Sashe 31
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kyabe fuska ta sake yi hankalinta yana kara tashi "zan wanke Ummi harda karkashi in gumbuda musu gishiri Yasin duk su mutu"
"Innawuro ko za'a bari ta gwada saka karkashin?" Mairama tace a hankali tana jin kunyar shigarwa 'yarta.
"Kyaleta Mairama don baki ga kan bane. Makero ya cinye keyar sai gashi kadan, gaban kuma amosani da kwarkwata. Yarinya mai cikar gashi da laushi duk ya lalace saboda rashin kula. Na fada miki Mairo ta biyo a cikar nan zai tofo da wuri"
"Ayya Ummi ki tausaya min mana" tace a wahale.
Emzee ya sake sakar mata nauyinsa akan cinyarta da ya dora kafafunsa yana dariya.
"Mugu daga ni"
Sake danneta yayi tayi kara Mairama ta kasa hakuri "Karami ka kiyayeni fa, me kake mata ne?"
Innawuro ya kalla suka sa dariya wai ta tarewa abokiyar fadanta sai ta kama bakinta ta kunshe.
Radhiya na ganin gashinta ya soma zuba ta soma wani sabon kukan "kiyiwa Allah da ManzonSa Innawuro ki bar min na zaman falo. Kina ji fa Baffa Gide yace duk aurar damu zaiyi"
Wannan karon dariya harda Mairama "wanne ne na zaman falo kuma?"
"Wanda zan rinka daurewa da ribbon inyi kwalliya"
Innawuro da Emzee suka cigaba da tunzurata tana ta zuba ana kwashe gashin "ance miki aure za'ayi miki ne kike neman gashin zaman falo?"
"Aure kuma Innawuro ai kamar habo ne. Yanzu idan kika kwashe gashin nan miji yazo yay...." shiru tayi da ta ji ana kankarar kan nata da reza.
Wani uban ihu ta saka an gama askin Innawuro tana mata kwaryar molo na gasken da reza ana kwashe sauran gashin da fatar da makero ya gama cinyewa tayi wani fari da tudu-tudu.
"Wayyo Allahna na shiga uku na lalace, wayyo, wayyo, wayyo"
Mairamu maficin hannunta ta daga zata kwada mata "wane irin sakarci ne wannan kike mana ihu kamar wata mara hankali"
Sai da ta tashi ta makawa Emzee harara da daradaran idanunta sannan tayi gaba tana cewa "dama Ummi wane hankali ne zaiyi saura akan budurwar da bata da gashi ai sai gyaran Allah"
Baki ta rike tana kada kai "anya yarinyar nan ba dabanci ta koyo a bodin din ba?"
"Ummi gang garesu fa na fitinannu inji wata kanwar abokina"
Daga cikin daki tana kuka ta leko "almunafunfun me ya kaika makarantar mata har ka jiyo gulma. Ummi ta sani dai SS ne ba wata kungiya ba"
Tsawa Mairama tayi mata akan ta dena amfani da kalmomi irin wadannan ga kaninta.
Innawuro tace "kema kinsan yau tunda da amincewarki akayi askin nan to dukkanmu sai ta nuna mana fushi take yi. Kai Karami zuba gashin nan a leda kaje ka kona. Kwarkwata harda ta sayarwa."
Hannuwansa yayi saurin nadewa a kirji cike da kyama "kwarkwatar zan taba? Ashe kowa zaiyi susa a gidan nan"
Dama Umminsa yake son tsokana ta fara fada yana dariya ya kwashe yaje bakin murhu ya zazzage. Waje yayi bayan ya wanke hannunsa aka bar su Mairama su kadai a tsakar gidan. Tayi zurfi a tunani da kwadayin ina ma ace zata iya ganin kamanin yaran a yanzu da suka kara girma. Alheran da Zayyan dinta suna da shekaru sha takwas da sha bakwai.
"Radhiya kyakkywa ce kamar wata dan daren goma sha hudu, Karami kuwa yadda kika san sojan maigidanki ba maraba sai haskenki da ya dauko"
Murmushi Mairama tayi kunya na kamata "Innawuro me ya kawo wannan bayanin kuma?"
