Sashe 111
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ya yi kyau lallai Mom tana ji da ƴar nan ta ta”
“Ai dole ta ji da ni, ni kaɗai gare ta, ko ƙawaye na ma Mom son su take balle kuma ni”
“Wow kai lallai ko zata so miji ki ma sosai”
“Sosai ma”
“Gaskiya na yi sa'ah”
“Sa'ah?”
“Eh mana, ai kin san dole Mom ta so ni sosai, to da ni mijin Nably ne right?”
“Uhnn. Yeah”
“Ko dai ban kwanta miki ba ne?”
“Idan baka kwanta min ba, ai ba zan tsaya ina baka lokaci na ba, ni fa ban ma yarda da rayuwar social media ba amman kai lokaci ɗaya ka shiga rai na sosai wallahi”
“Haka nake so kin san ni da gaske na ke yi wallahi auren ki zan yi matuƙar kika amince min”
“Wannan maganar ya kamata sai idan mun haɗu tukuna mu yi ta”
“To na bari gimbiyata”
“Zan duba abu sai na kira ka”
“Okay i love you”
“Thank you”
Daga haka ta katse kiran. Shi kuma ya mannawa wayar kiss zuciyarsa cike da farinciki dan har ga Allah yana ƙaunar Nabila, kuma ita yake fata ta maza matarsa ta biyu.
Wani tsiririn tsaki ya ja lokacin daya isa bakin gate ɗin gidansa, cox he hate one thing buɗe gate, gani yake a yanzu ya kamata ace buɗe masa ake, shi gaba ɗaya gidan ma ya ishe shi, plan ɗinsa a yanzu na samun sabon gida ne mai rai da lafiya, gidan da duk wanda ya kallesa sai yayi magana ba wannan ƙonanne ba.
Sai da ya fito ya buɗewa kansa gate ya shiga da Motar sannan ya dawo ya rufe gate ɗin. Kusa da BQ ya faka motarsa, ya faka motarsa ya buɗe ya fito, daga shigarsa cikin ɗakunan da suke BQ ɗin sai ya fara ya ƙuna fuska, like yana ƙyama, gurin duk ya yi datti kamar be taɓa zama a gurin ba. Da shigarsa ɗakin first thing da ya fara yi ɗauko murhun gawaye da ragowar gawai ɗin da Namra ta bari, ya zuba masa kanazir ɗin da Namra take kunna wuta da shi ya saka kofinta na roba na ƙyasta ashana, nan ta ke wutar ta kama, kamar an saka mata hetur.
Ƙamin tukunyarta ya ɗauka ya ɗauraye ya zuba mata ruwa, ya ɗora saman wutar sannan ya shiga ciki ya ɗauki tsintsina ya share ɗakin tsab kamar mace, ya ruba zuwa yayi mopping, sannan ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul, ya zo ya zube ruwan a roba ya sirka da ruwan sanyi, ya kai ɗaki.
Sai da ya tura kofar ɗakin, sannan ya cire tawul ɗin jikinsa ya zauna cikin robar, kamar wani ƙaramin yaro. Ƙasansa yake gasawa, dan har yanzu zafi yake masa duk da ya sha magani, kuma yana kan sha, amman gurin na masa zafi musamman idan zai duƙa ko kuma zai yi bayan gida.
Sai dai Hajiya ta faɗa masa dan yana sabon shiga ne da ya saba komai ba zai ji ba.
Ya samu kusan minti talatin a cikin ruwa, sannan ya tashi ya ɗaura tawul ɗin ya ɗauki ruwan ya zubar a can waje. Be da mu da ƙorar da tufafinsa na ɗazu suka yi ba, ya ɗauke su a haka ya saka, ya kwanta saman katifa, yana danna wayarsa.
Number Mama ya saka, duk da yana da ita a contact ɗinsa be tsaya nema ba sai kawai ya saka ya danna mata kira.
Ta daɗe tana ringing kamin ta ɗauka tana masa complain
“Ai na ɗauka na manta da ni, ka sake wata uwar”
“Hahha Mama kenan ni na isa duk duniyar nan ai bana da uwa kamar ki”
“Amman Ibrahim ace ko ɗan kiran nan na waya babu, babu aike, babu komai, daga na yi jinyarka ka warke shikenan Namratu ta karɓe min kai?”
“Wallahi Mama kina nan cikin rai na, kawai dai akwai irin da na ke ne, akwai kuɗin da nake jira ina son da na zo zan siya miki gida na nema miki mai aiki, na saka miki komai ba za ki nema ba”
“Ibrahim da gaske?”
