Sashe 92
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani abu taji ya tsaya mata a ƙahon zuciya ya yana numfashinta tafiya dai-dai har tayi salla asuba. Haƙiƙa wanda Halal be wadata shi ba, to Haram ba zai wadatar da shi ba, ko da kuwa ya wadatar da to ya aure shi ne na ɗan wani lokaci ya sake shi, a lokacin ne zai gane illar abinda ya aikata. Zina ya zama ruwan dare yanzu babu matan aure babu budare, an maida abun ado, wasu har gobe suna cin ribar abun saboda Allah yayi musu istijira'i na ɗan wani lokaci, kamin su haɗu da shi, wasu kuma tun a duniya Allah zai bayyana su. Da yawa sun ɗauko ƴaƴan da bana miji ba an kawo ciki gida walau ta gurin bin bokaye ko kuma ta gurin aiki ko abokan banza, shiyasa zaka ga yara suna kashe iyayensu ko kuna musguna musu ko suna wani abu da bae dace ba, wanda abu ne mai wahala ɗan halak ya aikata haka. A social media ma yanzu zina ake macen aure ta kawo wanda ba muharraminta ba gidan mijin ta,, gidanta na sunna, har ta jashi su aikata alfasha. Wasu akan yi musu lamani kaɗan, wasu kuma da yawa, sai dai babban tashin hankali gurin haɗuwa da Ubangijin ka...!
Sai a yanzu ta soma nadamar abunda ta aikata, sai dai nadamar bata yi tasirin yanke kuɗirin dake zuciyarta ba, na komawa gidan Hilal, ta yarda asirinta ya tonu amman a gidan Hilal, ta yarda ta kauce dukan hanyar da zata kauce inda har zata koma a gidan Hilal.
Bayan ta yi wanka ta shirya cikin atamfa pink color ta ɗauki mayafinta ta yafa sannan ta ɗauki handbag ɗinta, bata tsaya karyawa ba ta fice, daman ko ta tsaya ba zata iya cin komai ba. Kai tsaye gidansu Teema ta nufa ita kanta tayi mamakin sammakon data dako mata tun da safe, sai ta shirya ta karya sannan Teema ta faɗawa Iyayenta wai zata raka Rashida gidan Rasuwa, sannan suka fita.
Rashida take driving Teema na nuna mata hanya har suka isa garin ɗan-ƙane, cikin dajin suka kai kutsawa har suka isa gidan mutumen. Wannan kan ba'a kira sa da malam ba sai dai boka, dan babu komai a jikinsa sai walki da fatu, irin arnanan ne na kaduna masara imani waɗanda zasu iya aikata komai ba tare da fargaba ba.
Sun tarar mutane da dama, cikin har da ƴan siyasar da Rashida ta sansu, da kuma wasu matan manya, inda Allah ya taimake ta ta saka niƙab ba kowa ne zai gane ta ba.
Sai da mutane da ke gabasu suka gama shiga, sannan suka shiga a lokacin sun cin ma layi.
Irin kayan tsafe-tsafen da ta gani yasa gabanta faɗuwa, har da wani ƙaton madubi baƙi an masa rubutun larabci da jan jini. Cikin fargaba da tsoro ta zauna gaban bokan tana kallon walkin dake jikinsa.
Zata fara bayani ya ɗaga nata hannu.
“Bana buƙatar ki faɗa min komai, ni zan baki labarin duniyarki, sai dai idan baki son kowa ya ji zamu iya sallamar ƙawarki”
Ta jidaɗin maganarsa dan har ga Allah bata son Teema ta ji sirrinta, dan daga ganin wannan mutumen ba zai ɓoye komai ba.
Ba tare da tace ba, Teema ta tashi ta bar mata ɗakin.
Shi wannan bokan da jini yake duba a maimaikon ƙasa da wasu suke yi da ita, sai da yayi rubuce-rubucensa sannan ya dubeta ya ce
“Auren ki ya mutu, saboda mijin ya gano kina ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki, kin yi asiri wa kishiryar ki da take gidan mijinki ya faɗawa ɗan ki! Wata ƴar'uwarki na daf da shirya miki wani abu, akwai yiyuwar ki koma gidan mijinki amman idan har kin yarda ki daina salla azahar na tsawon sati ɗaya, tabbas buƙatar zata biya, idan har kika zake jefar abokiyar zaman ki to buƙatar ki zata biya zaki same ta, amman akwai yiyuwar jifar ta dawo kan ki, haƙiƙa baƙin duhu yana bibiyarki, wannan baƙin duhun baƙar rana ce...!”
