Sashe 116
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi ta faɗa tana ɗan leƙen ta. Sai Haleema ta yi saurin amsawa.
“A'a plate ɗin ne kawai ya fashe”
Ummi ta maida hankalinta gurin ɗan ta.
“Im happy for you Son, na daɗe ina jiran wannan ranar, you have no idea how happy you make me, sai dai ban gane wacce kake magana ba akai kam ba”
“Ye... ”
Ringing ɗin da wayarsa ta yi ne ya hana shi ƙarasa maganar sai yayi saurin tashi ya nufi wani ɓangare na falon yana amsa wayar.
“Salim”
“Sir mun bincika, Manjo Usman Zamau yana sokoto da zama a unguwar clapperto, yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha uku Namra ita ce ta goma, kuma ainahin sunan ta shi ne Khadija, ta yi makaranta a dan fodio tana level 300 aka yi mata aure, kuma har yanzu tana gidan aurenta zaune, facebook username ɗin ta Khadija Usman Zamau instagram kuma Namra's, haka yake a twitter da snapchat”
“Amman ba ku bincika zaman auren ta ba? Har yanzu tana da aure?”
“Binciken mu ya nuna har yanzu tana da aure kuma tana a garin katsina da zama, sunan mijin da take aure Ibrahim amman anfi kiransa da Asim”
“Thank you”
“Your Welcome Sir”
Wayar ya ƙurawa ido yana mamakin yadda Namra zata masa ƙarya, bayan ya tambaye tsakaninta da Allah, taya aurenta zai mutu kowa bai sani ba, hakan yana mufin ƙarya ta masa kenan ko kuma akwai abunda take ɓoyewa.
Juyowa yayi yana ƙoƙarin ɓatar da mamakin dake fuskarsa ya kalli Ummi yana tahowa ya ce.
“Wani aiki ya tashi Ummi Ana nema na a Kaduna yanzu yanzu nan”
“What?”
Ummi ta faɗa da mugun mamaki. Shi kuma ya ɗan ɗaga gira yana kallon Amal.dake zumuɗin labarin daya fara badawa.
Hello habibaties nasan kuna haƙuri da ni dan Allah ku ƙara haƙurin. Wallahi abubuwa ne suke min yawa, ga kuma rashin wutar nepa a gusau, yau four days babu wuta, sai an tashi engine ne muke samu mu saka. Idan kuma ka matsa za'a ce sai ka biya na Mai 😂 you know how our grandma's are, sai haƙuri 😂
Love you all fisabilliah ♥️🌹🌺❤
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *71*
Ɗauke kansa yayi daga kallon da yake ma Amal ya kalli Ummi, irin babu zacen wasa a kalamansa.
“Nima sai da na ce miyasa ba su bar ni nayi aikin ba acan ba sai yanzu da na dawo”
“Abdallah ka ce min kun samu hutu fa? Aikin me zaka je yi yanzu?”
“Wai General ne zai zo daga Abuja zuwa Kaduna gobe, kuma dole ne muje. Bari naje ya canja kaya gobe da safe ai zan dawo”
Be jira abunda Ummi zata ce ba, ya nufi ƙofar fita yana lalabar number Salim dan ya sama masa jirgin da zai koma Kaduna yanzu ko da Yammar nan.
Ummi dai da kallo Mamaki ta bishi, ta fi kowa sanin ɗanta dan haka ta san ba aiki ne zai maida shi Kaduna ba, sai dai wani abun na daban, kai ta girgiza tana kallon Amal data wani turo baki.
“Be ma ƙarasa mana labarin ba”
Ummi ta miƙe tsaye ta nufi kitchen tana faɗin
“Uhnm kya ji da shi”
AMIRA POV.
Tana gama kwashe plate ɗin da ya fashe ta zuba a shara, sai ta nufi ɗakinta cikin wani irin kuka marar misaltuwa.
Saman gadon Amal ta faɗa ta kife tana rera kukanta a hankali yadda wani ba zai ji.
“Shikenan na rasa komai, wata yake so ba ni ba, shi ma na rasa shi”
Tausayin kanta take da kanta tana tunanin irin rayuwar da zata yi nan gaba. Bayan ta rasa duk wani abun da zai iya saka ta farinciki. A hankali Haleema ta turo ƙofar ta shigo fuskarta ɗauke da tausayin Amira,wanda har zuciyarta haka ne. Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta taɓa ta.
