Sashe 120
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Zan karɓe ta da hannu biyu na mata masauki ta yadda zan shimfiɗa mata sabuwar rayuwar, ita da kanta zata yi nadama ta gane lallai Uba, Uba ne, ta yadda wata rana idan ta ga wanda zai aikata hakan ita da kanta zata hane shi”
“Lallai Mai Martaba kai ne za ka taimaka min wajen dawo da martabar Namra”
“Wacece Namra?”
“Gobe da safe zan dira Katsina zan tabarta maka komai Mai Martaba”
“Allah ya kai mu”
“Amin mu kwana lafiya, Allah ya ƙara mana nisan kwana da lafiya”
Ya aje wayar yana murmushin da shi kaɗai ya san manufarsa.
AMIRA POV.
Tana gama rubuta wasiƙar ta naɗe cikin wata paper, sannan ta ɗauki salati ta saka, ta ta saka ta cikin wani madaidaicin kwali ta yi rolling da wani jan gayenta sai ya fito kamar gift.
Sai da ta gama abunda ta ke sannan ta kwashe komai ta gyara gurin. Saman gado ta koma ta kwanta tana kallon sili kamar mai tunanin wani abu. Haleema ce ta turo kofar ɗakin ta shigo fuskarta ɗauke da damuwa dan ita har ga Allah tausayin Amira take.
Kusa da ita ta zauna tana kallon kwalin dake gefenta.
“Yau duk baki leƙo mu ba? Ko abinci ba ki ci ba”
Sai a lokacin Amira ta tuna rabonta da abincin tun jiya da rana. Sai dai kuma har yanzu bata jin yunwa. Duk ta wani zurma kamar marar lafiya.
Unƙurawa ta yi ta tashi.
“Bana jin yunwa, Dan Allah Haleema ki taimaka min ki kai ni tasha na bada wannan saƙon”
“Saƙon minene Amira?”
“Wasiƙa ce na rubutawa mutumen da ya fara cuta na, wata ƙila idan ya karanta zai gane ina raye har ya wanke, na koma gurin iyayena ko Allah zai sa Yayan ki ya so ni”
Bata damu da sanin abunda yake cikin wasiƙar ba, ta miƙe tsaye
“Okay, bari na ɗauko mayafi na”
Tana ficewa Amira ta tashi cikin rashin kuzari ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta da hawaye ya ɓata ta fito. Wannan karon Hijabi ta ɗauka ta saka, sai ta zauna gefen gado tana kallon kwalin zuciyarta sai bugawa take.
“Mu tafi”
Haleema ta baɗa yayinda ta turo ƙofar ɗakin makulin motarta na hannunta. Da sauri Amira ta ɗauki kwalin suka fice. Maganganu masu daɗi da tausasa zuciya Haleema ta riƙa mata har suka isa tashar. Suna shiga aka riƙa tambayar inda zasu sai Amira ta amsa da
“Motar Sokoto muke nema”
Aka nuna musu, almajira suna haɗawa da gudu ganin haɗaɗiyar mota a zatonsu ko da kayan dako ne. A gafen motoci Haleema ta faka motar suka fito tare, da ƙafa suka ƙarasa kusa da inda ake lodin motar sokoto suka samu direban yana daga gefe zaune yana jiran a gama haɗa masa passengers. Sallama suka fara masa sai ya amsa tare da mutanen da suke gurin.
“Dan Allah saƙo za a kai mu a sokoto”
Cewar Haleema.
“Ok na minene?”
Amira ta dire musu kwalin, kana ta ɗora da.
“Wannan abun za a kai ga addireshin”
Ta ƙarasa tana miƙa masa wata ƴar ƙaramar takardar. Hannu ya kai ya karɓa.
