← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 157

Sashe 37

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kaji mutum kamar ba namiji ba, meye na kukan? Ai komai ya wuce da yardar Allah"

Hawaye yake da gaske yaji bazai iya zama ba ya tashi ya nufi inda yasan nan ne dakinsa. Mami tace da Mairama ta dena damuwa zai hakura kamar kowa.

Ghazalatu ko shiga dakin bata yi ba ranta ya baci da kukan da wannan makauniyar ta saka mata shi. A take taji wani haushin Mairama ya kamata. Dama akan wannan da kallo daya zai sanar da mutum daga kauye take yake ta damuwa harda kuka. 

"Ghazalatu shigo mana, kinga yayanki na kuka ko? Kada ki damu zanyi masa magana"

Ba yadda ta iya dole ta shiga tana nadamar tahowa don gidan har ya fice mata daga rai. Akwatinta ta tura gefe sai da Mami tace "ga Ummin Awwab ki gaisheta mana"

"Sannu"

"Yauwa sannu 'yata. Yaya gajiyar hanya?"

Mugun kallon da Mami ta watsa mata ya sa ta chanja salon gaisuwar tace "ina wuni" a dakile.

Ba jimawa Mairama ta shiga bandaki ai kuwa Mami rai a bace ta soma yiwa Ghazalatu fada.

"Kar ki yarda na sake ganin irin haka kina jina? Wannan matar da kike gani ba karamar daraja da kima gareta a wurinmu ba. Dangi kowa kokari yake ya tayamu karramata. Bazan lamuncewa dabi'ar banza ba kinzo kina wani cin magan"

Abinka da makaho kunne ya kara fikewa. Mairama tana jinsu tayi murmushi kawai. To dama yaushe zata yi tunanin kowa nasu zai sota. Ita ce fa wadda mahaifinta har yau bai taba bin sawunta ba sai dai ita har sau uku taje kuma tana aika masa da 'yan abinda ba'a rasawa.

"Kiyi hakuru gajiyar hanya ce" Ghazalatu tace da ta tuna Mami ce fa mahaifiyar Awwab.

"A dai gyara"

**********

Fauziyya da Zahra suna kallo a falo Zainab tana duba takardun asibitoci uku da likitann nan ya aiko mata. Ibrahim baya gidan yaje gaishe da kakaninsa Hadir kuwa bacci yake a daki.

Radhiya ce ta fito yau babu hijabi tana dan murmushi fuskarta tasha kwalliua harda janbaki. Fauziyya da Zahra suka shiga gyara dankwalayensu. Zayyana daga shiga deban abinci a kitchen ta kasa fitowa tunda taji muryar Radhiya tana cewa.

"Ha mutum ya fito yasha iskar Allah."

Tana zama su Zahra suka mike, Zainab ta kwashe da dariya. Radhiya ta zama horror tunda tace zata yi musu balotelli. Jiya a gabanta Ibrahim ya nuna musu hoton Mario Balotelli wani dan ball baki na kasar Italy wanda yake kwashe kansa hagu da dama ya bar tsoro guda a tsakiya tun daga gaba har keya.

A karkace ta kallesu "tashi kuma zaku yi daga zamana?" 

"Ni bacci nake ji" cewar Fauziyya

"Fitsari zanyi ni kuma" Zahra tace tana matsawa gefe.

"To sai kun dawo, gumi ne ya dameni yau na saka lasi" kawai sai ta tuge dankwalinta rantal ya bayyana.

Wata irin dariya suka kwashe da ita har Zayyana dake kofar kitchen. Zainab na dago kai ta mayar dashi kan takardu kafin ta soma  dariya itama. Radhiya ta bata rai "ayi dariya da kyau naje soja na dawo. Kuma na dena daura dankwali iska zan rinka sha"

"Ki rufa mana asiri don Allah ki rufe" Zahra tace idonta harda hawayen ganin wannan gashi na Radhiya tsilli tsilli.

