Sashe 86
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Be ƙara cewa komai ba ganin Amira ta fito, sai kawai ya jiya ya nufi kowa yana wani shan ƙamshi.
Ko da ta isa har ya tashi motar ita kawao yake jira su wuce. Tana shiga ya fisgi motar kamar baya son ransa har sai da Amira ta tsorata.
Bata ce masa ba, shi ma be ce mata ba haka suka yi ta tafiya har suka isa nasarawa. A bakin gate ɗin gidan yayi parking ya fito yana ƙarewa gidan kallom ganin yadda ya kone.
Yana rufe gambun motar Amira ta buɗe ta fito, sai ya kalleta ya ce
“Ba daɗewa zan yi ba, kina iya zama a cikin kamin na dawo”
Ba musu ta koma cikin motar ta zauna, zuciyarta cike da tunani kala-kala.
Baya tunanin akwai mutane a gidan dan Ummi bata faɗa masa ba, hakan yasa be yi sallama ba ya tura kofar gate ɗin kawai ya shiga ciki. Gaban gidan ya fara dubawa kamin ya zagaya baya, tana nan ya hango mace tana girki a BQ. Hannayensa yasa aljihu ya nufi bq ɗin yana sallamar da kusan shi kaɗai ne zai iya jinta, sai kuma wanda yaga bakinsa ya motsa.
Namra na ganin mutum tayi saurin komawa ciki ta ɗauko hijabinta ta saka sannan ta fito. Ko da ta fito har ya ƙaraso bq ɗin yana ƙare ma bq ɗin kallo dan ita bata yi komai ba.
“Haba Malam waye kai zaka shigo babu sallama”
Dago da dubansa yayi gurin mai maganar. Ganin Namra yasa numfashinsa hijira daga jikinsa ma ɗan wasu daƙiƙu, sannan ya dawo. Be ɗauke idonsa daga gareta ba be kuma kyafta ba, haka ya ƙafe da ido kamar wani hoto. Nan da nan zuciyarsa ta soma rabawa jijiyoyin jikinsa jini da ƙarfi.
Rassss rassss rassss gabansa yake faɗuwa, sai dai kuma ba irin wacan faɗuwar ba, ta tsoro ko fargaba, faɗuwar gaba ne da shi kansa ba zai iya fassara na minene ba.
Ita sai yanzu ta gane ko wanene shi, daman tun ɗazu ta ga ganin kamar fuskar sani, mutume daya bita asibiti. Ƙamshin turaresan ya haddasa mata ciwon kan da bata yi zato ba, daman tun jiya bata cikin daɗin rai.
“Subhanallah malam wannan kallo ya haramta a musulumci”
Daɗin sautinsa yasa shi lumshe ido yana murmushi.
‘A'uzubillahi minal sheidanin rajin’
Ya furta a zuciyarsa yana ƙoƙarin da abunda sheiɗan yake son masa, sannan ya buɗe ido ya haɗe fuska kamar be taba dariya ba.
“Su waye ku?”
“Mu ne waɗanda suka kama hanyar wannan gidan”
Ta amsa masa a gautse.
“Bq kuka kama ko Main house”
“Main house muna ciki aka yi gobara sai muka dawo nan da zama”
“Ina mijin ki?”
“Baya nan ya tafi kasuwa”
“To idan ya zo ki ce an baku one week ku tashi za ayi gyaran gidan”
Gabanta yayi mummunan faɗuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi dan Allah ku gyara babban gidan sai ku bar mana BQ ɗin wallahi ba mu da gurin zuwa idan muka bar nan, dan Allah ku taimaka mana”
Ta haɗe hannayenta idonta na son cika da ƙwalla.
“Da yaushe ake tarar da mijin ki?”
“Da safe ko kuma da dare guraren goma”
“Okay zan zo na yi magana da shi gobe”
“Allah ya kai mu na gode”
Be sake cewa wani abu ba, ya juyo hannayensa zube a aljihu ya fito gidan. Har lokacin Amira na cikin mota zaune tana jiransa, yana shiga motar yayi mata key suka juya. Wannan karon ita ce ta ke ɗan jansa da fira shi kuma jikinsa duk ya mutu baya ma iya amsa mata. yawancin tambayarta akan gidan ne da kuma unguwar, sai kuma yaba garin Katsina da take. Shi dai har suka isa gida sai dai ya ɗaga mata kai kawai.
Ta rigashi fita daga motar, dan yau ranta fes yake ta ta fita tare da sahibinta. Bata tsaya a falo ba sai kawai ya wuce ɗakinta tana ƙoƙarin ɓoye nishaɗinta. Shi kuma ya zauna a falo, kusa da Ummi da take zaune a inda ya barta ɗazu, sai dai wannan karon ita da Shukura ne kuma carrots take gyarawa.
“Har kun dawo?”
“Yeah ai ba wani nisa”
“Kaga gidan ko?”