“Okay to zaki bada kuɗin mota, da kuma number wayarki da wanda za a kaiwa saƙon”
“Zan dai baka number na, amman ban da number wanda za'a kaiwa saƙon, shiyasa na rubuta maka addireshin sa, dan Allah ka taimaka min ka kai masa har gida”
“Okay ba matsala, amman gaskiya ko baki yo ba sai kin bada dubu uku, dan za a kai masa har gida ne, kuma kin ga yanayin da ake ciki ba mu cika son karɓar saƙo ba ma”
“Ina zuwa”
Haleema ta faɗa, sai ta juya ta nufi gurin motarta, bata ɗauki lokaci ba ta dawo ta miƙa masa dubu uku ƴan ɗari biyar biyar.
“Gashi amman dan Allah ka tabbatar saƙon ya isa, ki bashi number wayarki so that idan ya kai sai ya kira ya faɗa miki”
Ta ƙarasa tana kallon Amira. Ba musu Amira ta karɓi number wayarsa ta saka a wayarta, sai ta masa flashing number ta ta fito, sai da ta tabbatar yayi saving sannan ta juyo ita da Haleema suka nufi gurin da suka faka motar su.
Haleema ce ta fara shiga sannan Amira, har suka isa gida babu wanda yace da wani uffan, Haleema na wani tunanin na dabam, Amira ma haka har suka isa gida.
Tun kamin su faka motarsu Haleema ta gane yayanta ya dawo, ganin yadda sojojin suka koma cikin natsuwarsu sosai.
“Big bro ya dawo kenan!”
Ta faɗa tana zare key ɗin motar, Amira dai bata ce komai ba, har suka fita motar suka nufi ƙofar shiga falon.
Gabanta ya faɗi sosai lokacin data saka ƙafarta cikin falo, ta yi ido biyu da Abdool.
Abinci yake aunawa a cikinsa yana zubawa Ummi satti, yanayin fuskarsa kawai zaka kalla ka fahimci baya cikin damuwa, dan annuri ne shimfiɗe a fuskarsa.
Cikin sanyin jiki Haleema ta ƙarasa kusa da Ummi dana wasar haƙura, dan tasan laifinta na fita bata faɗawa Ummi ba.
“Daga ina kike?”
Ummi ta tambaya fuskarta babu alamun dariya. Ta ɗan sosa kai tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Ummi dan bata jin zata iya faɗa mata gaskiya.
“Ya Abdool an sauka lafiya”
Amira da ke can gefe Haleema ta miƙawa Abdool gaisuwa. Ba tare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa.
“Lafiya ƙalau”
Sai ya miƙe tsaye yana yi ma Haleema wani kallo.
“Daga Ina kuke?”
“Pizza na ce ta raka ni na siyo kuma ban samu ba”
Ta faɗa tana pretending like she's serious.
“Amman idan zaku je siyen Pizza sai kawai ki kama hanya ku fita without permission?”
“I'm sorry Ummi i promise ba zan sake ba”
“You're very stupid, haka kawai zaki saka kafa ki fita ba tare da kin faɗa ba? Baki san rayuwarku tana cikin haɗari ba? Ba ni kaɗai za a riƙa farauta ba har da ku”
Abdool ya faɗa yana kallonta har handkercheif ɗin dake hannunsa ya faɗi.
“Haba Big Bros Wallahi ba zan ƙara ba, dan Allah ku yi haƙuri”
Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Amira kan idonta na kan Abdool, annurin fuskarsa kawai take kallo, a ɗayan ɓangaren kuma tana Allah-Allah ya manta da handkercheif ɗinsa ta ɗauke, ta yadda zata fi jin daɗin tuna sa idan tana tare da shi.
“Miya hana ki zuwa makaranta?”
Ya tambaya yayinda ya risina ɗaukar handkercheif ɗin.
“Yau ba mu da lacca sai four”
Be sake ce mata komai ba, ya kalli Ummi.
“Zan je gurin Mai Martaba”
“Mu zaka ku? Tun da ka sauka naga ka kira shi fa, akwai abunda kuke shiryawa ko?”
“Kedai Ummi kawai ki sa ido ki yi kallo, wannan tsakanin ɗa da uba ne”
“Idan tayi tsami ma ji, miye sunan in-law ɗin tawa?”