"Daga yin abin arziki, godiya kawai zaki yi tunda na faranta miki"
Karamar dariya tayi ta lalubi sandarta ta tashi. Yanzu ta gane hanyar dakunan gidan ko babu dan jagora. Nasu ta karasa tana mitar wane irin jan kunne zata yiwa Alheran mai tambotsai. Kwanansu hudu tun washegarin dawowarta daga makaranta wai a saya mata form din makarantar sojoji. Tun Mairama na daukar abin wasa sai ga zance har kunnen su Ardo. Shine aka fara zancen aurar dasu. Ita kuma tana da burin Radhiya tayi ilimi mai zurfi amma bazata iya watsa musu kasa a ido ba. Tunawa da tayi anyi aski yau gidan kowa mai laifi ne a wurin 'Yar soja ya saka ta dariya ba shiri.
**********
Hadir sai tunani yake yi ina zasu je bayan masallaci maimakon su wuce gida. A motar kaninsa da yake kaisu sallar juma'a suke tare da Ibrahim. Yau sababbin kaya Ibrahim din ya saka masa iri daya da nasa, yadi ne mai kyau da laushi ruwan kwanduwar kwai anyi musu dinki iri daya wanda akayi da zare coffee color. Hatta hulunansu iri daya ne masu kalar zaren dinkin. Sai kamshi suke bazawa sunyi wani irin kyau. Tarin tambayoyi fal a zuciyar Hadir tun da aka fara komai. Mai aski har gida Ibrahim ya kawo yasa yayi masa gyaran fuska sabanin da da yake masa a gida da clipper da Zainab ta siyo masa.
Sun taimaka sun dora shi akan kujerarsa wheelchair bayan sun shiga gidan. Daga gefen matattakalar shiga anyi shafen sumunti alamun hanya ta hawa da wheelchair din. Gangara babansa yayi cikin ni'imtaccen falon da ya wadatu da sanyin AC da kamshi. Daga nan kanin Hadir yayi musu sallama ya juya abinsa.
Idanunsa na nuni da tashin hankali sai waige yake yi Ibrahim ya barshi ya nufi bakin wasu steps hudu da za'a taka abi hanyar dakuna. Su ma a gefe akwai wurin tura kujerar.
Wai kunya ce ta hana Zainab fitowa tana jinsu ta makale a daki. Ibrahim na taba kofar ta taso da wayoyinta a hannu kamar fitowa dama zata yi.
Wani kayataccen murmushi yayi mata na jindadi "Mama kinyi kyau wallahi"
Irin yadin jikinsu ta saka. Hatta zaren dinkin iri daya ne nata doguwar riga anyi mata surfani siriri mai kyau adon. Daurinta shima yayi kyau ga sarkar gwal dasu awarwaro. Haj Zainab kenan mata a gidan Hadir.
Murmushi tayi sai kuma tace "Wuce muje ni"
"Fara zuwa Mama naji cikina yana juya min"
Bai jira ta amsa ba ya fita da sauri ya shige sabon dakinsa ya dire akan gado yana murna. Abokinsa ne ya bashi shawarar kada ya tsaya musu a ka ya barsu su kadai.
Hadadden kamshinta ne ya fara zuwa hancin Hadir kafin yayi tozali da Zainabu Abunsa. Rufe ido yayi ya sake budesu a kanta. Wai da gaske Zainab ce kuwa?
A nutse ta iso har gaban kujerar tasa sai ta durkuso ta daidaita fuskarta da tasa. Hawayen farinciki ne ya sauko mata shi kuma idanunsa sunyi ja ya kasa dauke ido daga kanta.
Hannu tasa a kasan habarsa ta dago kansa tana masa kallon ido da ido ta sumbaci bakinsa sannan ta rungumo shi a jikinta tana mai kankame shi sosai ta saki kuka.
Hamdala Hadir ya rinka yi a jejjere a zuciyarsa don ya tabbata abu daya ne ma'anar kawo shi nan gidan da kuma kasancewarta a cikinsa.
