Sashe 98
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai ta taji an kira sallah azahar sannan ta samu kuzarin unƙurawa ta miƙe tsaye. Har taje tayi wanka tayi alwala abu ɗaya ne yake mata yawo.
Idan har Asim ya dawo ya tararda ita a gidan zai zaci ko dan tana son ya mayar da ita ne. Ita kuma yanzu ta yanke ƙauna da shi, idan akwai wanda ta tsana a duniya Asim ne, kuma har gobe bata nadamar zaɓar abunda yake cikinta saman da Asim.
Bayan ta yi sallah azahar ta ɗora da nafili sannan ta rokowa Allah buƙatarta, ta kai masa kukanta ta miƙa masa lamurranta.
Jingina ta yi da ginin gurin tana kuka, da hawaye masu zafi. Irin mutanen da suka yi nemanta aure take tuna amman kowa ya zo tace sai Asim, ayau Asim ɗin ne ya zaɓi rabuwa da ita saboda cikin shi, jininshi.
Tashi tayi ta koma saman katifa ta kwanta, tana kukan zuci wanda ya fili illa da baƙinciki. Wayarta tayi ƙarar saƙo duk da taji daɗin kwanciyar hakan be hanata unƙurawa ta ɗauƙi wayar ta duba ba.
_Karki kuskura cewa za ki siyar da gidan nan, amman na miki lamani ki zauna har ki canja shawara, idan kin yi tunani mai kyau na shirya maida ki a matsayin mata ta!_
“Kaico...”
Shine kawai abunda ta furta bayan ta gama karanta text ɗin ta share hawayenta. Kanta ta ɗaga sama tana kallon ɗakin, kwata-kwata jin tayi gidan ya fita a ranta. Sai dai kuma bata da gurin zuwa, duk inda zata je be yi kamar gidan mahaifinta ba, da ace Abbah ba xai wuƙantata ba, da ba zata damu da maganar mutane ba matuƙar tana gidansu, a ƙarƙashin iyayenta.
Hijabinta ta ɗauka ta saka, ta ɗauki jakarta da wasu ƙaƙanan abubuwa nata ta saka a jakar sannan ta fito, tun da ta baya bq ɗin baya ta sake kallon ta ba har ta fice daga gidan.
Fuskarta ta kumbura sosai haka ma idanunta, duk wanda ya ganta zai san tayi kuka, hakan yasa ta sanda kai ƙasa har ta isa titi. Napep ta tara sai da ta shiga sannan ta soma tunanin inda zai kai ta. Bata da wadataccen kuɗin da zata kama wani gidan ta zauna, kuma ta san ba mutuncin ta ba ne ta kama gida a wani gurin. Kuma bata jin zama a gidan dan zata iya aikata komai saboda baƙinciki.
“Hajiya ina za a kai ki?”
Tsayawa tayi tunani, har tashi Napep ɗin.
“Kai ni tashar mota, inda ake hawa motar sokoto”
“To amman yanzu tashar gov sun tashi sai dai babbar tasha”
Ya hau kan titi yana ƙara ƙure volume ɗin napep ɗin dake tashin wakar Umar m shariff. Ita dai saurare kawai take tana hawaye har suka isa, ɗari biyu ta ciro ta bashi ya miƙa mata canjin naira hansi sannan ta fita shi kuma ya juya.
“Sokoto, Kano, Kaduna, Abuja, jigawa, Kebbi, Zamfara”
Haka ƴan union ɗin suke ta faɗi suna neman passengers. Wasu suka yo kan Namra da gudu suna tambayar ta inda zata ta, tsaye kawai tayi tana tunanin inda zata ce duk da ta zo da niyar zuwa sokoto ne sai kuma ta ji ba zata iya, har tana jin ma kamar ta koma gida...
“Hajiya Kaduna zaki je?”
Wani daga cikin su ya tambaya, sai ta ɗaga masa kai.
