Sashe 67
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Na sani haba, ke dai ki zo ina neman ki, amman fa anjima idan mun tashi aiki”
“Na ji”
Ta kashe wayar, ta kunna motar ta hau titi.
ABDOOL POV.
Ko da sha ɗayan safe tayi Ummi da Jidda sun sauka garin Abuja. Kai tsaye ta wuce masaukin Abdool, a lokacin baya ma gidan yana gurin meeting, haka ta zauna a gidan har ya dawo sannan hankalinta ya kwanta ganin da gaske babu abunda ya same shi.
“Ummi na faɗa miki am fine amman kika ƙi yarda da ɗan ki”
“Yanzu ai na yarda, ina ita yarinyar ta ji sauƙi?”
“Eh ance min jiya ta farka, amman ban samu na je dubata ba, amman na ce suje su ɗauƙi statement”
“Allah sarki baiwar Allah ai ta taimaka da yanzu kai ne aka harba”
“Ko bata tare ba, ba zasu harbe ni ba, dan Allah ya rubuta ba zasu same ni ba”
“Haka ne kuma”
“Ummi me kuke so a siyo muku?”
“A'a ni ba zaka ƙara siyen abincin nan ba, ai da gaskiyar Mai martaba da yake cewa ka daina yawo kai ƙaɗai, ni gaskiya ya kamata ace ma ka yi aure dan ka huta da wannan wahalar siyen abincin kullum”
Dariya yayi ya tashi ya fita. Be daɗe ba ya dawo, ya tsaya daga bakin ƙofa
“Ummi zan je asibitin idan kun huta kun ci abinci direba zai kai ku ku ganta”
“To a kula dan Allah”
“Inshallah”
Ya ciro wayarsa dake ringing ya amsa kiran ya juya yana magana ya fice. Sai da ya biya wani office nasu yayi wani meeting sannan ya wuce.
Sun masa bayanin abunda suke zargi akansa, suka nuna masa bayananta da suka ɗauka sannan ya shiga ɗakin da take.
Kife take saman gadon asibitin sanye da tufafin majiyanta, wani irin kallo take masa irin kallon nan na mutum be san yana yi ba. Har ya zauna a kujerar dake facing ɗinta bata ɗauke idonta akansa ba.
Hannunsa ya riƙa yawo da shi dan ya tabbatar tana cikin hankalinta ko akasin hakan. Sai kawai ta lumshe ido hawaye ya silalo daga idon nata. She just can't believe Abdallah take ganin da idonta, mutumen da ko a mafarki take ganin yayi mata nisa, sai dai tasan tayi betrayed wanda yayi mata mafaka a lokacin da bata da gurin zuwa, ga shi waɗanda suka mata tambaya a ɗazu sun tabbatar mata da ya mutu.
“How are you feeling”
Ta buɗe ido ta kalleashi, sai kuma ta kawarda kanta gefe kamar bata ji abunda yace ba.
“Ko ba ki jin turanci ne?”
Ya tambaya yana leƙen fuskarta.
“Ina ji”
Ta amsa ba tare data kalleshi ba.
“Me kike yi ma kuka?”
“Kukan baƙinciki nake, miyasa baka bar ni can na mutu ba? Sai ka ɗauko ni ka kawo ni asibiti?”
“Taya zan bar mace data sadaukarda ranta gare ni ta mutu?”
“Na sadaukarda raina a gare ka saboda ni na rasa nawa ran, kai kana da amfani ga alumma ni ko bana shi, kuma na san duk na sadaukarda rai na a gareka dole ne kai ka rayu ni na mutu”
“Sai gashi kuma sai dik muka rayu”
“Shiyasa ni nake baƙinciki, na yi tunanin ni tawa wahalar ta yanke daga nan ne, ashe akwai sauranta”
“Wacece ke? Miyasa kike irin wannan furucin?”
“Nice wacce ta rasa uwa da uba, wacca aka koreta daga gidan su saboda saurayi ya yaudare ta”
“Ban gane ba?”
“Ƙawata ta haɗa kai da ɗan'uwanta ta yaudare ni. Fyaɗe tasa ɗan'uwanta yayi min, sanadin hakan na samu ciki, ni kuma sai iyayena suka kore ni, na zaje garin Kaduna, ranar dana sauka a garin na haɗu da Guy son yaje tasha karɓar saƙo, sai ya ɗauko ni ya kawo ni gidansa da sunan zai kwana da ni ya biya ni, daya fahimci bana da gurin zama, sai yayi masauki a gidansa, ashe ɗan fashine kuma yana kidnapped ni ban sani ba sai bayan mun shaƙu da shi, shi ya zubar min da cikin da ke jikina ya mayarda ni karuwarsa”
“Ayyah sorry, amman me kika sani game da Guy Son?”