**********
Danginsu Major na kusa da na nesa sai tururuwa suke domin ganinsu da yi musu barka da dawowa. Shekaru a kalla sha hudu ba wasa ba. Anyi haihuwa anyi rashi duk basa nan. Gidan kullum a cike da baki. Satinsu biyu kafin suka samu damar kai kayansu sabon gidan da suka rinka turo kudi domin ginawa a GRA. Sun sayi filin tun farkon fara aikin Mami kafin abubuwa su kara tsada.
Kwanansu biyu suna aikin son ganin gidan ya dau saiti abu yaci tura suka hakura sai sun dawo daga wurin su Hadir da Mairama.
Wannan Sojan mai alkawari da suke turawa kudin Mairama shine ya binciko musu Hadir yana Kano gidan iyayensa. Major yayi ta mamakin to me ya same shi yake gida. Mairama kuma wan Zayyan wato Maikudi tun a baya yace masa tayi aure amma Alheran tana Sakkwato wurinsa. Da wannan suka yi amfani akayi shawarar Kano zasu fara zuwa sannan su wuce Sakkwaton.
Basu riga sun sayi mota ba Daddy Harun da yake Abuja yanzu shine ya basu wata bus fara mai kyau da iyalinsa ke amfani da ita wurin tafiye tafiye tare da dreba.
Doki da fargabar yaya rayuwa ta kasancewa bayin Allahn nan sun cika zukatan su Mami da Major. Zahra da Fauziyya suna ta kokarin tuna Antinsu Zainab da Ibrahim da suke fada akan daukarsa. Babu wadda tayi shekara goma cikinsu lokacin. Labaran duka wanda Mami ke basu ne don babu abinda suke tunawa. Awwab kuma tuni 'yan kwanakin hutun nasa ya cinyesu a Katsina gashi tsarin aikinsu ba na zama wuri daya bane.
Da tambaya Allah Ya kaisu gidansu Hadir can cikin lungu. Bayan gaishe gaishe da iyayensa Major ya gabatar dasu. Sai da ta share hawaye tace yau kwanansa ashirin da shida da barin gidan an mayar da aurensa da Zainab tsohuwar matarsa.
"Bangane ba, da auren nasu ya mutu ne?" Yayi mata tambayar don neman karin bayani.
Murmushi tayi masa ganin hankalinsa ya tashi "Bari dai nasa a kaiku can gidan nasu sai kuji daga bakinta"
Wayar Zainab tasa aka kira mata bata shiga saboda suna asibiti. Kwanansu biyu da aure ta mayar dashi asibitin koyarwa na Kano wato Aminu Kano Teaching Hospital. Gwaji da bincike tasa ayi masa sosai inda aka gano matsalar da ya samu a kashin bayansa yayin fadawa wannan kwazazzabon a Liberia ita ce silar mutuwar jikinsa kashi ya danne wane bangaren na lakar bayansa. Rashin magana kuwa Likita ya tabbatar mata da cewa shock wato firgici ne ya haifar dashi. Da ace tun a baya sun tsananta dabarun dauke masa damuwa kila da tuni an manta da ya taba dena magana..
"Duk da haka Hajiya mijinki zai iya samun lafiya amma shawara mafi a'ala gaskiya ki fitar dashi ko da Egypt ne idan da hali. Lalurar ta dade a jikinsa yana bukatar kwararru a kansa da ingantattun kayan aiki"
Kallon Hadir tayi ta saki murmushi "Doctor ka taimaka ka tayani duba asibiti da kuma rough estimate na abinda zan bukata"
Bata ankara ba ta bayan kujerar taji an rungumo wuyanta sosai ta sa hannu tana dukan hannayen Ibrahim "dan gidanku shakeni zaka yi?"
Hadir yayi murmushi suna bashi sha'awa zamansu tamkar kaka da jikanta. Ibrahim dinsu matashi ne wanda kana kallonsa sai ka sake bare yanzu da mamansa ke kara wadata shi da kaya sa suka dace da zamani.