“Eh Kaduna zan je”
“Ga mota can daman mutum biyu ake jira, ina kayan ki suke?”
“Bana da kaya”
“Okay muje ga mota can”
Shine yayi mata ja gaba har gurin motar, sannan ya faɗa mata kuɗin motar. Cikin rashin kuzari ta cire ta biya, sannan ta shiga motar tana ta doubting akan taje can ɗin ko kuma a'a. Idan taje kaduna gurin wa zata je? Tun da bata taɓa zuwa ba duk da akwai taubashiyar Anty Amarya a can amman bata tunanin zata gane inda take tun da zuwan da duka yi tun da daɗewa ne kuma da motar gida, sunan unguwar ma bata riƙe sosai ba.
ASIM POV
A sale ya fito daga gidan, bama abunda ya fi baƙanta masa rai kamar jiƙa masa tufafi da Namra tayi, Yana ƙoƙari buɗe motarsa ya hango Mardiya tafe, ɗan tsayawa yayi yana kallon takunta, cikin yanga izza take tafiyar dan kuma kawai ta ɗauki hankalinsa ne. Shi kam yasakar mata ido sosai yana kallonta duk da jiƙaƙin tufafin ne a jikinsa, amman hakan be hana shi tsayawa gurun motar ba har ta iso, dan kawai ta ga shine yake tuƙa motar, yasan ko ba komai zai burge ta tun da yasan mata sun fi son mai mota.
Sai da ta kusa ƙarasowa sannan ya buɗe motar ya ciro ƙyale yana goge jikinsa.
“Asim ina kwana?”
Ta gaishe shi cikin kashe murya da ƙarawa muryar zaƙi. Da sauri ya kalleta yana murmushi kamar ba shine ya fito rai a ɓace ba.
“Ah lafiya ƙalau Mardiya ya gidan?”
“Gida ƙalau wallahi miya jiƙa mata kaya haka?”
“To sha'anin ne kin san halin na ku sai a hankali. Gari za a ne?”
“Eh wallahi zan ɗan shiga gra ne”
“Okay shige na aje ki”
“Mashallah ka siye sabon mota ne?”
Ta faɗa tana kallon motar cike da burgewa.
“Eh ai tama kwana biyu, sabuwa dai muke jira”
Buɗewa tayi ta shiga, sai shima ya shiga yana ƙoƙarin tashin motar ta kalli gate ɗin gidansa ta ce
“Kar fa Namra ta hango mu ko a kai mata rahoto”
“Mtsssss amman Mardiya ma kin mai yarda ni wani wawa, ni kam ai nafi ƙarfin matata ba irin mazan nan bane na banza, ashe ke matsoraciyace ba zaki iya kishi da ita ba”
“Ai kishi dabam, da ace yanzu aurna na ne zaka yi to bana shakar taji komai, amman kaga yanzu babu wata magana ta aure dole na ji tsoron irin maganar da zata je mata a kunne”
“To kisa a ranki auren ki zan yi”
Ya faɗa yana ƴar dariya. Itama dariyar tayi mai cike da jindaɗi. Har ya kai ta inda zata je fira suke kamar masu masoya ita kuma sai wani lanƙwashewa take tana karairaya. Daman shi tuni da kasheshi da kalamanta ma.
Daga gra ya wuce gidan Hajiya Sadiya, be same ta a gidan ba hakan ya tabbatar masa da akwai inda taje kenan. Ɗakinsa ya shiga ya canja tufafin jikinsa ya saka waƴan can a washing machine sannan ya dawo ya zauna. Yarinyar ɗazu ce ta faɗo masa a rai a ƙoƙarinsa na kawarda tunanin Namra a ransa dan ganin yake ita babbar maƙiyiyarsa ce, ko kaɗan baya nadamar sakinta da yayi kuma he's ever ready ya mai data idan ta yarda ta zubar da cikin.