"Allah bazan rufe ba iska nazo sha."

Kyalesu tayi suka sha dariyarsu tana cewa su kiyaye kada tayi sanadin da zaa kai amare da kwalkwal. Daga nan hira ta kaure don daga Zahran har Fauziyya basu da girman kai duk da ba sa'arsu bace. Suna cikin hira ta soma gyangyadi Zainab tace ta koma daki ta soma musu irin na masu magagi wai ba bacci take ba. Kafin la'asar ta bingire akan doguwar kujera abinta. Ana kiran sallah duka suka watse sai Zayyana.

Ta wayar Fauziyya Awwab ya kira yace yana kofar gida don dreban Harun ne ya kawo shi. Zayyana da ta amsa wayar taje ta bude masa gate tana murnar ganinsa.

Suna shigowa falo idanunsa suka gane masa Radhiya. Kanta yake iya gani sai rabin jikinta ta rufa dankwalinta daga kasa kuma fuskarta jikin kujera take kallo. Ya dai tabbatar kayan mata ne a jikin mai wannan kan a sanyaye ya karasa shigowa Zainab tana turo Hadir ya kallesu da tausayawa. Da guda daya tilo da suka haifa ashe dan daudu ne jiya da Mami da Ummi suna bashi labarin komai yana kwalla basu hada masa da wannan ba.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Iyakar karfinta tasa suna jan hijabin nata su ma suna ja. Mami na isowa tace su dagata amma an makara don Zahra tayi nasarar cire dankwalin.

Emzee da Ibrahim suna bakin kofa don sun jiyo hayaniya daga dakin. Rasa me bakin magana akayi harda Mami kuwa. Zainab ce ta kawo Mairama dakin, tunda taji shiru tasan aikin gama ya gama.

Zayyana ce ta fara dariya gashi ya  soma lekowa amma saboda makero baifi a kirga ba sai wani uban fari fari kamar amosani kamar kora. Kullum tana shafa mai idan tayi wanka amma yau saboda da mutane a dakin ta hakura ta daure kayanta.

Kowa ta kalla gimtse dariya yake ta harzuka sosai tayi kan Zahra tana ihu "wallahi sai na rama"

"KE! Samu wuri ki zauna kada naji kinyi fada da kowa."

Kuka ta fashe dashi da karfi "wallahi Ummi kada ki cuceni ki barni na rama."

"Zahra bata dankwalinta kafin na saba muku. Wane irin abu ne haka da girmanku saboda Allah." Mami ta soma fada.

Jefa mata dankwalin Zahra tayi don yadda take kallonta kamar kura ta ga nama bazata so hannunsu ya gogi na juna ba. 

Jikinsu sai yayi sanyi saboda kukan da take yi ta dauki dankwalinta ta kulle kan sannan ta mayar da hijabinta. Zainab da Mami na bata hakuri taki kula kowa sai sautin kuka da take karawa. Mairama tace su kyaleta ba shiru zata yi ba. Kowa ya fita daga dakin tana zaune tana kukanta dole Mami taje ta fadawa Major.

"A kirawo min ita"

Zahra ta kalli Fauziyya, a tsorace tace "ba dai ni ba, kece babba kuma ke kika bude mata kan"

"Zayyana...." Zahra ta soma kira ta bari saboda kyabe fuskar da ta ga tayi ta koma gefen Major tana cewa 

"Daddy kace bazani ba" 

"Mazaje waye zai kira min 'yata?" Yace da Ibrahim da Emzee kamar yana rokonsu.

Ibrahim ne ya tashi, Emzee kamar ruwa ya cinye shi. Yana zuwa ya sameta ta gama hada kayanta a cikin jakar da tazo da ita tana bakin kofa zata fito.

"Dariya ka dawo yi?"

"Daddy ne yake kiranki"

Gani tayi ya tsaya kallonta yaki tafiya ta zaro masa idanu "in sake bude maka ka gani da kyau ne?"