“Ki yi haƙuri Amira, ni kai na ban san haka zai faru ba...”
Da sauri Amira ta ɗago ta kalleta da idonta da suka gana canja kala saboda kuka.
“Ke ma kin yarda na rasa ɗan uwanki ko? Babu wani abun da za kiyi? Dan Allah ki taimaka min Haleema kema mecece zaki iya shiga a halin dana shiga, kin san irin abunda nake ji, Wallahi ina son Yaya kuma tsakani da Allah zan zauna da shi, idan har na ci amanarsa na yarda amanar Allah ta ci ni, na rantse da Allah ba zan cutar da shi ba”
Kuka take sosai zuciyarta a narke, ta kama hannayen Haleema ta riƙa tana mai jin kamar Haleema ta yi mata maganin damuwarta.
Cikin kuka Haleem ta ce.
“Babu wani taimako da zan iya yi miki Amira, Big Bro babu mai saka shi dole idan ba Ummi ba, kuma idan har ya nuna baya so ita ma bata so, babu abunda ya cutar da ke kamar zama ba a gurin iyayen ki ba”
“Ba zan iya komawa ba, ban san yadda zan yi na koma ba”
Ya zube ƙasa zaune tana rushewa da sabon kuka. Haleema ta riƙa ta tana bata haƙuri. Kamin ta tashi cikin ɓacin rai ta nufi hanyar fita, Amal ta samu tsaye jikin ƙofar ta yi wani wuƙi-wuƙi da ido.
“Ummi tan kiran ki”
Ta faɗa a sagarce, sannan ta falfala da gudu ta nufi ɗakin Ummi ɗin. Haleema ta rufa mata baya tana share hawayenta. Ƙusƙus ta tarar Amal na yi gurin Ummi, hakan ya tabbatar ma da Haleema Amal ta ji abunda suke cewa.
Meesha na gaban maduba Ummi tana ɗanɗasa kwaliya ita da Fauza, dan su basu ma san Abdool ya dawo ba.
“Ummi ga ni”
Ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zama kusa da ita.
“Gulma ta kuke yi?”
Da sauri Haleema ta sake kallon Ummi baki sake, kamin ta maida dubanta gurin Amal.
“Amman yarinyar nan munafuka ce Wallahi, gulamar ta kika ce na yi, aiko sai na miki ɗan banzan duka a gidan nan”
Ummi ta katsa mata tsawa.
“A'a akan me? Maganar me kuke ke da ita har kuke kuka?”
“Walahi akan big bro ne, dan ta ji ya samu mata shine take kuka ina bata haƙuri”
“Dan ya samu mata sai aka yi me?”
“Kin san son shi take sosai wallahi”
“Amman dai Haleema baki da hankali, ke ko a mafarki aka ce yayanki zai aureta idan kika farka ai kya nemi tsarin Allah, macen data zauna da yan fashi? Kika san ciki nawa ta zubar? Baki san zaman ta a nan ma it very risk ba”
“Haba Ummi ciwo ƴa mace na ƴa mace ne, yanzu idan nice a wannan hali zaki jidaɗi? Ba ita ta ƙaddaro ma kanta ba, kuma ta yi sadaukarwa ma Big Bro ita ta cancanci ya so ta wallahi”
Ummi kasa magana ta yi saboda mamakin furucin Haleema. Meesha ta taso daga gaban madubi da take zaune tana faɗin.
“Kin san me Ummi zata iya saka mana guba duka mu mutu idan har ta ji Big Bro ba zai aureta ba, ƙila ma turo ta aka yi, ta ina ma.taji Yaya ya samu mata? Kodai ta ga alamun ba zai so ta ba ne”
Fauza ta amsa.
“Kuma Wallahi irin waɗan nan ba tsoron kisan kai suke ba, tun da sun saba”
Ran Haleema ya ɓace sosai.
“Ku daina judge mutane ne, hakan be da kyau, Allah ma yana karɓar tubar bayinsa balle kuma mu....”
Shigowar Abdool ne yasa duk suka warsar da maganar, Fauza da Meesha suka fara ɗaukin shigowarsa tare da masa sannu da zuwa.