“Wallahi Mama”
“Wane irin kuɗi ne wannan? Karka ka jefa kan ka a halaka, garin neman gira a rasa ido, zamani ya lalace tsafi ya yi yawa”
Dariya ya yi dan yasan abunda Mama take tsoro, kamar kar ace tsafi ne a bada ita.
“Ba tsafi na ke ba, kuma ko tsafi na ke ai ba zan bada ke ba, wannan matar data ɗauke ni aiki ce take ba ni kuɗi kuma kullum idan na mata ciniki a shagonta riba uku ake kasawa ita da biyu ni da ɗaya”
“Wane irin sana'ah ne haka?”
“Wayoyi ne mu ke sidawa, da zinari”
“Hahaha Mashallah, ka ga abun Allah ko? Sannu-sannu sai ka fi haka ma, ai ina nan ina maka addu'ah indai kuɗi ne suna nan zuwa”
“A cigaba da yi mana addu'ar nan ai ita cw ke bin mu. Nan da wata ɗaya zan zo gurin ki”
“To Allah ya yarda, ya dafa maka, ɗan Albarka, irin alheri”
Dariya ya yi kana ya ɗora da.
“Zan aiko miki kuɗi ta hanyar Yusufa, zai kawo miki dubu dari da hansi ki riƙe kamin na zo”
“Kai Alhamdulillah Ibrahim Allah ya biya ka yau ɗa na ne yake ba ni wannan kuɗi Allahu akbar...”
Sai kawai ta sa kuka. Shi kuma ya kashe wayar yana dariya, da ganin kuɗin a gare shi yanzu ai ba wani abun ba ne, he past that level, manyan su ma yake hange, he's feeling so high.
KALSOOM POV.
Life goes on yadda take tsammanin rayuwa ba haka ta zo mata ba,tana iya ƙoƙarinta wajen ganin ta kwamtar da hankalinta, 5ana koyar yadda zata yi rayuwa babu abokin rayuwarta, but she can't duk abunda take tunanin sauƙi ne a gareta, sai ta ga ba haka ba.
Duk lokacin da tayi unƙurin danne abunda yake zuciyarta, ta manta da komai, sai ta kasa. Sai yanzu take gane aure rahama ne dan har ta manta da ɗan zaman da tayi na budurci a gidan, sai take ganin kamar yanzu ne ta ke koyon komai, ga maganganun mutane su na ta kai kawo a kunenta, wai ta kashe aurenta ta dawo gida, some people be like daman can irin wayayun ƴan bokon nan basa zaman aure, wasu kuma wai ta kashe ɗan kishiyarta mijin ya sake ta, maganganu dai kala-kala har da na fitar hankali.
Abincin da ta ɗibo ta saka a gaba tana kallo, ta san dai ba iya ci zata yi ba, dan ba ta jin cin komai ga kuma yunwa tana ji, kusan kullum haka take wuni, ta fi son abu mai ruwa sai kuma ɗan furau-furau, wannan abincin ma Momi ce ta cilasta mata ɗibowa wai ko zata iya ci, amman ta kasa.
Ɗaukar abincin ta yi ta nufi falo da shi, da zimmar kai wa kitchen.
“Ba ki ci abincin nan ba ko?”
Cewar Momi da ke zaune saman kujera.
“Wallahi Momi ba na zan iya ci ba”
“Sai yaushe za ki cirewa kan ki damuwar nan ne Ummu?”
“Momi dole na damu, ki duba ko abunda abunda mutanen unguwar nan suke cewa, wai na kore uwar gidana na kashe ɗan ta, ni wallahi da na san haka auren mai mata yake da ban aureshi ba, ni da ma na san haka rayuwar auren ta ke tun farko da ban yi ba”
Ta ƙarasa zancen da kuka. Ajiyar zuciyar Momi ta sauke.
“Na san ba abunda mutane suke cewa ba ne ya fi damun ki, hukuncin da mahaifin ki ya yanke ne ya hana ki sakewa, ina son ki san be yi hakan dan ya cutar da ke ba, sai dan nema miki yanci, ba wai dan ya shiga tsakanin ki da Hilal ba”
Hawayen idonta ta share, ta aje plate ta zauna.
“Ba wai rai na ya ɓace ba ne da hukuncin Dady ,kawai abun yana damu na ne, duk duk yaushe na yi auren nan yanzu ace har na dawo gida, a can gidan auren ma ba wani daɗi na ji ba, matar nan ta hana ni sakewa, ta bi ta fitine ni bayan fitar ta kuma kishi ya koma tsakanin ni da ƴarta, wallahi yaron nan ban san lokacin da ƴa ci guba ba, amman sun ce ni ce na kashe shi, da wanne zan ji? Ga shi mahaifiyarsa ta sa ya sake ni na dawo gida kuma mutanen unguwa sun ɗasa na su gulmar, dole na yi damuwa”
Da kuka ta ƙarasa maganar tana rufe fuskarta. Momy taja wani dogon numfashi ta sauke tana kallon ƴarta cike da damuwa.