“Eh duk ya lalace idan aka ce za a gyara shi sai anci kuɗi kam ”
“ Ai dole a gyara shi tun da gidan marainiya ce, a ciro kuɗinta ayi mata gyaran, daman kasan Amal bata da daɗi ta matsa min tuni kamar ni ce na ƙone gidan.Yanzu sai ci nawa idan za a gyara shi?”
“A lot, nawa kika siya mata shi?”
“Ba da kai aka yi cinikin ba, da Alhaji Ƙasimu da Mansur”
“Kai ai bana iya tunawa kin san abu da yawa”
“Nine million aka siye shi”
“Na siya 15 million”
Ummi tayi saurin dubansa.
“Joking abii?”
“I'm serious wallahi na siya”
“Ba zamu siyar ba”
“Saboda me?”
“Muka sani ko zinari aka gani a gidan zaka mana wayo”
Ta faɗa tana tashi ta nufi kitchen, dan ga dukan alamu yai da kanta zata yi girki. Dariya Abdool yayi ya cire hular kansa ya jingina da kujera yana faɗin
“Indai Amal ce ai abu mai sauƙi ne”
Lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya. Babu wacce yake gani sai Namra, da sauri ya buɗe ido ya tashi ta nufi Gardem.
FIVE READ MORE.....🙌🏻
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *57*
Bata taɓa sanin haka jikin da zuciya suke ba idan wani abu marar daɗi ya faru da mutum sai yau. Duk tashin hankalin da ta shiga lokacin da Rafiq ya kamu da ciwo be kai wanda take ciki ba yanzu.
Wannan karon kuka ma yayi ƙaura daga idonta duniyarta sai juya mata take. Gani take kamar mafarki take ba da gaske ba ne Hilal ya miƙa mata wannan takardar.
Miƙewa tayi tsaye sai gata ta dawo xaune saboda rashin ƙarfin jiki, ga wani sanyi da take jin ƙafafunta sun mata.
Wani abu taji yayi mata tsaye a zuciya, hango kanta take a bazarawa, irin rayuwar da tayi ta budurci kuma yanzu ace aurenta ya mutu bayan bata daɗe gidan mijin ba. Takardar ta ƙurawa ido tana auna yadda Mominta zata ji.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shi tai ta maimatawa sannan ta samu ƙarfin jiki, har ta unƙura ta tashi. Durowarta ta buɗe ta ɗauki canjin da yake ciki da Atm ta saka a jikarta tare da takardar ta saka hijabin ta fito falo. Saman kujera ta zauna tana maida numfashi kamar wanda tayi gudun fanfalaƙi. Hannu ta kai ta rufe bakinta saboda kukan daya zo mata gadan-gadan.
Sai dai hakan be hana hawayenta zuba ba, ashe da gaske hawaye suna da zafi, sai a yau ta tabbatar dan yau ta ji hawayenta kamar ruwan zafi.
“Me yasa zan yi kuka akan abunda ba zai sauyu ba? Miyasa zan kuka akan mutumen daya zaɓi rabuwa da ni? Anya Hilal ya cancanci hawaye na?”
Sune tambayoyin da tayi ma kanta a fili, sai dai har ta tashi ta kai bakin ƙofar falon bata samu amsarsu ba. Kamin ta ƙarasa gate ta gyara fuskarta, ta goge idonta da Hijabin gudun kar wani ya gani ya zargi wani abu.
Sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta samu Napep, sai da ta shiga sannan ta faɗa masa inda zai kai ta. Har suka isa estate ɗin su idanuwanta basu daina cika da ƙwallah ba.
Tana biyan Mai Napep ɗin ta shiga gida hawaye na bin fuskarta. Bata samu kowa a falon ba, daman by this time ba zata samu kowa a gidan b Sai Momynta. A saman kujera ta zauna ta haɗe kai da gwuiwa tana kuka. Sautin kukanta ne tashi daga bachi da take ta fito da sauri falo. Ganin Kalsoom ya tashi hankalinta, tasan da maganar kotu da Rashida ta sata amman bata zaton shine zai sa Kalsoom wannan kukan bayan ko kotun ba'a shiga ba. Kusa da ita ta zauna tana ƙoƙarin ɗago kanta.
“Ke miya same ki?”
Ɗagowa tayi cikin kukan ta rumgume Mominta. Girgiza Momi tayi
“Ke ki min magana mana, waya mutu? Ko Rafiq ɗin ne ya mutu?”
“Ni ce Momi Hilal ya sake ni...!”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, me kika masa?”
Kasa magana tayi sai kuka take kamar zata shuɗe, Momi ma hawaye take, ita kanta bata jidaɗin maganar da Kalsoom ta faɗa mata ba, babu mace da zata so auren ƴarta ya mutu sai dole, balle Kalsoom da aka samu aka yi auren daker.
“Ya isa bari kuka, aure rai ne da shi idan lokacin yin sa yayi sai an yi, idan kuma mutuwarsa yayi dole ya mutu, ki kwantar da hankalinki”
Ta faɗa tana share mata hawaye, sai dai kuma ita na ta hawayen ba su daina zuba ba. Daker Momi ta lalaɓa Kalsoom tayi shiru, har ta shiga ɗakin Momi ta kwanta, kanta sai sarawa yake, ga wani ɗan banzan nauyi da yayi mata kamar an ɗora mata dutse, idonta kuma har ji take kamar ƙasa ce a ciki.