“Ai kune ba ku san ya dawo ba, mu tuni muka sani har ya ba mu labarin matarsa da zai aura”
Ya ɗaga gira ɗaya yana kallon Amal, ita kuna ta shigar da kai jikin Ummi dake dariya, ita ala dole ga auta.
“My girls ku fita za mu yi magana”
Ya faɗa yana ƙoƙarin zama a kujerar dake fuskantar gadon Ummi. Ba musu duk suka fita har Amal uwar son zancen dan bata ga alamun wasa a fuskarsa ba balle ta tsaya.
“Maganar gaskiya Ummi ba aiki zani ba, gurin yarinyar nan zan koma, kawai ki min addu'ah, gobe da safe zan dawo”
“Na gama karantar ka sarau Lamiɗo kallon ka kawai na ke yi. Allah ya kai ka lafiya, kuma a gaishe min ita sosai da sosai”
‘Ai ba gaisuwa ba, ni kaina ban san makomata ba’
Zance daa ya faɗo masa kenan a rai kamin ya ɗago ya saurari zancen da Ummi ta ɗora da shi.
“Dan Allah ka nemo iyayen yarinyar nan, idan ba zata iya zuwa ba, su suzo su tafi da ita”
“Ummi laifin wa? Idan na yi magana ai cewa kike na ɗaga mata ƙafa”
“Ai ba ƙafa ba komai ma.an ɗaga mata, yanzu kam ya kamata ace tana gaban iyayenta”
Miƙewa yayi tsaye yana faɗin
“Don't worry Ummi, if she planning something evil, za a sanar da ni, ai akwai mai kula da cctv camera. A min addu'ah jirgin mu zai tashi nan da ten minutes”
“Allah ya kiyaye ya kai ku lafiya”
Tasowa ta yi ta suka fito tare da shi yana labarta mata maganar da suka yi da Mai Martaba.
Ko da ya isa airport sauran minti uku jirgin ya tashi, abun ka da manya a take aka masa checking ya wuce.
Be da sukuni har sai da jirginsu ya sauka garin Kaduna, yana sauka airport yayi waya daga Abuja, suka kuma suka yi waya a kaduna, cikin minti ashiri sai ga direba in military uniform sun zo ɗaukarsa.
“A'a plate ɗin ne kawai ya fashe”
Ummi ta maida hankalinta gurin ɗan ta.
“Im happy for you Son, na daɗe ina jiran wannan ranar, you have no idea how happy you make me, sai dai ban gane wacce kake magana ba akai kam ba”
“Ye... ”
Ringing ɗin da wayarsa ta yi ne ya hana shi ƙarasa maganar sai yayi saurin tashi ya nufi wani ɓangare na falon yana amsa wayar.
“Salim”
“Sir mun bincika, Manjo Usman Zamau yana sokoto da zama a unguwar clapperto, yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha uku Namra ita ce ta goma, kuma ainahin sunan ta shi ne Khadija, ta yi makaranta a dan fodio tana level 300 aka yi mata aure, kuma har yanzu tana gidan aurenta zaune, facebook username ɗin ta Khadija Usman Zamau instagram kuma Namra's, haka yake a twitter da snapchat”
“Amman ba ku bincika zaman auren ta ba? Har yanzu tana da aure?”
“Binciken mu ya nuna har yanzu tana da aure kuma tana a garin katsina da zama, sunan mijin da take aure Ibrahim amman anfi kiransa da Asim”
“Thank you”
“Your Welcome Sir”
Wayar ya ƙurawa ido yana mamakin yadda Namra zata masa ƙarya, bayan ya tambaye tsakaninta da Allah, taya aurenta zai mutu kowa bai sani ba, hakan yana mufin ƙarya ta masa kenan ko kuma akwai abunda take ɓoyewa.
Juyowa yayi yana ƙoƙarin ɓatar da mamakin dake fuskarsa ya kalli Ummi yana tahowa ya ce.
“Wani aiki ya tashi Ummi Ana nema na a Kaduna yanzu yanzu nan”
“What?”
Ummi ta faɗa da mugun mamaki. Shi kuma ya ɗan ɗaga gira yana kallon Amal.dake zumuɗin labarin daya fara badawa.