“Allah zai saka miki ai zalumci baya ɗorewa, gaskiya zata bayyana sakamakin ki zai fito, kawai ki cigaba da addu'ah kina faɗawa Allah buƙatar ki, zai yaye miki komai”
Kuka ta yi sosai, sannan t tashi ta nufi kitchen ta aje plate ɗin ta fito.
“Ko za ki je gidansu gidan Salma ki ɗan yi fira ko zaki rage damuwa”
Da to kawai ta amsa ma Momi ta nufi bedroom ɗin ta, fuskarta ta fara wankewa sannan ta ɗauki hijabi ta saka ta ɗauki jakarta, ta fito.
“Na tafi”
Ta faɗa murya can ciki.
“Sai kin dawo ina a gaishe ta”
A hankali ta fito daga gidan, tana.fitowa gate ta yi sa'ar samun Napep kasanceqar an sauke wata ne gidan da ke kusa d na su, tara kawai ta yi ta shiga tana faɗa masa ind zai kai ta.
“Sauke ni a nan”
Ta faɗa tun kamin ya ƙaraso kusa da gidan Salma. Naira ɗari ta miƙa mas sannan ta fita daga napep ɗin ta ƙars da ƙafa.
Tun da ta hango gate ɗin buɗe ta fahimci Salma zata fita ne.
A hankali take tafiya har ta ƙarasa harabar gidan. Lokacin da ta isa ƙofar falon si t ki hannu zta buɗe sai ga Mijin Salma ta buɗe ya fito. Ja ta yi da baya tana ƙirƙiro murmushi, tare da gaishe shi, shi kuma ya amsa mata yana gyara hular kansa.
“Lafiya ƙalau Kalsoom ce a gidan na mu!”
“Eh wallahi yau na ce bari na leƙo Salma ne”
“Ayyah gashi bata gida Wallahi ta je suna”
Juyawa ta yi tana faɗin
“Okay idan ta zo a gaishe ta”
“Wuce wa za ki yi?”
“Eh”
“Ai dole ta ji da ni, ni kaɗai gare ta, ko ƙawaye na ma Mom son su take balle kuma ni”
“Wow kai lallai ko zata so miji ki ma sosai”
“Sosai ma”
“Gaskiya na yi sa'ah”
“Sa'ah?”
“Eh mana, ai kin san dole Mom ta so ni sosai, to da ni mijin Nably ne right?”
“Uhnn. Yeah”
“Ko dai ban kwanta miki ba ne?”
“Idan baka kwanta min ba, ai ba zan tsaya ina baka lokaci na ba, ni fa ban ma yarda da rayuwar social media ba amman kai lokaci ɗaya ka shiga rai na sosai wallahi”
“Haka nake so kin san ni da gaske na ke yi wallahi auren ki zan yi matuƙar kika amince min”
“Wannan maganar ya kamata sai idan mun haɗu tukuna mu yi ta”
“To na bari gimbiyata”
“Zan duba abu sai na kira ka”
“Okay i love you”
“Thank you”
Daga haka ta katse kiran. Shi kuma ya mannawa wayar kiss zuciyarsa cike da farinciki dan har ga Allah yana ƙaunar Nabila, kuma ita yake fata ta maza matarsa ta biyu.
Wani tsiririn tsaki ya ja lokacin daya isa bakin gate ɗin gidansa, cox he hate one thing buɗe gate, gani yake a yanzu ya kamata ace buɗe masa ake, shi gaba ɗaya gidan ma ya ishe shi, plan ɗinsa a yanzu na samun sabon gida ne mai rai da lafiya, gidan da duk wanda ya kallesa sai yayi magana ba wannan ƙonanne ba.
Sai da ya fito ya buɗewa kansa gate ya shiga da Motar sannan ya dawo ya rufe gate ɗin. Kusa da BQ ya faka motarsa, ya faka motarsa ya buɗe ya fito, daga shigarsa cikin ɗakunan da suke BQ ɗin sai ya fara ya ƙuna fuska, like yana ƙyama, gurin duk ya yi datti kamar be taɓa zama a gurin ba. Da shigarsa ɗakin first thing da ya fara yi ɗauko murhun gawaye da ragowar gawai ɗin da Namra ta bari, ya zuba masa kanazir ɗin da Namra take kunna wuta da shi ya saka kofinta na roba na ƙyasta ashana, nan ta ke wutar ta kama, kamar an saka mata hetur.