Kin sakinta yayi yana kara manna kansa a wuyanta "Mama mungode injini da Babana"
"Innawuro ko za'a bari ta gwada saka karkashin?" Mairama tace a hankali tana jin kunyar shigarwa 'yarta.
"Kyaleta Mairama don baki ga kan bane. Makero ya cinye keyar sai gashi kadan, gaban kuma amosani da kwarkwata. Yarinya mai cikar gashi da laushi duk ya lalace saboda rashin kula. Na fada miki Mairo ta biyo a cikar nan zai tofo da wuri"
"Ayya Ummi ki tausaya min mana" tace a wahale.
Emzee ya sake sakar mata nauyinsa akan cinyarta da ya dora kafafunsa yana dariya.
"Mugu daga ni"
Sake danneta yayi tayi kara Mairama ta kasa hakuri "Karami ka kiyayeni fa, me kake mata ne?"
Innawuro ya kalla suka sa dariya wai ta tarewa abokiyar fadanta sai ta kama bakinta ta kunshe.
Radhiya na ganin gashinta ya soma zuba ta soma wani sabon kukan "kiyiwa Allah da ManzonSa Innawuro ki bar min na zaman falo. Kina ji fa Baffa Gide yace duk aurar damu zaiyi"
Wannan karon dariya harda Mairama "wanne ne na zaman falo kuma?"
"Wanda zan rinka daurewa da ribbon inyi kwalliya"
Innawuro da Emzee suka cigaba da tunzurata tana ta zuba ana kwashe gashin "ance miki aure za'ayi miki ne kike neman gashin zaman falo?"
"Aure kuma Innawuro ai kamar habo ne. Yanzu idan kika kwashe gashin nan miji yazo yay...." shiru tayi da ta ji ana kankarar kan nata da reza.
Wani uban ihu ta saka an gama askin Innawuro tana mata kwaryar molo na gasken da reza ana kwashe sauran gashin da fatar da makero ya gama cinyewa tayi wani fari da tudu-tudu.
"Wayyo Allahna na shiga uku na lalace, wayyo, wayyo, wayyo"
Mairamu maficin hannunta ta daga zata kwada mata "wane irin sakarci ne wannan kike mana ihu kamar wata mara hankali"
Sai da ta tashi ta makawa Emzee harara da daradaran idanunta sannan tayi gaba tana cewa "dama Ummi wane hankali ne zaiyi saura akan budurwar da bata da gashi ai sai gyaran Allah"
Baki ta rike tana kada kai "anya yarinyar nan ba dabanci ta koyo a bodin din ba?"
"Ummi gang garesu fa na fitinannu inji wata kanwar abokina"
Daga cikin daki tana kuka ta leko "almunafunfun me ya kaika makarantar mata har ka jiyo gulma. Ummi ta sani dai SS ne ba wata kungiya ba"
Tsawa Mairama tayi mata akan ta dena amfani da kalmomi irin wadannan ga kaninta.
Innawuro tace "kema kinsan yau tunda da amincewarki akayi askin nan to dukkanmu sai ta nuna mana fushi take yi. Kai Karami zuba gashin nan a leda kaje ka kona. Kwarkwata harda ta sayarwa."
Hannuwansa yayi saurin nadewa a kirji cike da kyama "kwarkwatar zan taba? Ashe kowa zaiyi susa a gidan nan"
Dama Umminsa yake son tsokana ta fara fada yana dariya ya kwashe yaje bakin murhu ya zazzage. Waje yayi bayan ya wanke hannunsa aka bar su Mairama su kadai a tsakar gidan. Tayi zurfi a tunani da kwadayin ina ma ace zata iya ganin kamanin yaran a yanzu da suka kara girma. Alheran da Zayyan dinta suna da shekaru sha takwas da sha bakwai.
"Radhiya kyakkywa ce kamar wata dan daren goma sha hudu, Karami kuwa yadda kika san sojan maigidanki ba maraba sai haskenki da ya dauko"
Murmushi Mairama tayi kunya na kamata "Innawuro me ya kawo wannan bayanin kuma?"