“Ban san komai akansa ba, baya bari na shiga lamurransa”
“Ya aka yi kika san yana attacking ɗi na?”
“Saboda ya san ina son zuwa Abuja, sai yace zai zo da ni, amman wani aiki zai zo yi, na kashe wani soja wanda wata mata tasa aka she shi, amman a nan ba su kashe ka sai ka koma Katsina”
“Ya faɗa miki wacece matar?”
“Be faɗa min ba, ban ma san kai wanene ba kawai ya faɗa min zai zo bibiyar sawon ka ne, ni kuma naga ba zan iya bari ta kashe ka ba, shiyasa na zaɓi mutuwa kai ka rayu, dan nasan dole zai nemi kashe ni, ni kuma buƙatana ya biya tun da ka rayu”
“Wane gari kike?”
“Sokoto”
“Amman miyasa kika zauna da shi bayan kin san yana aikata kisan kai?”
“Me kake tunani ga mace da iyayenta suka koreta? Idan ban zauna da shi ba da wa zan zauna? Wa zai min masauki? Ina za a karɓe ni?”
Kuka ta fara rerawa tasa hannu a baki gwanin tausayi.
Kallonta yake indai har da gaske na abunda ta faɗa, to ita abar tausayawa ce, sai dai shi yana jin be yardar da ita ba.
Jin kukan nata na son yawa yasa shi tashi ya bar ɗakin. Baga ɗaya fita yayi daga harabar asibitin ya nufi wani part na gurin. Wani ɗaki ya shiga ya kwashe waya ɗaya a ɗakin suna tattaunawa sai da aka ce masa ga Ummi nan sannan ya fito ya tare su.
“Jikin nata da sauƙi dai ko?”
“Da sauƙi sosai ma, mun yi magana da ita sosai sai dai a bayanan ta ban yarda da ita ba, dan haka nasa a bincika min komai a kanta”
“Hakan yayi mi tace maka ne?”
A nan ya fara bata labarin da Amira ta bashi, suna takawa zuwa part ɗin da Asibitin take da ƙafa.
Sosai da sosai Ummi ta ji tausayinta ya kamata, har idonta ya cika da ƙwallah, sai Allah wadai take ma iyayenta da ƙawar data cuce ta.
Amira na jin lokacin da suka shigo amman tayi pretending like she's seriously sleep. Fukarta kawai Ummi ta leƙa cike da tausayawa ta juyo ta fito tana mata addu'ar samun sauƙi.
KALSOOM POV.
Tayi mamakin ganin haila a yanzu, bayan tasan tana ɗauke da ciki, kuma rabonta da haila tun kamin ta samu ciki. Hakan yasa ta fara zargin ko dai bata da cikin ne? Sai dai kuma ita tasan tana jin alamun masu ciki kuma Doc ma ya tabbatar mata da haka. Wani tunanin ne ya zo mata, wata ƙila tana cikin matan da suke haila a lokacin da suke ɗauke da juna biyu.
Ita dai abun ya ɗaure mata kai. Tun a dare da abun ya same ta Doc ya sani sai ya ɗaga mata kafa ya saurara na tsawon kwana biyu ya gani ko jinin zai ɗauke mata, amman be ɗauke mata ba. Hakan ya bashi mamaki.
Yayi mata tambaboyi akan lafiyarta, kamin ya ɗauke ta suje suje su yi hoto dan tabbatar da lafiyarta.
Ya yi mamakin results ɗin da hoton ya bada wai bata da ciki, alamu ya nuna mahaifarta ma ciki be taɓa zama ciki ba.
A tare suka dawo gida sai dai be yarda da faɗa mata abunda result ɗin ya bada ba, dan har yanzu mamaki yake, daya sauke ta be shigo ciki ba, ya ce mata ya zai koma gurin aiki.
Ita sam bata lura ba, dan bata kawo komai a ranta ba. Tana shiga falon ranta yayi mugun ɓaci ganin yadda duk suka lalata falon kamar bata gyara shi ba kamin ta fita.
Saman kujera ta zauna tana kallon falon cike da takaici tace
“Ezzah zo ki share falon nan, Ulfah ke kuma ki kwashe plates ɗin nan shine bayan fita na kuka sake ɗiban abinci kamar ba ku ci ba? Kuma duk kuka lalata falon haba dan Allah miyasa ba ku tausayina ne?”