“Da saura Ummi, bata kama hanyar zama in-law ba tukuna, sai mun yi settling abubuwa. Her name is NAMRA...!”
Wani irin faɗuwa gaban Amira yayi har sai da kanta ya tsara.
‘Namra’
Ta maimaita sunan a ranta tana, tuna wacan Namra wacce take ganin ita ce silar shiga ta wannan halin rayuwar. Kamin ta kalli Abdool da ya kai hannu ya ɗauki apple ya fice yana wasa da shi. Ummi kuma ta tashi ta nufi Kitchen, sai ya rage daga Amira sai Haleema ne a falon. Amira ta matsa kusa da Haleema ta dafa kaɗatar.
“Haleema zan shiga ciki, idan Ummi fa faɗi abunda za a girka da ranar nan kya sanar da ni please”
“Okay Sleep well”
Cikin sanyin jiki ta juya ta nufi ɗakin Amal da ya zame mata kamar ɗakinta.
ABDOOL POV.
Cike da zumuɗi ya isa faɗar Mai Martaba, kai tsaye ya wuce part ɗinsa da yake zama. A babban falonsa ya same shi, Hajiya Shafa na haɗa masa abun karyawa, yana ganin ɗansa ya washe haƙura, wanda hakan sam be yi ma uwaegidan Mai Martaba daɗi ba.
Cikin girmamawa Abdool ya gaishe ta, ta amsa masa kamar babu komai sannan ya gaishe da Mai Martaba yana masa kirari.
“Ba wani daɗin baki da zaka min sai da ka fara gaishe ta sannan zaka miƙa min gaisuwa”
Dariya yayi shi da Hajiya Shafa, sannan ya ce
“Ayi haƙuri Mai Martaba, zafi zafina na zo dan labarta maka komai”
“Muma nan ai mun aje maka labari har da ɗuminsa”
Hajiya Shafa ta faɗa. Abdool ya ce
“Tau a fara bani na sha”
“Wannan albishir kuma Mahaifinka zai maka shi”
Ta tashi ta fice tana dariya. Mar Martaba ya miƙa ma Abdool tea da aka haɗa masa shi kuma Abdool ya aje tea a gefe ya shiga haɗa ma Mai Martaba wani yana labarta masa labarin Namra.
Sai kusan Sha ɗaya da rabi suka gama karyawa tare da Mai Martaba yadda Abdool ya zage yana cin abincin ba zaka ce ya ci abinci gurin Ummi ba.
Mai Martaba ya jinjina lamarin Namra sosai kuma ya tausaya mata duk da be ganta, bama abunda ya fi taɓa shi kamar yadda ya ji tana raɓe a gidan wasu bayan kuma uwarta da ubanta suna raye.
“Amman Ina ka haɗu da ita?”
Abdool ya yi shiru yana tunanin faɗawa Mai Martaba gaskiyas lamari.
“Ranka ya daɗe ina binka bashin albishir fa”
“Albishir ɗin ka, zan faɗa maka idan ka samu natsuwa kun kai ƙarshen wannan matsalar”
“Yanzu ya kake ganin za a ɓullowa lamarin?”
Mai Martaba ya gyara zamansa.
“Abunda za mu yi, zan sa a rubuta masa wasiƙa daga nan Masarautar zuwa can inda yake, ai kana da addireshinsa ko?”
“Eh ina da shi, dan nasa an min bincike akan sa”
“Okay zamu saka a aika ma Sarkin Musulmi na sokoto shi kuma zai aika wani ya kai masa wasiƙar”
“Amman Mai Martaba me zai hana ka aika masa kai tsaye?”
“Ai mu sarakuna bama haka, dole ne sai sarkin gari ya san da abunda wani sarkin yake so a garinsa. Musamman babban sarki kamar shi”
“Okay zuwa yaushe za a aika?”
“Yau zamu aika, ina tunanin gobe zata isa gare shi”
Abdool ya ji daɗin haɗin kan da Mai Martaba ya bashi sosai da sosai. Daman ya tsammaci haka, dan ƴasan yana samun goyon bayansa a dukan abunda zai yi.