Da sauri Rashida ta miƙe tsaye tayi baya-baya tana kallonsa tashin hankali ƙarara a fuskarta. Bata iya ce masa komai ba ta fice daga ɗakin kamar wacce ta ruɗe. Tana fitowa hannun Teema kawai ta kama ta jata tana hawaye suka fice daga gurin. Teema na tambayar lafiya amman Rashida bata tsaya faɗa mata komai ba, ta shiga motar tayi mata key ganin hakan yasa Teema ta shiga gidan gaba, kamar za su tashi sama haka Rashida ta riƙa tuƙin motar suna ratsa dajin, har sai da Teema ta riƙa ta tana girgizawa, sannan ta dawo hayyacinta har ta rage gudun ta faka gefen titi tana kuka.
*ABDOOL POV.*
Satinsa biyu a kaduna, kusan kullum sai Amira ta tura masa saƙon barka da safiya da dare ma haka, sai dai har yanzu be taɓa mata reply ba, shi kan ba ma ita ce gabansa ba. Kusan kullum sai yayi waya da Ummi kamar yadda ya saba, ya maida hankali akn aikinsa sosai dan aiki ne mai muhimmanci.
Yau kam be kira Ummi da safe ba har sai da ya shiga office, yana shirin kiranta sai gata ta kira shi. Da sauri ya ɗauka Cikin jindaɗin kiran na mahaifiyarsa
“Ummi na ta kai na good morning”
“How are you?”
“Im fine i miss you, na ga nawa satin nan ya zo na zo gida na ganki”
“Nima ai ina son ka zo akwai maganar da zamu yi da kai”
“Wace magana ce?”
“Idan ka zo zaka ji, akwai kayan da nayi oda daga paris za su iso Lagos jibi, zan tura maka address ɗin sai ka aika a karɓo min”
“Yes Ma'am”
Dariya tayi ta kashe wayar shima ya sauke yana murmushi cike da ƙaunar mahaifiyarsa.
Ɗayan ɓangaren kuma yana jin rashin daɗin maganar da tayi ma mai martaba na cewar yace a nema masa mata, sai dai babu yadda ya iya tun da shi kansa ya san yana buƙatar auren a yanzu, idan be yi ba a yanzu sai yaushe, lokaci tafiya yake baya jiran kowa, kuma shi har yanzu be da wacce zai iya fitarwa a matsayin matar aurensa.
Sai dai shi kuma ya sha alwashin aurar da duka ƙanensa dan ba zai yarda Ummi ta riƙa matsa masa ba bayan ga ƙanensa mata nan duk sun isa aure.
*Ummi*
Tana gama waya da shi, sai ga Amira ta shigo da sallama cikin ladabi, already ta gaishe da Ummi da safe so bata buƙatar repetitive, sai kawai tace
“Ummi me za a girka na rana?”
“Ayi mana mana miyar kuɓewa sai Shukura tayi tuwon semo”
“Tau”
Ta miƙe tsaye ta fice cikin tsantsar ladabin nan. Bata kira Shukura ba da kanta tayi tuwon semo miyar kuɓuwa sannan kuma tayi miyar agusi dan kawai ta burge su. Ko da azahar tayi har ta gama komai ta jera a dinning sannan ta shiga tayi wanka.
A lokacin ne su Amal suka dawo makaranta tare da Haleema, daman yau Meesha bata je ba, dan su da lacca. Fauza ce kawai ta tafi sai Haleema.
A ɗaki suka samu Ummi da Meesha suna duba wasu atamfofi da aka turo ta whatsapp. Jikin Ummi Amal ta faɗa tana zuba shagwaɓa wai ita ala dole ga auta.
“Ummi yunwa”
“Ai ga abinci can ana gama”
“Me aka girka”
Haleema ta tambaya tana zaunawa kusa da Meesha.
“Tuwon semu miyar kuɓewa”
“Ɓi bana so, sai dai ki girka min makaroni”
“Kai Amal kin cika son rigima wallahi, miyar tayi daɗi fa”
“Wa yayi? Wannan Amira ko”
“Eh miya har kala biyu tayi”
.“Ni bana so bata iya komai ba sai ƙazanta”
Haleema ta buge mata baki
“Data saba girkawa kina ci fa? Wai Amal miyasa baki da kunya, ke uban kowa kin raina, Amirar nan aiki da take ko da muke cikin gida albarka, tana ƙoƙari sosai wallahi”
“Ta riga ta saba wahalar ne tun gidansu, maybe talakawa ne”
Cewar Meesha, tana taba eyebrows.