Ƙamin tukunyarta ya ɗauka ya ɗauraye ya zuba mata ruwa, ya ɗora saman wutar sannan ya shiga ciki ya ɗauki tsintsina ya share ɗakin tsab kamar mace, ya ruba zuwa yayi mopping, sannan ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul, ya zo ya zube ruwan a roba ya sirka da ruwan sanyi, ya kai ɗaki.
Sai da ya tura kofar ɗakin, sannan ya cire tawul ɗin jikinsa ya zauna cikin robar, kamar wani ƙaramin yaro. Ƙasansa yake gasawa, dan har yanzu zafi yake masa duk da ya sha magani, kuma yana kan sha, amman gurin na masa zafi musamman idan zai duƙa ko kuma zai yi bayan gida.
Sai dai Hajiya ta faɗa masa dan yana sabon shiga ne da ya saba komai ba zai ji ba.
Ya samu kusan minti talatin a cikin ruwa, sannan ya tashi ya ɗaura tawul ɗin ya ɗauki ruwan ya zubar a can waje. Be da mu da ƙorar da tufafinsa na ɗazu suka yi ba, ya ɗauke su a haka ya saka, ya kwanta saman katifa, yana danna wayarsa.
Number Mama ya saka, duk da yana da ita a contact ɗinsa be tsaya nema ba sai kawai ya saka ya danna mata kira.
Ta daɗe tana ringing kamin ta ɗauka tana masa complain
“Ai na ɗauka na manta da ni, ka sake wata uwar”
“Hahha Mama kenan ni na isa duk duniyar nan ai bana da uwa kamar ki”
“Amman Ibrahim ace ko ɗan kiran nan na waya babu, babu aike, babu komai, daga na yi jinyarka ka warke shikenan Namratu ta karɓe min kai?”
“Wallahi Mama kina nan cikin rai na, kawai dai akwai irin da na ke ne, akwai kuɗin da nake jira ina son da na zo zan siya miki gida na nema miki mai aiki, na saka miki komai ba za ki nema ba”
“Ibrahim da gaske?”
“Wallahi Mama”
“Wane irin kuɗi ne wannan? Karka ka jefa kan ka a halaka, garin neman gira a rasa ido, zamani ya lalace tsafi ya yi yawa”
Dariya ya yi dan yasan abunda Mama take tsoro, kamar kar ace tsafi ne a bada ita.
“Ba tsafi na ke ba, kuma ko tsafi na ke ai ba zan bada ke ba, wannan matar data ɗauke ni aiki ce take ba ni kuɗi kuma kullum idan na mata ciniki a shagonta riba uku ake kasawa ita da biyu ni da ɗaya”
“Wane irin sana'ah ne haka?”
“Wayoyi ne mu ke sidawa, da zinari”
“Hahaha Mashallah, ka ga abun Allah ko? Sannu-sannu sai ka fi haka ma, ai ina nan ina maka addu'ah indai kuɗi ne suna nan zuwa”
“A cigaba da yi mana addu'ar nan ai ita cw ke bin mu. Nan da wata ɗaya zan zo gurin ki”
“To Allah ya yarda, ya dafa maka, ɗan Albarka, irin alheri”
Dariya ya yi kana ya ɗora da.
“Zan aiko miki kuɗi ta hanyar Yusufa, zai kawo miki dubu dari da hansi ki riƙe kamin na zo”
“Kai Alhamdulillah Ibrahim Allah ya biya ka yau ɗa na ne yake ba ni wannan kuɗi Allahu akbar...”
Sai kawai ta sa kuka. Shi kuma ya kashe wayar yana dariya, da ganin kuɗin a gare shi yanzu ai ba wani abun ba ne, he past that level, manyan su ma yake hange, he's feeling so high.
KALSOOM POV.
Life goes on yadda take tsammanin rayuwa ba haka ta zo mata ba,tana iya ƙoƙarinta wajen ganin ta kwamtar da hankalinta, 5ana koyar yadda zata yi rayuwa babu abokin rayuwarta, but she can't duk abunda take tunanin sauƙi ne a gareta, sai ta ga ba haka ba.
Duk lokacin da tayi unƙurin danne abunda yake zuciyarta, ta manta da komai, sai ta kasa. Sai yanzu take gane aure rahama ne dan har ta manta da ɗan zaman da tayi na budurci a gidan, sai take ganin kamar yanzu ne ta ke koyon komai, ga maganganun mutane su na ta kai kawo a kunenta, wai ta kashe aurenta ta dawo gida, some people be like daman can irin wayayun ƴan bokon nan basa zaman aure, wasu kuma wai ta kashe ɗan kishiyarta mijin ya sake ta, maganganu dai kala-kala har da na fitar hankali.