KALSOOM POV.
*Bayan wata biyu*
“Lallai Mai Martaba kai ne za ka taimaka min wajen dawo da martabar Namra”
“Wacece Namra?”
“Gobe da safe zan dira Katsina zan tabarta maka komai Mai Martaba”
“Allah ya kai mu”
“Amin mu kwana lafiya, Allah ya ƙara mana nisan kwana da lafiya”
Ya aje wayar yana murmushin da shi kaɗai ya san manufarsa.
AMIRA POV.
Tana gama rubuta wasiƙar ta naɗe cikin wata paper, sannan ta ɗauki salati ta saka, ta ta saka ta cikin wani madaidaicin kwali ta yi rolling da wani jan gayenta sai ya fito kamar gift.
Sai da ta gama abunda ta ke sannan ta kwashe komai ta gyara gurin. Saman gado ta koma ta kwanta tana kallon sili kamar mai tunanin wani abu. Haleema ce ta turo kofar ɗakin ta shigo fuskarta ɗauke da damuwa dan ita har ga Allah tausayin Amira take.
Kusa da ita ta zauna tana kallon kwalin dake gefenta.
“Yau duk baki leƙo mu ba? Ko abinci ba ki ci ba”
Sai a lokacin Amira ta tuna rabonta da abincin tun jiya da rana. Sai dai kuma har yanzu bata jin yunwa. Duk ta wani zurma kamar marar lafiya.
Unƙurawa ta yi ta tashi.
“Bana jin yunwa, Dan Allah Haleema ki taimaka min ki kai ni tasha na bada wannan saƙon”
“Saƙon minene Amira?”
“Wasiƙa ce na rubutawa mutumen da ya fara cuta na, wata ƙila idan ya karanta zai gane ina raye har ya wanke, na koma gurin iyayena ko Allah zai sa Yayan ki ya so ni”
Bata damu da sanin abunda yake cikin wasiƙar ba, ta miƙe tsaye
“Okay, bari na ɗauko mayafi na”
Tana ficewa Amira ta tashi cikin rashin kuzari ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta da hawaye ya ɓata ta fito. Wannan karon Hijabi ta ɗauka ta saka, sai ta zauna gefen gado tana kallon kwalin zuciyarta sai bugawa take.
“Mu tafi”
Haleema ta baɗa yayinda ta turo ƙofar ɗakin makulin motarta na hannunta. Da sauri Amira ta ɗauki kwalin suka fice. Maganganu masu daɗi da tausasa zuciya Haleema ta riƙa mata har suka isa tashar. Suna shiga aka riƙa tambayar inda zasu sai Amira ta amsa da
“Motar Sokoto muke nema”
Aka nuna musu, almajira suna haɗawa da gudu ganin haɗaɗiyar mota a zatonsu ko da kayan dako ne. A gafen motoci Haleema ta faka motar suka fito tare, da ƙafa suka ƙarasa kusa da inda ake lodin motar sokoto suka samu direban yana daga gefe zaune yana jiran a gama haɗa masa passengers. Sallama suka fara masa sai ya amsa tare da mutanen da suke gurin.
“Dan Allah saƙo za a kai mu a sokoto”
Cewar Haleema.
“Ok na minene?”
Amira ta dire musu kwalin, kana ta ɗora da.
“Wannan abun za a kai ga addireshin”
Ta ƙarasa tana miƙa masa wata ƴar ƙaramar takardar. Hannu ya kai ya karɓa.
“Okay to zaki bada kuɗin mota, da kuma number wayarki da wanda za a kaiwa saƙon”
“Zan dai baka number na, amman ban da number wanda za'a kaiwa saƙon, shiyasa na rubuta maka addireshin sa, dan Allah ka taimaka min ka kai masa har gida”
“Okay ba matsala, amman gaskiya ko baki yo ba sai kin bada dubu uku, dan za a kai masa har gida ne, kuma kin ga yanayin da ake ciki ba mu cika son karɓar saƙo ba ma”
“Ina zuwa”
Haleema ta faɗa, sai ta juya ta nufi gurin motarta, bata ɗauki lokaci ba ta dawo ta miƙa masa dubu uku ƴan ɗari biyar biyar.