Murmushi yayi mata kawai don idan ya sake ya bude baki sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba. Sai yanzu ya gane meyasa kan nata yake kullum a daure kamar mai tallan magani.

Da jakarta a hannu ta shiga su Zahra suka fara kuskus. Daddy ya gani sai ya shareta  "waye ya saka ki kuka?"

Rage tsayi tayi bakin nan a gaba kowa ya ganta yasan an tabota karshe "Daddy na san komai fa, kaine da kanka ka turo Zayyana su gane min aski na"

Kafin su shigo sai da Mami ta roke shi akan ya taimaka kada yayi dariya. An san soja da dakiya, amma a cikin iyalansu, iyalan ma na Zayyanunsa mantawa yake ya taba zama soja. Ya fi fahimtar ya sake tare dasu ya nuna musu shi uba ne a garesu domin kada a sami wani shamaki tsakaninsu.

"Cewa nayi ace ki wanke kanki fa 'Yar soja uwar sojoji"

Sai da tayi murmushin jindadin kirarin ta sake daurewa "a bani kudin mota in tafi gida ko kuma a barni na rama"

"Radhiya kiyi hakuri da kaina zanyi punishing dinsu. Amma ki bar zancen ramuwa ko tafiya gida" Mami tace tana hararar bangaren da su Zahra suke.

Kumbura baki tayi "ni dai wallahi sai dai a zabi daya"

Mairama taji kunyar kada a fara ganin ko harda sakacin tarbiya a halayen Radhiya. Fada ta soma yi mata tace ta tashi ta koma ciki ta zauna.

"Allah Yasa naji kinyi fada da wani, zaki ga yadda zanyi dake. Ana lallabaki kina wani botsarewa mutane"

"Laifinsu ne fa ki kyaleta, zo nan kinji Radhiya"

Kin tashi tayi tana kallon Zainab din tace "kema Mama na ga kamar kin danyi dariya da aka bude kan"

Mairama ta sake fusata Daddy yace duk suyi hakuri laifinsa ne amma tayi hakuri.

"Ku kuma manyan ku daku kuna tsokanarta na kusa bata kambun girma a gidan nan. Kwanannan zata zama yayar kowa da kowa a cikinku sai na ga wanda zai sake gane mata askinta" murmushi yayi amma bata ji haushi ba tunda ya yi mata alkawarin zata zama yayar kowa.

Da yake ba riko gareta ba sai ta saki fuska ta harari wannan ta harari wancan "kun dai ji me Daddy yace, kuma daga nan ma soja zai kaini abuna. Hahaha idan na dawo gidan nan za'a ga kawuna"

Zayyana sai tasa hannu ta rike nata kan tana kallonta a tsorace "yanke mana kai zaki yi?"

"Inaaa yarinya kan Balotelli zanyi muku in huce haushin yau"

Ibrahim ya tuntsire da dariya harda fadowa daga kan kujera. Zainab ta daka masa duka a baya ko a jikinsa sai dariya yake "zan rike miki su 'yar uwa, ai dai baki ganni ina dariya ba"

Major ma dariyar yake yadda ta hakikance abinta. Sauran matan babu wadda ta damu da ball ko 'yan ball balle su fahimci me take nufi da Balotelli din. Hakuri dai yayi ta bata tana kara jaddada masa burinta na zama soja tunda ta ga yana lallabata.

"Soja mai babban mukami zanyi miki amma ta cikin gida, yanzu dai ku tashi amma idan kun shiga ciki kada ki kula kowa"

"Daddy gaba fa kenan?" Tace tana ware idanunta ta rike haba.

Su Zainab sai dariya, Major ya dage yana ta bayanin cewa ba gaba yake nufi ba. Kada ta kula su dai azo ana rigima.

"Au ho...ai na hakura tunda idan na dawo daga soja zan dauki mataki. Baba zanyi kyau da soja ko?" Tace tana kallon Hadir.
Chapter 37 · 0% Book details