Abincin da ta ɗibo ta saka a gaba tana kallo, ta san dai ba iya ci zata yi ba, dan ba ta jin cin komai ga kuma yunwa tana ji, kusan kullum haka take wuni, ta fi son abu mai ruwa sai kuma ɗan furau-furau, wannan abincin ma Momi ce ta cilasta mata ɗibowa wai ko zata iya ci, amman ta kasa.
Ɗaukar abincin ta yi ta nufi falo da shi, da zimmar kai wa kitchen.
“Ba ki ci abincin nan ba ko?”
Cewar Momi da ke zaune saman kujera.
“Wallahi Momi ba na zan iya ci ba”
“Sai yaushe za ki cirewa kan ki damuwar nan ne Ummu?”
“Momi dole na damu, ki duba ko abunda abunda mutanen unguwar nan suke cewa, wai na kore uwar gidana na kashe ɗan ta, ni wallahi da na san haka auren mai mata yake da ban aureshi ba, ni da ma na san haka rayuwar auren ta ke tun farko da ban yi ba”
Ta ƙarasa zancen da kuka. Ajiyar zuciyar Momi ta sauke.
“Na san ba abunda mutane suke cewa ba ne ya fi damun ki, hukuncin da mahaifin ki ya yanke ne ya hana ki sakewa, ina son ki san be yi hakan dan ya cutar da ke ba, sai dan nema miki yanci, ba wai dan ya shiga tsakanin ki da Hilal ba”
Hawayen idonta ta share, ta aje plate ta zauna.
“Ba wai rai na ya ɓace ba ne da hukuncin Dady ,kawai abun yana damu na ne, duk duk yaushe na yi auren nan yanzu ace har na dawo gida, a can gidan auren ma ba wani daɗi na ji ba, matar nan ta hana ni sakewa, ta bi ta fitine ni bayan fitar ta kuma kishi ya koma tsakanin ni da ƴarta, wallahi yaron nan ban san lokacin da ƴa ci guba ba, amman sun ce ni ce na kashe shi, da wanne zan ji? Ga shi mahaifiyarsa ta sa ya sake ni na dawo gida kuma mutanen unguwa sun ɗasa na su gulmar, dole na yi damuwa”
Da kuka ta ƙarasa maganar tana rufe fuskarta. Momy taja wani dogon numfashi ta sauke tana kallon ƴarta cike da damuwa.
“Allah zai saka miki ai zalumci baya ɗorewa, gaskiya zata bayyana sakamakin ki zai fito, kawai ki cigaba da addu'ah kina faɗawa Allah buƙatar ki, zai yaye miki komai”
Kuka ta yi sosai, sannan t tashi ta nufi kitchen ta aje plate ɗin ta fito.
“Ko za ki je gidansu gidan Salma ki ɗan yi fira ko zaki rage damuwa”
Da to kawai ta amsa ma Momi ta nufi bedroom ɗin ta, fuskarta ta fara wankewa sannan ta ɗauki hijabi ta saka ta ɗauki jakarta, ta fito.
“Na tafi”
Ta faɗa murya can ciki.
“Sai kin dawo ina a gaishe ta”
A hankali ta fito daga gidan, tana.fitowa gate ta yi sa'ar samun Napep kasanceqar an sauke wata ne gidan da ke kusa d na su, tara kawai ta yi ta shiga tana faɗa masa ind zai kai ta.
“Sauke ni a nan”
Ta faɗa tun kamin ya ƙaraso kusa da gidan Salma. Naira ɗari ta miƙa mas sannan ta fita daga napep ɗin ta ƙars da ƙafa.
Tun da ta hango gate ɗin buɗe ta fahimci Salma zata fita ne.
A hankali take tafiya har ta ƙarasa harabar gidan. Lokacin da ta isa ƙofar falon si t ki hannu zta buɗe sai ga Mijin Salma ta buɗe ya fito. Ja ta yi da baya tana ƙirƙiro murmushi, tare da gaishe shi, shi kuma ya amsa mata yana gyara hular kansa.
“Lafiya ƙalau Kalsoom ce a gidan na mu!”
“Eh wallahi yau na ce bari na leƙo Salma ne”
“Ayyah gashi bata gida Wallahi ta je suna”
Juyawa ta yi tana faɗin
“Okay idan ta zo a gaishe ta”
“Wuce wa za ki yi?”
“Eh”