Hello habibaties nasan kuna haƙuri da ni dan Allah ku ƙara haƙurin. Wallahi abubuwa ne suke min yawa, ga kuma rashin wutar nepa a gusau, yau four days babu wuta, sai an tashi engine ne muke samu mu saka. Idan kuma ka matsa za'a ce sai ka biya na Mai 😂 you know how our grandma's are, sai haƙuri 😂
Love you all fisabilliah ♥️🌹🌺❤
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *71*
Ɗauke kansa yayi daga kallon da yake ma Amal ya kalli Ummi, irin babu zacen wasa a kalamansa.
“Nima sai da na ce miyasa ba su bar ni nayi aikin ba acan ba sai yanzu da na dawo”
“Abdallah ka ce min kun samu hutu fa? Aikin me zaka je yi yanzu?”
“Wai General ne zai zo daga Abuja zuwa Kaduna gobe, kuma dole ne muje. Bari naje ya canja kaya gobe da safe ai zan dawo”
Be jira abunda Ummi zata ce ba, ya nufi ƙofar fita yana lalabar number Salim dan ya sama masa jirgin da zai koma Kaduna yanzu ko da Yammar nan.
Ummi dai da kallo Mamaki ta bishi, ta fi kowa sanin ɗanta dan haka ta san ba aiki ne zai maida shi Kaduna ba, sai dai wani abun na daban, kai ta girgiza tana kallon Amal data wani turo baki.
“Be ma ƙarasa mana labarin ba”
Ummi ta miƙe tsaye ta nufi kitchen tana faɗin
“Uhnm kya ji da shi”
AMIRA POV.
Tana gama kwashe plate ɗin da ya fashe ta zuba a shara, sai ta nufi ɗakinta cikin wani irin kuka marar misaltuwa.
Saman gadon Amal ta faɗa ta kife tana rera kukanta a hankali yadda wani ba zai ji.
“Shikenan na rasa komai, wata yake so ba ni ba, shi ma na rasa shi”
Tausayin kanta take da kanta tana tunanin irin rayuwar da zata yi nan gaba. Bayan ta rasa duk wani abun da zai iya saka ta farinciki. A hankali Haleema ta turo ƙofar ta shigo fuskarta ɗauke da tausayin Amira,wanda har zuciyarta haka ne. Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta taɓa ta.
“Ki yi haƙuri Amira, ni kai na ban san haka zai faru ba...”
Da sauri Amira ta ɗago ta kalleta da idonta da suka gana canja kala saboda kuka.
“Ke ma kin yarda na rasa ɗan uwanki ko? Babu wani abun da za kiyi? Dan Allah ki taimaka min Haleema kema mecece zaki iya shiga a halin dana shiga, kin san irin abunda nake ji, Wallahi ina son Yaya kuma tsakani da Allah zan zauna da shi, idan har na ci amanarsa na yarda amanar Allah ta ci ni, na rantse da Allah ba zan cutar da shi ba”
Kuka take sosai zuciyarta a narke, ta kama hannayen Haleema ta riƙa tana mai jin kamar Haleema ta yi mata maganin damuwarta.
Cikin kuka Haleem ta ce.
“Babu wani taimako da zan iya yi miki Amira, Big Bro babu mai saka shi dole idan ba Ummi ba, kuma idan har ya nuna baya so ita ma bata so, babu abunda ya cutar da ke kamar zama ba a gurin iyayen ki ba”
“Ba zan iya komawa ba, ban san yadda zan yi na koma ba”
Ya zube ƙasa zaune tana rushewa da sabon kuka. Haleema ta riƙa ta tana bata haƙuri. Kamin ta tashi cikin ɓacin rai ta nufi hanyar fita, Amal ta samu tsaye jikin ƙofar ta yi wani wuƙi-wuƙi da ido.
“Ummi tan kiran ki”
Ta faɗa a sagarce, sannan ta falfala da gudu ta nufi ɗakin Ummi ɗin. Haleema ta rufa mata baya tana share hawayenta. Ƙusƙus ta tarar Amal na yi gurin Ummi, hakan ya tabbatar ma da Haleema Amal ta ji abunda suke cewa.
Meesha na gaban maduba Ummi tana ɗanɗasa kwaliya ita da Fauza, dan su basu ma san Abdool ya dawo ba.
“Ummi ga ni”
Ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zama kusa da ita.
“Gulma ta kuke yi?”