Number yarinya ya nemo ya danna mata kira, ringing biyu ta ɗauka ciki muryarta mai sanyi. Cikin turanci ta soma watsa masa tambayar wake kiran shima ya maida mata da yaren da tafi ganewa. Nan da nan ta sake da shi suka gaisa duk kalmar da tayi masa sai ya maida mata, ya ɗan tambaye kaɗan daga rayuwarta, sai da amsa masa a inda abunda take tunanin ya sani. Ya jidaɗin da tace masa ita ƴar Katsina ce, daman ta faɗa masa tun a chat amman a yanzu ne take faɗa masa sunan unguwarsu a Katsina.
Sun daɗe suna waya sannan yayi mata sallama ya kashe wayar. Ko da ya kalli ogagon ɗakinsa ƙarfe biyu saura ya gani, sai ya tashi yaje yayi alwalah yayi salla a cikin gida. Bayan ya sallame zancen gidan ya faɗo masa rai, wai kar dai Namra tace zata sai da gidan ta gudu da kuɗin. Wayarsa ya ɗauka ya aika mata text sannan ya kunna data shi.
HILAL POV
Yana cikin aiki wayarsa tayi ringing. Sai dai be duba mai kiransa ba har sai da ya kai ƙarshen duba marasa lafiyar da yake.
Sai da ya gama da duka katinan da suke gabansa, sannan ya tashi ya nufi office ɗinsa yana duba wayar. Number Dady ya gani Abbah Rashida, yayi mamakin ganin kiran, sai dai be kawo komai a ransa ba dan a tunaninsa, akan maganar shiga kotu ne zai sa ya kira shi tun da monday nan mai zuwa za a shiga.
Sai dai ganin text ɗinsa ya sa gabansa faɗuwa, miyasa yake son ya zo gidansa ya gansa? Duk akan maganar ne ko kuma wani abun daban. Ba tare da shakar komai ba ya shiga office ɗinsa ya cire ƴar samansa ya ɗauki keys ɗinsa ya fice.
Cikin ƴan mintuna ya isa gidan su Rashiida yayi gudu ne a hanya sosai, dan baya son Rafiq ya farka baya kusa. Yana ganin Motar Rashida da ta Dadynta yasan tana cikin gidan.
Be fita cikin motarsa ba har sai da ya kira Dady yace masa gashi ya iso.
“Ka shigo ciki”
Shine reply ɗin da ya masa a wayar cikin tsawa, ko kaɗan Hilal be ɗauki haka a wani abuba dan har gobe yana girmama iyayen Rashida tun da akwai ƴaƴa a tsakaninsu, kuma duk mutumen daya aura maka ƴarsa ya fi gaban ka raina shi ko da kuwa kun rabu da ƴar ne.
Buɗe motar yayi ya fito, yana tuna when last ya shigo gidan nan. Babban falon Dady ya nufa daman ko lokacin da yana surukinsu a can Rashida take sauke shi idan sun zo gidan.
Yana shiga ya samu Dady zaune yana jiran ƙarasowarsa. Momy ma tana zaune daga gefe tana watsa masa harara. Cikin ladabi ya ƙarasa ya zauna saman kujera yana gaishe shi. Dady be amsa ba dan ba gaisuwar ce a gabansa sai kawai ya hau shi da kalamai masu zafi.
“Ma cuce mayaudari, yanzu da kaga ka laƙa mata ciwo shine ka sake ta ko? Ai ni daman nasan sakin da ka yi mata bana Allah ba ne, kaje can kayi yawon ka ka samu cuta kaxo ka laƙa mata”
Ɗaga kai yayi yana kallon Dady maganar ta xo masa a baibai kuma da halshe biyu. Radhida ce ta faɗa musu ko kuma su suka gano haka? Har da shi tace yana ɗauke da cutar ko kuma ita kaɗai?