“Ezzah ce ta ce mu ɗibo mu ci tun da abincin Baban mu ne, wai ita bata ƙoshi ba kin sa mata kaɗan”
Ulfah ta faɗa tana shirin tattara plates ɗin. Kallon Ezzah Kalsoom tayi cike da mamaki.
“Abincin da nake sa muku ne baya isarku shine ba zaki yi magana a daɗa miki ba? Sometimes ba ke da kanki kike ɗiba ba? Ezzah me ke damun ki ne? Me yake cikin kan ki ne? Kwanakin nan kwata-kwata kin canja kina son lalata kan ki”
Wata irin harara ta bankaɗo ma Kalsoom kamar ta taso tazo ta maƙareta. Kalsoom ta nufi inda take tana nuna kan ta
“Ke ni kike harara? Warin ki ce ne?”
Ta zungureta. Sai kawai ta fashe da kuka daman jira take.
“Wayyo Ammyn mu....”
“Ooo munafuka, daman abunda kike nema kenan ko? Na dake ki so that ace na cuce ki ko? Ke ƙaramar yarinya da ke kin san munafurci? Tau Wallahi ba zan ɗauka ba, ba zai yiyu na yi kishi da uwarki ba yanzu kuma na yi da ke ba, tashi ki share falon nan ko na miki matsiyacin duka”
Cikin kuka ta tashi ta shiga kitchen ta ɗauko tsintsiya ta soma sharar. Ulfah na daga gefe tana kallon Kalsoom cikinta dik ya ɗuri ruwa ji take kamar itama zuwa zatayi ta dake ta.
Doc be dawo ba sai dare, tun a bakin ƙofa Ulfah ta same shi ta labarta masa abunda Kalsoom tayi ma Ezzah, sai dai be ɗauki abun serious ba dan yasan Kalsoom ba zata dake ta a banza ba.
Sai dai samun Ezzah a falo da yayi tana kuka ya ɗan sosa masa rai.
“Me kike yi ma kuka kuma?”
“Yunwa na ke ji, Anty tace karna sake ɗiba abinci har sai ta ga dama ta ba ni”
“Ba ki ci abinci dare ba ne?”
“Har na rana ban ci ba, wai dan nace sai na faɗa ma maka ta fita”
“Je ki ɗibi abincin zan yi magana da ita”
Ta tashi ta nufi dinning, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom cike da gajiya.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: 4»»»»6»»»»»»»»»»»»»
“Na ji”
Ta kashe wayar, ta kunna motar ta hau titi.
ABDOOL POV.
Ko da sha ɗayan safe tayi Ummi da Jidda sun sauka garin Abuja. Kai tsaye ta wuce masaukin Abdool, a lokacin baya ma gidan yana gurin meeting, haka ta zauna a gidan har ya dawo sannan hankalinta ya kwanta ganin da gaske babu abunda ya same shi.
“Ummi na faɗa miki am fine amman kika ƙi yarda da ɗan ki”
“Yanzu ai na yarda, ina ita yarinyar ta ji sauƙi?”
“Eh ance min jiya ta farka, amman ban samu na je dubata ba, amman na ce suje su ɗauƙi statement”
“Allah sarki baiwar Allah ai ta taimaka da yanzu kai ne aka harba”
“Ko bata tare ba, ba zasu harbe ni ba, dan Allah ya rubuta ba zasu same ni ba”
“Haka ne kuma”
“Ummi me kuke so a siyo muku?”
“A'a ni ba zaka ƙara siyen abincin nan ba, ai da gaskiyar Mai martaba da yake cewa ka daina yawo kai ƙaɗai, ni gaskiya ya kamata ace ma ka yi aure dan ka huta da wannan wahalar siyen abincin kullum”
Dariya yayi ya tashi ya fita. Be daɗe ba ya dawo, ya tsaya daga bakin ƙofa
“Ummi zan je asibitin idan kun huta kun ci abinci direba zai kai ku ku ganta”
“To a kula dan Allah”
“Inshallah”
Ya ciro wayarsa dake ringing ya amsa kiran ya juya yana magana ya fice. Sai da ya biya wani office nasu yayi wani meeting sannan ya wuce.
Sun masa bayanin abunda suke zargi akansa, suka nuna masa bayananta da suka ɗauka sannan ya shiga ɗakin da take.
Kife take saman gadon asibitin sanye da tufafin majiyanta, wani irin kallo take masa irin kallon nan na mutum be san yana yi ba. Har ya zauna a kujerar dake facing ɗinta bata ɗauke idonta akansa ba.