Da sauri Haleema ta sake kallon Ummi baki sake, kamin ta maida dubanta gurin Amal.
“Amman yarinyar nan munafuka ce Wallahi, gulamar ta kika ce na yi, aiko sai na miki ɗan banzan duka a gidan nan”
Ummi ta katsa mata tsawa.
“A'a akan me? Maganar me kuke ke da ita har kuke kuka?”
“Walahi akan big bro ne, dan ta ji ya samu mata shine take kuka ina bata haƙuri”
“Dan ya samu mata sai aka yi me?”
“Kin san son shi take sosai wallahi”
“Amman dai Haleema baki da hankali, ke ko a mafarki aka ce yayanki zai aureta idan kika farka ai kya nemi tsarin Allah, macen data zauna da yan fashi? Kika san ciki nawa ta zubar? Baki san zaman ta a nan ma it very risk ba”
“Haba Ummi ciwo ƴa mace na ƴa mace ne, yanzu idan nice a wannan hali zaki jidaɗi? Ba ita ta ƙaddaro ma kanta ba, kuma ta yi sadaukarwa ma Big Bro ita ta cancanci ya so ta wallahi”
Ummi kasa magana ta yi saboda mamakin furucin Haleema. Meesha ta taso daga gaban madubi da take zaune tana faɗin.
“Kin san me Ummi zata iya saka mana guba duka mu mutu idan har ta ji Big Bro ba zai aureta ba, ƙila ma turo ta aka yi, ta ina ma.taji Yaya ya samu mata? Kodai ta ga alamun ba zai so ta ba ne”
Fauza ta amsa.
“Kuma Wallahi irin waɗan nan ba tsoron kisan kai suke ba, tun da sun saba”
Ran Haleema ya ɓace sosai.
“Ku daina judge mutane ne, hakan be da kyau, Allah ma yana karɓar tubar bayinsa balle kuma mu....”
Shigowar Abdool ne yasa duk suka warsar da maganar, Fauza da Meesha suka fara ɗaukin shigowarsa tare da masa sannu da zuwa.
“Ai kune ba ku san ya dawo ba, mu tuni muka sani har ya ba mu labarin matarsa da zai aura”
Ya ɗaga gira ɗaya yana kallon Amal, ita kuna ta shigar da kai jikin Ummi dake dariya, ita ala dole ga auta.
“My girls ku fita za mu yi magana”
Ya faɗa yana ƙoƙarin zama a kujerar dake fuskantar gadon Ummi. Ba musu duk suka fita har Amal uwar son zancen dan bata ga alamun wasa a fuskarsa ba balle ta tsaya.
“Maganar gaskiya Ummi ba aiki zani ba, gurin yarinyar nan zan koma, kawai ki min addu'ah, gobe da safe zan dawo”
“Na gama karantar ka sarau Lamiɗo kallon ka kawai na ke yi. Allah ya kai ka lafiya, kuma a gaishe min ita sosai da sosai”
‘Ai ba gaisuwa ba, ni kaina ban san makomata ba’
Zance daa ya faɗo masa kenan a rai kamin ya ɗago ya saurari zancen da Ummi ta ɗora da shi.
“Dan Allah ka nemo iyayen yarinyar nan, idan ba zata iya zuwa ba, su suzo su tafi da ita”
“Ummi laifin wa? Idan na yi magana ai cewa kike na ɗaga mata ƙafa”
“Ai ba ƙafa ba komai ma.an ɗaga mata, yanzu kam ya kamata ace tana gaban iyayenta”
Miƙewa yayi tsaye yana faɗin
“Don't worry Ummi, if she planning something evil, za a sanar da ni, ai akwai mai kula da cctv camera. A min addu'ah jirgin mu zai tashi nan da ten minutes”
“Allah ya kiyaye ya kai ku lafiya”
Tasowa ta yi ta suka fito tare da shi yana labarta mata maganar da suka yi da Mai Martaba.
Ko da ya isa airport sauran minti uku jirgin ya tashi, abun ka da manya a take aka masa checking ya wuce.
Be da sukuni har sai da jirginsu ya sauka garin Kaduna, yana sauka airport yayi waya daga Abuja, suka kuma suka yi waya a kaduna, cikin minti ashiri sai ga direba in military uniform sun zo ɗaukarsa.