“Ba wani sabo wallahi kawai dai tana da mutunci ne, kuma gani nake kamar Big bros take so, dama an haɗa su wlh dan zata kula da shi”
Meesha ta tofarda yawu
“Tuuu Allah kiyaye big Bros da wannan yarinyar amman wallahi Haleema baki da hankali zuwa makaranta be amfane ki ba, daga ganin yarinya an taimaka mata ki ce wai ta auri yayanki, ke anya kina son yaya kuwa? Ke nifa ban ma yarda da yarinyar nan ba, tsantsan ɗinta yayi ta cika shige mana jiki, waya sani ko cutar mu ta zo tayi”
Amal ta haye saman gadon Ummi tana hararar Haleema.
“Sai na gayawa Dude, mu mana son ta”
Ummi ta kama kunne Amal.
“Bana raba ki da yi ma manya rashin kunya ba?”
“Ooo Ummi it hurt”
Ta riƙe kunne, tana son kuka. Haleema yaja wani dogon tsaki
“Ke kin wuce shiga halin da ta shiga ne hala? Idan Allah ya tubuta shine mijinta ya zaki yi?”
Ummi ta kalle ta kallo da babu wasa a fuskarta.
“Ke Haleema ki daina wannan maganar, yarinya daga taimako sai kuma neman wuce gurin tana da tarbiya zata bar gaban iyayenta ana neman ta koma bata so sannan ki ce ta auri ɗan'uwanki dan baki da tunani? Kin san iya zaman da ta yi taraiya da su? Wanda yayi maka hallaci ya cancanci hallaci shiyasa take zaune tare da mu, amman nan gaba kan gurin iyayenta zan maida ta, Allah ya bata miji na gari”
“Amman Ummi ta mana hallaci wallahi, kuma idan ba a barta ta auri Yaya kamar ba a mata hallaci ba”
Meesha ta zungureta
“Ai ke sai ki mata hallaci ko? Yayan manya ma Big Bros be so ba sai ita yarinyar data ƴan fashi, ashe za'a iya haɗa kai da ke ayi ma masa wani mugun abu, haka kawai daga ganin yarinya ki ce a haɗa su amman baki da hankali Haleema”
“Ke da kika da shi ai sai ki ara min na saka, ko ita ba mutum bace? Ke idan kina so wani ya zaki ji”
“Ba zan so wanda ya fi ƙarfina ba balle har na damu, ke daga ganin ajin Yaya kin san yafi ƙarfin Amira wallahi, yarinyar data gama bada kanta ga mazan banza sai kuma ta dawo yaya ya aureta, ai abun kunya ma ne wallahi”
Sai a yanzu ta soma nadamar abunda ta aikata, sai dai nadamar bata yi tasirin yanke kuɗirin dake zuciyarta ba, na komawa gidan Hilal, ta yarda asirinta ya tonu amman a gidan Hilal, ta yarda ta kauce dukan hanyar da zata kauce inda har zata koma a gidan Hilal.
Bayan ta yi wanka ta shirya cikin atamfa pink color ta ɗauki mayafinta ta yafa sannan ta ɗauki handbag ɗinta, bata tsaya karyawa ba ta fice, daman ko ta tsaya ba zata iya cin komai ba. Kai tsaye gidansu Teema ta nufa ita kanta tayi mamakin sammakon data dako mata tun da safe, sai ta shirya ta karya sannan Teema ta faɗawa Iyayenta wai zata raka Rashida gidan Rasuwa, sannan suka fita.
Rashida take driving Teema na nuna mata hanya har suka isa garin ɗan-ƙane, cikin dajin suka kai kutsawa har suka isa gidan mutumen. Wannan kan ba'a kira sa da malam ba sai dai boka, dan babu komai a jikinsa sai walki da fatu, irin arnanan ne na kaduna masara imani waɗanda zasu iya aikata komai ba tare da fargaba ba.
Sun tarar mutane da dama, cikin har da ƴan siyasar da Rashida ta sansu, da kuma wasu matan manya, inda Allah ya taimake ta ta saka niƙab ba kowa ne zai gane ta ba.