"Daga yin abin arziki, godiya kawai zaki yi tunda na faranta miki"
Karamar dariya tayi ta lalubi sandarta ta tashi. Yanzu ta gane hanyar dakunan gidan ko babu dan jagora. Nasu ta karasa tana mitar wane irin jan kunne zata yiwa Alheran mai tambotsai. Kwanansu hudu tun washegarin dawowarta daga makaranta wai a saya mata form din makarantar sojoji. Tun Mairama na daukar abin wasa sai ga zance har kunnen su Ardo. Shine aka fara zancen aurar dasu. Ita kuma tana da burin Radhiya tayi ilimi mai zurfi amma bazata iya watsa musu kasa a ido ba. Tunawa da tayi anyi aski yau gidan kowa mai laifi ne a wurin 'Yar soja ya saka ta dariya ba shiri.
**********
Hadir sai tunani yake yi ina zasu je bayan masallaci maimakon su wuce gida. A motar kaninsa da yake kaisu sallar juma'a suke tare da Ibrahim. Yau sababbin kaya Ibrahim din ya saka masa iri daya da nasa, yadi ne mai kyau da laushi ruwan kwanduwar kwai anyi musu dinki iri daya wanda akayi da zare coffee color. Hatta hulunansu iri daya ne masu kalar zaren dinkin. Sai kamshi suke bazawa sunyi wani irin kyau. Tarin tambayoyi fal a zuciyar Hadir tun da aka fara komai. Mai aski har gida Ibrahim ya kawo yasa yayi masa gyaran fuska sabanin da da yake masa a gida da clipper da Zainab ta siyo masa.
Sun taimaka sun dora shi akan kujerarsa wheelchair bayan sun shiga gidan. Daga gefen matattakalar shiga anyi shafen sumunti alamun hanya ta hawa da wheelchair din. Gangara babansa yayi cikin ni'imtaccen falon da ya wadatu da sanyin AC da kamshi. Daga nan kanin Hadir yayi musu sallama ya juya abinsa.
Idanunsa na nuni da tashin hankali sai waige yake yi Ibrahim ya barshi ya nufi bakin wasu steps hudu da za'a taka abi hanyar dakuna. Su ma a gefe akwai wurin tura kujerar.
Wai kunya ce ta hana Zainab fitowa tana jinsu ta makale a daki. Ibrahim na taba kofar ta taso da wayoyinta a hannu kamar fitowa dama zata yi.
Wani kayataccen murmushi yayi mata na jindadi "Mama kinyi kyau wallahi"
Irin yadin jikinsu ta saka. Hatta zaren dinkin iri daya ne nata doguwar riga anyi mata surfani siriri mai kyau adon. Daurinta shima yayi kyau ga sarkar gwal dasu awarwaro. Haj Zainab kenan mata a gidan Hadir.
Murmushi tayi sai kuma tace "Wuce muje ni"
"Fara zuwa Mama naji cikina yana juya min"
Bai jira ta amsa ba ya fita da sauri ya shige sabon dakinsa ya dire akan gado yana murna. Abokinsa ne ya bashi shawarar kada ya tsaya musu a ka ya barsu su kadai.
Hadadden kamshinta ne ya fara zuwa hancin Hadir kafin yayi tozali da Zainabu Abunsa. Rufe ido yayi ya sake budesu a kanta. Wai da gaske Zainab ce kuwa?
A nutse ta iso har gaban kujerar tasa sai ta durkuso ta daidaita fuskarta da tasa. Hawayen farinciki ne ya sauko mata shi kuma idanunsa sunyi ja ya kasa dauke ido daga kanta.
Hannu tasa a kasan habarsa ta dago kansa tana masa kallon ido da ido ta sumbaci bakinsa sannan ta rungumo shi a jikinta tana mai kankame shi sosai ta saki kuka.
Hamdala Hadir ya rinka yi a jejjere a zuciyarsa don ya tabbata abu daya ne ma'anar kawo shi nan gidan da kuma kasancewarta a cikinsa.