Hannunsa ya riƙa yawo da shi dan ya tabbatar tana cikin hankalinta ko akasin hakan. Sai kawai ta lumshe ido hawaye ya silalo daga idon nata. She just can't believe Abdallah take ganin da idonta, mutumen da ko a mafarki take ganin yayi mata nisa, sai dai tasan tayi betrayed wanda yayi mata mafaka a lokacin da bata da gurin zuwa, ga shi waɗanda suka mata tambaya a ɗazu sun tabbatar mata da ya mutu.
“How are you feeling”
Ta buɗe ido ta kalleashi, sai kuma ta kawarda kanta gefe kamar bata ji abunda yace ba.
“Ko ba ki jin turanci ne?”
Ya tambaya yana leƙen fuskarta.
“Ina ji”
Ta amsa ba tare data kalleshi ba.
“Me kike yi ma kuka?”
“Kukan baƙinciki nake, miyasa baka bar ni can na mutu ba? Sai ka ɗauko ni ka kawo ni asibiti?”
“Taya zan bar mace data sadaukarda ranta gare ni ta mutu?”
“Na sadaukarda raina a gare ka saboda ni na rasa nawa ran, kai kana da amfani ga alumma ni ko bana shi, kuma na san duk na sadaukarda rai na a gareka dole ne kai ka rayu ni na mutu”
“Sai gashi kuma sai dik muka rayu”
“Shiyasa ni nake baƙinciki, na yi tunanin ni tawa wahalar ta yanke daga nan ne, ashe akwai sauranta”
“Wacece ke? Miyasa kike irin wannan furucin?”
“Nice wacce ta rasa uwa da uba, wacca aka koreta daga gidan su saboda saurayi ya yaudare ta”
“Ban gane ba?”
“Ƙawata ta haɗa kai da ɗan'uwanta ta yaudare ni. Fyaɗe tasa ɗan'uwanta yayi min, sanadin hakan na samu ciki, ni kuma sai iyayena suka kore ni, na zaje garin Kaduna, ranar dana sauka a garin na haɗu da Guy son yaje tasha karɓar saƙo, sai ya ɗauko ni ya kawo ni gidansa da sunan zai kwana da ni ya biya ni, daya fahimci bana da gurin zama, sai yayi masauki a gidansa, ashe ɗan fashine kuma yana kidnapped ni ban sani ba sai bayan mun shaƙu da shi, shi ya zubar min da cikin da ke jikina ya mayarda ni karuwarsa”
“Ayyah sorry, amman me kika sani game da Guy Son?”
“Ban san komai akansa ba, baya bari na shiga lamurransa”
“Ya aka yi kika san yana attacking ɗi na?”
“Saboda ya san ina son zuwa Abuja, sai yace zai zo da ni, amman wani aiki zai zo yi, na kashe wani soja wanda wata mata tasa aka she shi, amman a nan ba su kashe ka sai ka koma Katsina”
“Ya faɗa miki wacece matar?”
“Be faɗa min ba, ban ma san kai wanene ba kawai ya faɗa min zai zo bibiyar sawon ka ne, ni kuma naga ba zan iya bari ta kashe ka ba, shiyasa na zaɓi mutuwa kai ka rayu, dan nasan dole zai nemi kashe ni, ni kuma buƙatana ya biya tun da ka rayu”
“Wane gari kike?”
“Sokoto”
“Amman miyasa kika zauna da shi bayan kin san yana aikata kisan kai?”
“Me kake tunani ga mace da iyayenta suka koreta? Idan ban zauna da shi ba da wa zan zauna? Wa zai min masauki? Ina za a karɓe ni?”
Kuka ta fara rerawa tasa hannu a baki gwanin tausayi.
Kallonta yake indai har da gaske na abunda ta faɗa, to ita abar tausayawa ce, sai dai shi yana jin be yardar da ita ba.
Jin kukan nata na son yawa yasa shi tashi ya bar ɗakin. Baga ɗaya fita yayi daga harabar asibitin ya nufi wani part na gurin. Wani ɗaki ya shiga ya kwashe waya ɗaya a ɗakin suna tattaunawa sai da aka ce masa ga Ummi nan sannan ya fito ya tare su.
“Jikin nata da sauƙi dai ko?”
“Da sauƙi sosai ma, mun yi magana da ita sosai sai dai a bayanan ta ban yarda da ita ba, dan haka nasa a bincika min komai a kanta”
“Hakan yayi mi tace maka ne?”
A nan ya fara bata labarin da Amira ta bashi, suna takawa zuwa part ɗin da Asibitin take da ƙafa.
Sosai da sosai Ummi ta ji tausayinta ya kamata, har idonta ya cika da ƙwallah, sai Allah wadai take ma iyayenta da ƙawar data cuce ta.