Sai da mutane da ke gabasu suka gama shiga, sannan suka shiga a lokacin sun cin ma layi.
Irin kayan tsafe-tsafen da ta gani yasa gabanta faɗuwa, har da wani ƙaton madubi baƙi an masa rubutun larabci da jan jini. Cikin fargaba da tsoro ta zauna gaban bokan tana kallon walkin dake jikinsa.
Zata fara bayani ya ɗaga nata hannu.
“Bana buƙatar ki faɗa min komai, ni zan baki labarin duniyarki, sai dai idan baki son kowa ya ji zamu iya sallamar ƙawarki”
Ta jidaɗin maganarsa dan har ga Allah bata son Teema ta ji sirrinta, dan daga ganin wannan mutumen ba zai ɓoye komai ba.
Ba tare da tace ba, Teema ta tashi ta bar mata ɗakin.
Shi wannan bokan da jini yake duba a maimaikon ƙasa da wasu suke yi da ita, sai da yayi rubuce-rubucensa sannan ya dubeta ya ce
“Auren ki ya mutu, saboda mijin ya gano kina ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki, kin yi asiri wa kishiryar ki da take gidan mijinki ya faɗawa ɗan ki! Wata ƴar'uwarki na daf da shirya miki wani abu, akwai yiyuwar ki koma gidan mijinki amman idan har kin yarda ki daina salla azahar na tsawon sati ɗaya, tabbas buƙatar zata biya, idan har kika zake jefar abokiyar zaman ki to buƙatar ki zata biya zaki same ta, amman akwai yiyuwar jifar ta dawo kan ki, haƙiƙa baƙin duhu yana bibiyarki, wannan baƙin duhun baƙar rana ce...!”
Da sauri Rashida ta miƙe tsaye tayi baya-baya tana kallonsa tashin hankali ƙarara a fuskarta. Bata iya ce masa komai ba ta fice daga ɗakin kamar wacce ta ruɗe. Tana fitowa hannun Teema kawai ta kama ta jata tana hawaye suka fice daga gurin. Teema na tambayar lafiya amman Rashida bata tsaya faɗa mata komai ba, ta shiga motar tayi mata key ganin hakan yasa Teema ta shiga gidan gaba, kamar za su tashi sama haka Rashida ta riƙa tuƙin motar suna ratsa dajin, har sai da Teema ta riƙa ta tana girgizawa, sannan ta dawo hayyacinta har ta rage gudun ta faka gefen titi tana kuka.
*ABDOOL POV.*
Satinsa biyu a kaduna, kusan kullum sai Amira ta tura masa saƙon barka da safiya da dare ma haka, sai dai har yanzu be taɓa mata reply ba, shi kan ba ma ita ce gabansa ba. Kusan kullum sai yayi waya da Ummi kamar yadda ya saba, ya maida hankali akn aikinsa sosai dan aiki ne mai muhimmanci.
Yau kam be kira Ummi da safe ba har sai da ya shiga office, yana shirin kiranta sai gata ta kira shi. Da sauri ya ɗauka Cikin jindaɗin kiran na mahaifiyarsa
“Ummi na ta kai na good morning”
“How are you?”
“Im fine i miss you, na ga nawa satin nan ya zo na zo gida na ganki”
“Nima ai ina son ka zo akwai maganar da zamu yi da kai”
“Wace magana ce?”
“Idan ka zo zaka ji, akwai kayan da nayi oda daga paris za su iso Lagos jibi, zan tura maka address ɗin sai ka aika a karɓo min”
“Yes Ma'am”
Dariya tayi ta kashe wayar shima ya sauke yana murmushi cike da ƙaunar mahaifiyarsa.
Ɗayan ɓangaren kuma yana jin rashin daɗin maganar da tayi ma mai martaba na cewar yace a nema masa mata, sai dai babu yadda ya iya tun da shi kansa ya san yana buƙatar auren a yanzu, idan be yi ba a yanzu sai yaushe, lokaci tafiya yake baya jiran kowa, kuma shi har yanzu be da wacce zai iya fitarwa a matsayin matar aurensa.
Sai dai shi kuma ya sha alwashin aurar da duka ƙanensa dan ba zai yarda Ummi ta riƙa matsa masa ba bayan ga ƙanensa mata nan duk sun isa aure.
*Ummi*
Tana gama waya da shi, sai ga Amira ta shigo da sallama cikin ladabi, already ta gaishe da Ummi da safe so bata buƙatar repetitive, sai kawai tace
“Ummi me za a girka na rana?”