“Dady zan so Rashida tana nan kamin na yi magana”
“Ta zo ka kunsa mata baƙinciki ko? Ka zo ka ƙaryata ta ka ƙara mata baƙinciki ko? Ɗan iska marar mutumci, wallahi Allah sai ya isar mata”
Idan har Asim ya dawo ya tararda ita a gidan zai zaci ko dan tana son ya mayar da ita ne. Ita kuma yanzu ta yanke ƙauna da shi, idan akwai wanda ta tsana a duniya Asim ne, kuma har gobe bata nadamar zaɓar abunda yake cikinta saman da Asim.
Bayan ta yi sallah azahar ta ɗora da nafili sannan ta rokowa Allah buƙatarta, ta kai masa kukanta ta miƙa masa lamurranta.
Jingina ta yi da ginin gurin tana kuka, da hawaye masu zafi. Irin mutanen da suka yi nemanta aure take tuna amman kowa ya zo tace sai Asim, ayau Asim ɗin ne ya zaɓi rabuwa da ita saboda cikin shi, jininshi.
Tashi tayi ta koma saman katifa ta kwanta, tana kukan zuci wanda ya fili illa da baƙinciki. Wayarta tayi ƙarar saƙo duk da taji daɗin kwanciyar hakan be hanata unƙurawa ta ɗauƙi wayar ta duba ba.
_Karki kuskura cewa za ki siyar da gidan nan, amman na miki lamani ki zauna har ki canja shawara, idan kin yi tunani mai kyau na shirya maida ki a matsayin mata ta!_
“Kaico...”
Shine kawai abunda ta furta bayan ta gama karanta text ɗin ta share hawayenta. Kanta ta ɗaga sama tana kallon ɗakin, kwata-kwata jin tayi gidan ya fita a ranta. Sai dai kuma bata da gurin zuwa, duk inda zata je be yi kamar gidan mahaifinta ba, da ace Abbah ba xai wuƙantata ba, da ba zata damu da maganar mutane ba matuƙar tana gidansu, a ƙarƙashin iyayenta.
Hijabinta ta ɗauka ta saka, ta ɗauki jakarta da wasu ƙaƙanan abubuwa nata ta saka a jakar sannan ta fito, tun da ta baya bq ɗin baya ta sake kallon ta ba har ta fice daga gidan.
Fuskarta ta kumbura sosai haka ma idanunta, duk wanda ya ganta zai san tayi kuka, hakan yasa ta sanda kai ƙasa har ta isa titi. Napep ta tara sai da ta shiga sannan ta soma tunanin inda zai kai ta. Bata da wadataccen kuɗin da zata kama wani gidan ta zauna, kuma ta san ba mutuncin ta ba ne ta kama gida a wani gurin. Kuma bata jin zama a gidan dan zata iya aikata komai saboda baƙinciki.
“Hajiya ina za a kai ki?”
Tsayawa tayi tunani, har tashi Napep ɗin.
“Kai ni tashar mota, inda ake hawa motar sokoto”
“To amman yanzu tashar gov sun tashi sai dai babbar tasha”
Ya hau kan titi yana ƙara ƙure volume ɗin napep ɗin dake tashin wakar Umar m shariff. Ita dai saurare kawai take tana hawaye har suka isa, ɗari biyu ta ciro ta bashi ya miƙa mata canjin naira hansi sannan ta fita shi kuma ya juya.
“Sokoto, Kano, Kaduna, Abuja, jigawa, Kebbi, Zamfara”
Haka ƴan union ɗin suke ta faɗi suna neman passengers. Wasu suka yo kan Namra da gudu suna tambayar ta inda zata ta, tsaye kawai tayi tana tunanin inda zata ce duk da ta zo da niyar zuwa sokoto ne sai kuma ta ji ba zata iya, har tana jin ma kamar ta koma gida...
“Hajiya Kaduna zaki je?”
Wani daga cikin su ya tambaya, sai ta ɗaga masa kai.
“Eh Kaduna zan je”
“Ga mota can daman mutum biyu ake jira, ina kayan ki suke?”