“Gashi amman dan Allah ka tabbatar saƙon ya isa, ki bashi number wayarki so that idan ya kai sai ya kira ya faɗa miki”
Ta ƙarasa tana kallon Amira. Ba musu Amira ta karɓi number wayarsa ta saka a wayarta, sai ta masa flashing number ta ta fito, sai da ta tabbatar yayi saving sannan ta juyo ita da Haleema suka nufi gurin da suka faka motar su.
Haleema ce ta fara shiga sannan Amira, har suka isa gida babu wanda yace da wani uffan, Haleema na wani tunanin na dabam, Amira ma haka har suka isa gida.
Tun kamin su faka motarsu Haleema ta gane yayanta ya dawo, ganin yadda sojojin suka koma cikin natsuwarsu sosai.
“Big bro ya dawo kenan!”
Ta faɗa tana zare key ɗin motar, Amira dai bata ce komai ba, har suka fita motar suka nufi ƙofar shiga falon.
Gabanta ya faɗi sosai lokacin data saka ƙafarta cikin falo, ta yi ido biyu da Abdool.
Abinci yake aunawa a cikinsa yana zubawa Ummi satti, yanayin fuskarsa kawai zaka kalla ka fahimci baya cikin damuwa, dan annuri ne shimfiɗe a fuskarsa.
Cikin sanyin jiki Haleema ta ƙarasa kusa da Ummi dana wasar haƙura, dan tasan laifinta na fita bata faɗawa Ummi ba.
“Daga ina kike?”
Ummi ta tambaya fuskarta babu alamun dariya. Ta ɗan sosa kai tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Ummi dan bata jin zata iya faɗa mata gaskiya.
“Ya Abdool an sauka lafiya”
Amira da ke can gefe Haleema ta miƙawa Abdool gaisuwa. Ba tare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa.
“Lafiya ƙalau”
Sai ya miƙe tsaye yana yi ma Haleema wani kallo.
“Daga Ina kuke?”
“Pizza na ce ta raka ni na siyo kuma ban samu ba”
Ta faɗa tana pretending like she's serious.
“Amman idan zaku je siyen Pizza sai kawai ki kama hanya ku fita without permission?”
“I'm sorry Ummi i promise ba zan sake ba”
“You're very stupid, haka kawai zaki saka kafa ki fita ba tare da kin faɗa ba? Baki san rayuwarku tana cikin haɗari ba? Ba ni kaɗai za a riƙa farauta ba har da ku”
Abdool ya faɗa yana kallonta har handkercheif ɗin dake hannunsa ya faɗi.
“Haba Big Bros Wallahi ba zan ƙara ba, dan Allah ku yi haƙuri”
Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Amira kan idonta na kan Abdool, annurin fuskarsa kawai take kallo, a ɗayan ɓangaren kuma tana Allah-Allah ya manta da handkercheif ɗinsa ta ɗauke, ta yadda zata fi jin daɗin tuna sa idan tana tare da shi.
“Miya hana ki zuwa makaranta?”
Ya tambaya yayinda ya risina ɗaukar handkercheif ɗin.
“Yau ba mu da lacca sai four”
Be sake ce mata komai ba, ya kalli Ummi.
“Zan je gurin Mai Martaba”
“Mu zaka ku? Tun da ka sauka naga ka kira shi fa, akwai abunda kuke shiryawa ko?”
“Kedai Ummi kawai ki sa ido ki yi kallo, wannan tsakanin ɗa da uba ne”
“Idan tayi tsami ma ji, miye sunan in-law ɗin tawa?”
“Da saura Ummi, bata kama hanyar zama in-law ba tukuna, sai mun yi settling abubuwa. Her name is NAMRA...!”