“Ayi mana mana miyar kuɓewa sai Shukura tayi tuwon semo”
“Tau”
Ta miƙe tsaye ta fice cikin tsantsar ladabin nan. Bata kira Shukura ba da kanta tayi tuwon semo miyar kuɓuwa sannan kuma tayi miyar agusi dan kawai ta burge su. Ko da azahar tayi har ta gama komai ta jera a dinning sannan ta shiga tayi wanka.
A lokacin ne su Amal suka dawo makaranta tare da Haleema, daman yau Meesha bata je ba, dan su da lacca. Fauza ce kawai ta tafi sai Haleema.
A ɗaki suka samu Ummi da Meesha suna duba wasu atamfofi da aka turo ta whatsapp. Jikin Ummi Amal ta faɗa tana zuba shagwaɓa wai ita ala dole ga auta.
“Ummi yunwa”
“Ai ga abinci can ana gama”
“Me aka girka”
Haleema ta tambaya tana zaunawa kusa da Meesha.
“Tuwon semu miyar kuɓewa”
“Ɓi bana so, sai dai ki girka min makaroni”
“Kai Amal kin cika son rigima wallahi, miyar tayi daɗi fa”
“Wa yayi? Wannan Amira ko”
“Eh miya har kala biyu tayi”
.“Ni bana so bata iya komai ba sai ƙazanta”
Haleema ta buge mata baki
“Data saba girkawa kina ci fa? Wai Amal miyasa baki da kunya, ke uban kowa kin raina, Amirar nan aiki da take ko da muke cikin gida albarka, tana ƙoƙari sosai wallahi”
“Ta riga ta saba wahalar ne tun gidansu, maybe talakawa ne”
Cewar Meesha, tana taba eyebrows.
“Ba wani sabo wallahi kawai dai tana da mutunci ne, kuma gani nake kamar Big bros take so, dama an haɗa su wlh dan zata kula da shi”
Meesha ta tofarda yawu
“Tuuu Allah kiyaye big Bros da wannan yarinyar amman wallahi Haleema baki da hankali zuwa makaranta be amfane ki ba, daga ganin yarinya an taimaka mata ki ce wai ta auri yayanki, ke anya kina son yaya kuwa? Ke nifa ban ma yarda da yarinyar nan ba, tsantsan ɗinta yayi ta cika shige mana jiki, waya sani ko cutar mu ta zo tayi”
Amal ta haye saman gadon Ummi tana hararar Haleema.
“Sai na gayawa Dude, mu mana son ta”
Ummi ta kama kunne Amal.
“Bana raba ki da yi ma manya rashin kunya ba?”
“Ooo Ummi it hurt”
Ta riƙe kunne, tana son kuka. Haleema yaja wani dogon tsaki
“Ke kin wuce shiga halin da ta shiga ne hala? Idan Allah ya tubuta shine mijinta ya zaki yi?”
Ummi ta kalle ta kallo da babu wasa a fuskarta.
“Ke Haleema ki daina wannan maganar, yarinya daga taimako sai kuma neman wuce gurin tana da tarbiya zata bar gaban iyayenta ana neman ta koma bata so sannan ki ce ta auri ɗan'uwanki dan baki da tunani? Kin san iya zaman da ta yi taraiya da su? Wanda yayi maka hallaci ya cancanci hallaci shiyasa take zaune tare da mu, amman nan gaba kan gurin iyayenta zan maida ta, Allah ya bata miji na gari”
“Amman Ummi ta mana hallaci wallahi, kuma idan ba a barta ta auri Yaya kamar ba a mata hallaci ba”
Meesha ta zungureta
“Ai ke sai ki mata hallaci ko? Yayan manya ma Big Bros be so ba sai ita yarinyar data ƴan fashi, ashe za'a iya haɗa kai da ke ayi ma masa wani mugun abu, haka kawai daga ganin yarinya ki ce a haɗa su amman baki da hankali Haleema”
“Ke da kika da shi ai sai ki ara min na saka, ko ita ba mutum bace? Ke idan kina so wani ya zaki ji”
“Ba zan so wanda ya fi ƙarfina ba balle har na damu, ke daga ganin ajin Yaya kin san yafi ƙarfin Amira wallahi, yarinyar data gama bada kanta ga mazan banza sai kuma ta dawo yaya ya aureta, ai abun kunya ma ne wallahi”