“Bana da kaya”
“Okay muje ga mota can”
Shine yayi mata ja gaba har gurin motar, sannan ya faɗa mata kuɗin motar. Cikin rashin kuzari ta cire ta biya, sannan ta shiga motar tana ta doubting akan taje can ɗin ko kuma a'a. Idan taje kaduna gurin wa zata je? Tun da bata taɓa zuwa ba duk da akwai taubashiyar Anty Amarya a can amman bata tunanin zata gane inda take tun da zuwan da duka yi tun da daɗewa ne kuma da motar gida, sunan unguwar ma bata riƙe sosai ba.
ASIM POV
A sale ya fito daga gidan, bama abunda ya fi baƙanta masa rai kamar jiƙa masa tufafi da Namra tayi, Yana ƙoƙari buɗe motarsa ya hango Mardiya tafe, ɗan tsayawa yayi yana kallon takunta, cikin yanga izza take tafiyar dan kuma kawai ta ɗauki hankalinsa ne. Shi kam yasakar mata ido sosai yana kallonta duk da jiƙaƙin tufafin ne a jikinsa, amman hakan be hana shi tsayawa gurun motar ba har ta iso, dan kawai ta ga shine yake tuƙa motar, yasan ko ba komai zai burge ta tun da yasan mata sun fi son mai mota.
Sai da ta kusa ƙarasowa sannan ya buɗe motar ya ciro ƙyale yana goge jikinsa.
“Asim ina kwana?”
Ta gaishe shi cikin kashe murya da ƙarawa muryar zaƙi. Da sauri ya kalleta yana murmushi kamar ba shine ya fito rai a ɓace ba.
“Ah lafiya ƙalau Mardiya ya gidan?”
“Gida ƙalau wallahi miya jiƙa mata kaya haka?”
“To sha'anin ne kin san halin na ku sai a hankali. Gari za a ne?”
“Eh wallahi zan ɗan shiga gra ne”
“Okay shige na aje ki”
“Mashallah ka siye sabon mota ne?”
Ta faɗa tana kallon motar cike da burgewa.
“Eh ai tama kwana biyu, sabuwa dai muke jira”
Buɗewa tayi ta shiga, sai shima ya shiga yana ƙoƙarin tashin motar ta kalli gate ɗin gidansa ta ce
“Kar fa Namra ta hango mu ko a kai mata rahoto”
“Mtsssss amman Mardiya ma kin mai yarda ni wani wawa, ni kam ai nafi ƙarfin matata ba irin mazan nan bane na banza, ashe ke matsoraciyace ba zaki iya kishi da ita ba”
“Ai kishi dabam, da ace yanzu aurna na ne zaka yi to bana shakar taji komai, amman kaga yanzu babu wata magana ta aure dole na ji tsoron irin maganar da zata je mata a kunne”
“To kisa a ranki auren ki zan yi”
Ya faɗa yana ƴar dariya. Itama dariyar tayi mai cike da jindaɗi. Har ya kai ta inda zata je fira suke kamar masu masoya ita kuma sai wani lanƙwashewa take tana karairaya. Daman shi tuni da kasheshi da kalamanta ma.
Daga gra ya wuce gidan Hajiya Sadiya, be same ta a gidan ba hakan ya tabbatar masa da akwai inda taje kenan. Ɗakinsa ya shiga ya canja tufafin jikinsa ya saka waƴan can a washing machine sannan ya dawo ya zauna. Yarinyar ɗazu ce ta faɗo masa a rai a ƙoƙarinsa na kawarda tunanin Namra a ransa dan ganin yake ita babbar maƙiyiyarsa ce, ko kaɗan baya nadamar sakinta da yayi kuma he's ever ready ya mai data idan ta yarda ta zubar da cikin.