Wani irin faɗuwa gaban Amira yayi har sai da kanta ya tsara.
‘Namra’
Ta maimaita sunan a ranta tana, tuna wacan Namra wacce take ganin ita ce silar shiga ta wannan halin rayuwar. Kamin ta kalli Abdool da ya kai hannu ya ɗauki apple ya fice yana wasa da shi. Ummi kuma ta tashi ta nufi Kitchen, sai ya rage daga Amira sai Haleema ne a falon. Amira ta matsa kusa da Haleema ta dafa kaɗatar.
“Haleema zan shiga ciki, idan Ummi fa faɗi abunda za a girka da ranar nan kya sanar da ni please”
“Okay Sleep well”
Cikin sanyin jiki ta juya ta nufi ɗakin Amal da ya zame mata kamar ɗakinta.
ABDOOL POV.
Cike da zumuɗi ya isa faɗar Mai Martaba, kai tsaye ya wuce part ɗinsa da yake zama. A babban falonsa ya same shi, Hajiya Shafa na haɗa masa abun karyawa, yana ganin ɗansa ya washe haƙura, wanda hakan sam be yi ma uwaegidan Mai Martaba daɗi ba.
Cikin girmamawa Abdool ya gaishe ta, ta amsa masa kamar babu komai sannan ya gaishe da Mai Martaba yana masa kirari.
“Ba wani daɗin baki da zaka min sai da ka fara gaishe ta sannan zaka miƙa min gaisuwa”
Dariya yayi shi da Hajiya Shafa, sannan ya ce
“Ayi haƙuri Mai Martaba, zafi zafina na zo dan labarta maka komai”
“Muma nan ai mun aje maka labari har da ɗuminsa”
Hajiya Shafa ta faɗa. Abdool ya ce
“Tau a fara bani na sha”
“Wannan albishir kuma Mahaifinka zai maka shi”
Ta tashi ta fice tana dariya. Mar Martaba ya miƙa ma Abdool tea da aka haɗa masa shi kuma Abdool ya aje tea a gefe ya shiga haɗa ma Mai Martaba wani yana labarta masa labarin Namra.
Sai kusan Sha ɗaya da rabi suka gama karyawa tare da Mai Martaba yadda Abdool ya zage yana cin abincin ba zaka ce ya ci abinci gurin Ummi ba.
Mai Martaba ya jinjina lamarin Namra sosai kuma ya tausaya mata duk da be ganta, bama abunda ya fi taɓa shi kamar yadda ya ji tana raɓe a gidan wasu bayan kuma uwarta da ubanta suna raye.
“Amman Ina ka haɗu da ita?”
Abdool ya yi shiru yana tunanin faɗawa Mai Martaba gaskiyas lamari.
“Ranka ya daɗe ina binka bashin albishir fa”
“Albishir ɗin ka, zan faɗa maka idan ka samu natsuwa kun kai ƙarshen wannan matsalar”
“Yanzu ya kake ganin za a ɓullowa lamarin?”
Mai Martaba ya gyara zamansa.
“Abunda za mu yi, zan sa a rubuta masa wasiƙa daga nan Masarautar zuwa can inda yake, ai kana da addireshinsa ko?”
“Eh ina da shi, dan nasa an min bincike akan sa”
“Okay zamu saka a aika ma Sarkin Musulmi na sokoto shi kuma zai aika wani ya kai masa wasiƙar”
“Amman Mai Martaba me zai hana ka aika masa kai tsaye?”
“Ai mu sarakuna bama haka, dole ne sai sarkin gari ya san da abunda wani sarkin yake so a garinsa. Musamman babban sarki kamar shi”
“Okay zuwa yaushe za a aika?”
“Yau zamu aika, ina tunanin gobe zata isa gare shi”
Abdool ya ji daɗin haɗin kan da Mai Martaba ya bashi sosai da sosai. Daman ya tsammaci haka, dan ƴasan yana samun goyon bayansa a dukan abunda zai yi.
KALSOOM POV.
*Bayan wata biyu*