me ya sami yarinyar. Harara Salame ta jefa mata sannan tasa hannu tana dan taba gefen jikinta wai rarrashi. Daga sama ta bayan kujerar ta ga an zuro hannuwa an dauketa.
Waigawa tayi da sauri idanunta su ka gane mata Zayyan Tureta. Sanye yake da khakinsa ya zura hularsa cikin wani abu da aka yiwa maballi daga kafadar rigar. Yayi matukar kyau da haske aure ya sake gyara shi. A kafada ya dora ‘yarsa yana shafa mata baya.
“Waye ya taba min mamana? Sojoji basa kuka fa ‘Yar soja”
“Zayyan ina wuni?” Salame tace cikin sanyin jiki. Bata san zai shigo ba da ko don ta burge shi ta dauki ‘yar.
Tamkar bai ga mutum ba ya shareta ya shiga kwalawa Mairama kira. Tana tsaye dama daga kofar kitchen din duk abinda Salame tayi ta gani tunda kujerar ta bata baya ne. Mamakin wannan mummunan canjin daga ‘yar uwarta take yi. Ashe ko me ya hadasu tun kafin suyi aure bai kare ba har yana son shafar ‘ya’ya. Hawaye taji ya soma sauko mata tana kallon bayan Salame a inda take zaune kamar gunki saboda yadda taji kunyar abinda ta yiwa jaririyar a gaban babanta.
Hawayen nata Zayyan ya gani ya matsa gareta da dayan hannun da yake shafa babyn ya janyota jikinsa da karfi ya rungume da hannu daya.
“Kada na sake ganin kin bar min yarinya ita kadai a falo. Idan babu kowa ki goyata ki shiga kitchen din…kinji”
“Kayi hakuri baza’a kuma ba, na ga Adda tana wurin ne” tace tana karbarta daga hannunsa. Salame ta juyo kamar mai ciwon wuya tana neman kalaman wanke kanta.
Kamar bai ji ba sai cewa yayi “Taimaka ki hada min abinci da zan tafi dashi inda zamu kwana da Salisu. Zan kaishi yayi sallah da wanka na dawo na dauka. Amma ki fara cikawa wannan sojar ciki”
Hannunta daya ta dora a gefen ido tayi masa salute “Yes Sir”
Matsowa yayi yana neman sumbatarta ta goce tana dariya. Mutuwar zaune Salame tayi. Shi kuwa Zayyan da biyu yake yi don ji yayi ya kara tsanarta. Ba don ta hada jini da Mairamansa ba da sai ya saka ta a guardroom ko na sa’a daya ne ya huce kukan ‘yarsa.
Da ya fita Mairama ta kawo mata sauran kayan abincin batare da ta sake yi mata magana ba ta zauna bawa ‘yar nono.
“Ki kwashe ba ci zanyi ba don yanzu ba komai ke zauna min a ciki ba”
Wai nan so take ta sanar da ita itama tana da cikin. Sai Mairama ta gwada mata halin matar soja da ta fara koyon yadda yake juya zance musamman idan ya fuskanci abu kake son sanar dashi da dabara don ka bashi haushi.
"Adda yaya hanya? Ya zaman Kano?"
Sai da Salame ta kara kallonta irin baki ji me nace dinnan ba sannan ta chanja zancen tace lafiya. Zaman kurame su ka koma har Nene ta fito tana tambayar me ya sami baby dazu take kuka. Babu wadda ta amsa mata a cikinsu duk sun daure fuska sai ta kyale su ta sa tv a gaba tana kallon tashar NTA.
Zaman ne ya ishi Salame ta tashi ta shiga daki wai zata yi wanka. Mairama ta bi bayanta taji ko akwai abin da zata bukata. A tsaye ta sameta tana karewa dakin kallo tana tabe baki.
"Af...ke fa gadon da Malamijo yayi mana dashi aka kawoki ko? Amma naga labulayen kamar sababbi ga TV ma a falon da firij. Kin fara sana'a ne ko Zayyan din kike tatikewa?"
"Yo Allah na tuba Adda mace da mijinta har sai kinji yaya ake kudi ke fita har a gyara mata gida? Dadin zama ne kawai da iya tafiyar da miji"
Ta fadi haka ne saboda gorin da Salamen ke shirin yi mata. Ita kuma Salame sai ta dauka cin fuska ne ko ta gane ta son sa.
"Ki dai bi a hankali maza basu da tabbas. Canja mace a wurinsu ba wata tsiya bace"
Zaro idanu Mairama tayi da mamaki. Har fatan aurenta ya mutu kuma Salame take yi? Indai haka ne dole ta kama kanta don bata ga me ta tsare mata ba da take nuna mata hassada irin haka. Kowa ya shaida mijinta yana da kudi ta rasa gane bakincikin na meye.
Karfe goma na safe a gidansu Zayyan tayi musu. Anyi taron suna na kayatarwa don Zayyan ya sakar musu yadda zasu fita kunya. 'Yan uwansa mutan Agadas sunyi masa halacci duk da rashin mahaifiyarsa sun zo da yawansu tare da gudunmawa mai yawa. A cewarsu basu sami bikinsa ba dole a fanshe yanzu. Gashi jaririya ta gaji sunan 'yar uwarsu.
Mutan Sumaila ma sun sha kallo ganin irin suturar da Zayyan ya wadata Mairama da su na fitar suna. Abin nasu ya burge sosai musamman da wata kanwar innar Zayyan ta kawo kayansu na gargajiya na kabilarsu ta Tamasheq ta bawa Mairama.
" 'Yata ga wannan ku saka ke da maigidanki da jikarmu ayi hoto. Dashi nake son tafiya saboda wadanda basu zo ba su ganku."
Mairama sai godiya take su Zainab suna tayata. Riga ce fara kamar buba ta zarta gwiwa da kadan gaban ta sha aiki da shudin zare sai zani shudi. Ga kuma sarkoki da yari duka irin nasu da abubuwan sakawa a ka. Mami ce ta karbi Radhiya yayin da wasu 'yan mata biyu kusan sa'annin Mairama su ka ja ta dakin da su ka kwana. Da taimakonsu ta shirya komai su suka yi mata. Abin hannu da na wuya da kunne harda hanci kowanne yayi mata cif. Na gashin kuwa sai da daya ta yi mata kalba kananu guda uku-uku a gefe da gefen kunnenta ta zubo mata dogon gashin irin nasu sannan aka dora mata shi ya zauna daga gaba kai kace wata sarauniya ce. Hatta fuskarta kwalliyarsu aka yi mata leben nan ya sha fenti yayi baki. Da yake fara ce ba karamin kyau tayi ba ta saje dasu. Wata guda ta soma ji daga tsakar gidan aka dora mata shudin yadi irin na zanin wani irin yafawa yadda suke yi sannan su ka rike mata hannuwa aka fito da ita.
Turus tayi ga wata irin kunya kamar sabon aure da su ka hada idanu da Zayyan. Yayi kyau har bata san yadda za ta kwatanta ba. Shima kayan gargajiyar ne a jikinsa na ciki farare babbar rigar da kuma rawani duka shudi.
Kanta a kasa shi kuwa ya zuba mata idanu, manya cikin 'yan uwan nasu suna ta guda. Da shirinsu suka zo da sunan yi masa nasu bikin. Taro ya kayatar da jama'a ba kadan ba duk da iyakarsu cikin gidan. Salame tamkar ta bude ido ta ganta a matsayin Mairama. Ganinsa cikin wannan kaya ba karamin sake fama mata ciwon son sa da yake nukurkusarta yayi ba.