Number yarinya ya nemo ya danna mata kira, ringing biyu ta ɗauka ciki muryarta mai sanyi. Cikin turanci ta soma watsa masa tambayar wake kiran shima ya maida mata da yaren da tafi ganewa. Nan da nan ta sake da shi suka gaisa duk kalmar da tayi masa sai ya maida mata, ya ɗan tambaye kaɗan daga rayuwarta, sai da amsa masa a inda abunda take tunanin ya sani. Ya jidaɗin da tace masa ita ƴar Katsina ce, daman ta faɗa masa tun a chat amman a yanzu ne take faɗa masa sunan unguwarsu a Katsina.
Sun daɗe suna waya sannan yayi mata sallama ya kashe wayar. Ko da ya kalli ogagon ɗakinsa ƙarfe biyu saura ya gani, sai ya tashi yaje yayi alwalah yayi salla a cikin gida. Bayan ya sallame zancen gidan ya faɗo masa rai, wai kar dai Namra tace zata sai da gidan ta gudu da kuɗin. Wayarsa ya ɗauka ya aika mata text sannan ya kunna data shi.
HILAL POV
Yana cikin aiki wayarsa tayi ringing. Sai dai be duba mai kiransa ba har sai da ya kai ƙarshen duba marasa lafiyar da yake.
Sai da ya gama da duka katinan da suke gabansa, sannan ya tashi ya nufi office ɗinsa yana duba wayar. Number Dady ya gani Abbah Rashida, yayi mamakin ganin kiran, sai dai be kawo komai a ransa ba dan a tunaninsa, akan maganar shiga kotu ne zai sa ya kira shi tun da monday nan mai zuwa za a shiga.
Sai dai ganin text ɗinsa ya sa gabansa faɗuwa, miyasa yake son ya zo gidansa ya gansa? Duk akan maganar ne ko kuma wani abun daban. Ba tare da shakar komai ba ya shiga office ɗinsa ya cire ƴar samansa ya ɗauki keys ɗinsa ya fice.
Cikin ƴan mintuna ya isa gidan su Rashiida yayi gudu ne a hanya sosai, dan baya son Rafiq ya farka baya kusa. Yana ganin Motar Rashida da ta Dadynta yasan tana cikin gidan.
Be fita cikin motarsa ba har sai da ya kira Dady yace masa gashi ya iso.
“Ka shigo ciki”
Shine reply ɗin da ya masa a wayar cikin tsawa, ko kaɗan Hilal be ɗauki haka a wani abuba dan har gobe yana girmama iyayen Rashida tun da akwai ƴaƴa a tsakaninsu, kuma duk mutumen daya aura maka ƴarsa ya fi gaban ka raina shi ko da kuwa kun rabu da ƴar ne.
Buɗe motar yayi ya fito, yana tuna when last ya shigo gidan nan. Babban falon Dady ya nufa daman ko lokacin da yana surukinsu a can Rashida take sauke shi idan sun zo gidan.
Yana shiga ya samu Dady zaune yana jiran ƙarasowarsa. Momy ma tana zaune daga gefe tana watsa masa harara. Cikin ladabi ya ƙarasa ya zauna saman kujera yana gaishe shi. Dady be amsa ba dan ba gaisuwar ce a gabansa sai kawai ya hau shi da kalamai masu zafi.
“Ma cuce mayaudari, yanzu da kaga ka laƙa mata ciwo shine ka sake ta ko? Ai ni daman nasan sakin da ka yi mata bana Allah ba ne, kaje can kayi yawon ka ka samu cuta kaxo ka laƙa mata”
Ɗaga kai yayi yana kallon Dady maganar ta xo masa a baibai kuma da halshe biyu. Radhida ce ta faɗa musu ko kuma su suka gano haka? Har da shi tace yana ɗauke da cutar ko kuma ita kaɗai?
“Dady zan so Rashida tana nan kamin na yi magana”
“Ta zo ka kunsa mata baƙinciki ko? Ka zo ka ƙaryata ta ka ƙara mata baƙinciki ko? Ɗan iska marar mutumci, wallahi Allah sai ya isar mata”