Amira na jin lokacin da suka shigo amman tayi pretending like she's seriously sleep. Fukarta kawai Ummi ta leƙa cike da tausayawa ta juyo ta fito tana mata addu'ar samun sauƙi.
KALSOOM POV.
Tayi mamakin ganin haila a yanzu, bayan tasan tana ɗauke da ciki, kuma rabonta da haila tun kamin ta samu ciki. Hakan yasa ta fara zargin ko dai bata da cikin ne? Sai dai kuma ita tasan tana jin alamun masu ciki kuma Doc ma ya tabbatar mata da haka. Wani tunanin ne ya zo mata, wata ƙila tana cikin matan da suke haila a lokacin da suke ɗauke da juna biyu.
Ita dai abun ya ɗaure mata kai. Tun a dare da abun ya same ta Doc ya sani sai ya ɗaga mata kafa ya saurara na tsawon kwana biyu ya gani ko jinin zai ɗauke mata, amman be ɗauke mata ba. Hakan ya bashi mamaki.
Yayi mata tambaboyi akan lafiyarta, kamin ya ɗauke ta suje suje su yi hoto dan tabbatar da lafiyarta.
Ya yi mamakin results ɗin da hoton ya bada wai bata da ciki, alamu ya nuna mahaifarta ma ciki be taɓa zama ciki ba.
A tare suka dawo gida sai dai be yarda da faɗa mata abunda result ɗin ya bada ba, dan har yanzu mamaki yake, daya sauke ta be shigo ciki ba, ya ce mata ya zai koma gurin aiki.
Ita sam bata lura ba, dan bata kawo komai a ranta ba. Tana shiga falon ranta yayi mugun ɓaci ganin yadda duk suka lalata falon kamar bata gyara shi ba kamin ta fita.
Saman kujera ta zauna tana kallon falon cike da takaici tace
“Ezzah zo ki share falon nan, Ulfah ke kuma ki kwashe plates ɗin nan shine bayan fita na kuka sake ɗiban abinci kamar ba ku ci ba? Kuma duk kuka lalata falon haba dan Allah miyasa ba ku tausayina ne?”
“Ezzah ce ta ce mu ɗibo mu ci tun da abincin Baban mu ne, wai ita bata ƙoshi ba kin sa mata kaɗan”
Ulfah ta faɗa tana shirin tattara plates ɗin. Kallon Ezzah Kalsoom tayi cike da mamaki.
“Abincin da nake sa muku ne baya isarku shine ba zaki yi magana a daɗa miki ba? Sometimes ba ke da kanki kike ɗiba ba? Ezzah me ke damun ki ne? Me yake cikin kan ki ne? Kwanakin nan kwata-kwata kin canja kina son lalata kan ki”
Wata irin harara ta bankaɗo ma Kalsoom kamar ta taso tazo ta maƙareta. Kalsoom ta nufi inda take tana nuna kan ta
“Ke ni kike harara? Warin ki ce ne?”
Ta zungureta. Sai kawai ta fashe da kuka daman jira take.
“Wayyo Ammyn mu....”
“Ooo munafuka, daman abunda kike nema kenan ko? Na dake ki so that ace na cuce ki ko? Ke ƙaramar yarinya da ke kin san munafurci? Tau Wallahi ba zan ɗauka ba, ba zai yiyu na yi kishi da uwarki ba yanzu kuma na yi da ke ba, tashi ki share falon nan ko na miki matsiyacin duka”
Cikin kuka ta tashi ta shiga kitchen ta ɗauko tsintsiya ta soma sharar. Ulfah na daga gefe tana kallon Kalsoom cikinta dik ya ɗuri ruwa ji take kamar itama zuwa zatayi ta dake ta.
Doc be dawo ba sai dare, tun a bakin ƙofa Ulfah ta same shi ta labarta masa abunda Kalsoom tayi ma Ezzah, sai dai be ɗauki abun serious ba dan yasan Kalsoom ba zata dake ta a banza ba.
Sai dai samun Ezzah a falo da yayi tana kuka ya ɗan sosa masa rai.
“Me kike yi ma kuka kuma?”
“Yunwa na ke ji, Anty tace karna sake ɗiba abinci har sai ta ga dama ta ba ni”
“Ba ki ci abinci dare ba ne?”
“Har na rana ban ci ba, wai dan nace sai na faɗa ma maka ta fita”
“Je ki ɗibi abincin zan yi magana da ita”
Ta tashi ta nufi dinning, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom cike da gajiya.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: 4»»»»6»»»»»»»»»»»»»