**********
Danginsu Major na kusa da na nesa sai tururuwa suke domin ganinsu da yi musu barka da dawowa. Shekaru a kalla sha hudu ba wasa ba. Anyi haihuwa anyi rashi duk basa nan. Gidan kullum a cike da baki. Satinsu biyu kafin suka samu damar kai kayansu sabon gidan da suka rinka turo kudi domin ginawa a GRA. Sun sayi filin tun farkon fara aikin Mami kafin abubuwa su kara tsada.
Kwanansu biyu suna aikin son ganin gidan ya dau saiti abu yaci tura suka hakura sai sun dawo daga wurin su Hadir da Mairama.
Wannan Sojan mai alkawari da suke turawa kudin Mairama shine ya binciko musu Hadir yana Kano gidan iyayensa. Major yayi ta mamakin to me ya same shi yake gida. Mairama kuma wan Zayyan wato Maikudi tun a baya yace masa tayi aure amma Alheran tana Sakkwato wurinsa. Da wannan suka yi amfani akayi shawarar Kano zasu fara zuwa sannan su wuce Sakkwaton.
Basu riga sun sayi mota ba Daddy Harun da yake Abuja yanzu shine ya basu wata bus fara mai kyau da iyalinsa ke amfani da ita wurin tafiye tafiye tare da dreba.
Doki da fargabar yaya rayuwa ta kasancewa bayin Allahn nan sun cika zukatan su Mami da Major. Zahra da Fauziyya suna ta kokarin tuna Antinsu Zainab da Ibrahim da suke fada akan daukarsa. Babu wadda tayi shekara goma cikinsu lokacin. Labaran duka wanda Mami ke basu ne don babu abinda suke tunawa. Awwab kuma tuni 'yan kwanakin hutun nasa ya cinyesu a Katsina gashi tsarin aikinsu ba na zama wuri daya bane.
Da tambaya Allah Ya kaisu gidansu Hadir can cikin lungu. Bayan gaishe gaishe da iyayensa Major ya gabatar dasu. Sai da ta share hawaye tace yau kwanansa ashirin da shida da barin gidan an mayar da aurensa da Zainab tsohuwar matarsa.
"Bangane ba, da auren nasu ya mutu ne?" Yayi mata tambayar don neman karin bayani.
Murmushi tayi masa ganin hankalinsa ya tashi "Bari dai nasa a kaiku can gidan nasu sai kuji daga bakinta"
Wayar Zainab tasa aka kira mata bata shiga saboda suna asibiti. Kwanansu biyu da aure ta mayar dashi asibitin koyarwa na Kano wato Aminu Kano Teaching Hospital. Gwaji da bincike tasa ayi masa sosai inda aka gano matsalar da ya samu a kashin bayansa yayin fadawa wannan kwazazzabon a Liberia ita ce silar mutuwar jikinsa kashi ya danne wane bangaren na lakar bayansa. Rashin magana kuwa Likita ya tabbatar mata da cewa shock wato firgici ne ya haifar dashi. Da ace tun a baya sun tsananta dabarun dauke masa damuwa kila da tuni an manta da ya taba dena magana..
"Duk da haka Hajiya mijinki zai iya samun lafiya amma shawara mafi a'ala gaskiya ki fitar dashi ko da Egypt ne idan da hali. Lalurar ta dade a jikinsa yana bukatar kwararru a kansa da ingantattun kayan aiki"
Kallon Hadir tayi ta saki murmushi "Doctor ka taimaka ka tayani duba asibiti da kuma rough estimate na abinda zan bukata"
Bata ankara ba ta bayan kujerar taji an rungumo wuyanta sosai ta sa hannu tana dukan hannayen Ibrahim "dan gidanku shakeni zaka yi?"
Hadir yayi murmushi suna bashi sha'awa zamansu tamkar kaka da jikanta. Ibrahim dinsu matashi ne wanda kana kallonsa sai ka sake bare yanzu da mamansa ke kara wadata shi da kaya sa suka dace da zamani.
Kin sakinta yayi yana kara manna kansa a wuyanta "Mama mungode injini da Babana"