Momi kan cikin rashin kuzari tayi girkin yau, sai dai har tayi ta gama bata lasa miyar ba balle ma ta ci abincin. Sai da ta zuba a plate sannan ta kaiwa Kalsoom, banɗaki ta tararda ita tana alwala, dan lokacin ɗaya da rabi tayi, ta daɗe a banɗakin tana aikin kuka sannan ta fito.
“Haba Kalsoom ina ce kin saba da irin wannan jarrabawar, komai fa idan an yi haƙuri za'a ga riba”
Momi ta faɗa tana kallon fuskarta data kumbura. Kusa da ita Kalsoom ta zauna, idonta cike da ƙwalla ta ce
“Momi yanzu duniya zata ɗauka da gaske na aikata, yanzu kowa zai zarge ni akan ni ce ma bawa Rafiq guba, tun da ga shi har Mahaifinsa ya zaɓi rabuwa da ni”
“Amman baki masa bayani ba ne? Ko da yake ba lallai ne ya gamsu ba, saboda gidan daga ke sai yaron ne, kuma abun mamaki ne ace ya sha guba, dole duk wanda ya ji ya zarge ki, ni ba ma abunda ya ɓata min rai kamar zuwa kotun nan da za'ayi”
“Ya ce min babu maganar kotu, ɗazu da zai ba ni takarda”
“Allah ya sauwaƙe, idan auren ku akwai alheri a ciki Allah ya maida shi, idan babu kuma Allah ya kawo miki na ƙwarai, shi kuma ya haɗa shi da matar ƙwarai”
Ko da ta isa har ya tashi motar ita kawao yake jira su wuce. Tana shiga ya fisgi motar kamar baya son ransa har sai da Amira ta tsorata.
Bata ce masa ba, shi ma be ce mata ba haka suka yi ta tafiya har suka isa nasarawa. A bakin gate ɗin gidan yayi parking ya fito yana ƙarewa gidan kallom ganin yadda ya kone.
Yana rufe gambun motar Amira ta buɗe ta fito, sai ya kalleta ya ce
“Ba daɗewa zan yi ba, kina iya zama a cikin kamin na dawo”
Ba musu ta koma cikin motar ta zauna, zuciyarta cike da tunani kala-kala.
Baya tunanin akwai mutane a gidan dan Ummi bata faɗa masa ba, hakan yasa be yi sallama ba ya tura kofar gate ɗin kawai ya shiga ciki. Gaban gidan ya fara dubawa kamin ya zagaya baya, tana nan ya hango mace tana girki a BQ. Hannayensa yasa aljihu ya nufi bq ɗin yana sallamar da kusan shi kaɗai ne zai iya jinta, sai kuma wanda yaga bakinsa ya motsa.
Namra na ganin mutum tayi saurin komawa ciki ta ɗauko hijabinta ta saka sannan ta fito. Ko da ta fito har ya ƙaraso bq ɗin yana ƙare ma bq ɗin kallo dan ita bata yi komai ba.
“Haba Malam waye kai zaka shigo babu sallama”
Dago da dubansa yayi gurin mai maganar. Ganin Namra yasa numfashinsa hijira daga jikinsa ma ɗan wasu daƙiƙu, sannan ya dawo. Be ɗauke idonsa daga gareta ba be kuma kyafta ba, haka ya ƙafe da ido kamar wani hoto. Nan da nan zuciyarsa ta soma rabawa jijiyoyin jikinsa jini da ƙarfi.
Rassss rassss rassss gabansa yake faɗuwa, sai dai kuma ba irin wacan faɗuwar ba, ta tsoro ko fargaba, faɗuwar gaba ne da shi kansa ba zai iya fassara na minene ba.
Ita sai yanzu ta gane ko wanene shi, daman tun ɗazu ta ga ganin kamar fuskar sani, mutume daya bita asibiti. Ƙamshin turaresan ya haddasa mata ciwon kan da bata yi zato ba, daman tun jiya bata cikin daɗin rai.
“Subhanallah malam wannan kallo ya haramta a musulumci”
Daɗin sautinsa yasa shi lumshe ido yana murmushi.
‘A'uzubillahi minal sheidanin rajin’
Ya furta a zuciyarsa yana ƙoƙarin da abunda sheiɗan yake son masa, sannan ya buɗe ido ya haɗe fuska kamar be taba dariya ba.
“Su waye ku?”
“Mu ne waɗanda suka kama hanyar wannan gidan”
Ta amsa masa a gautse.
“Bq kuka kama ko Main house”
“Main house muna ciki aka yi gobara sai muka dawo nan da zama”
“Ina mijin ki?”
“Baya nan ya tafi kasuwa”
“To idan ya zo ki ce an baku one week ku tashi za ayi gyaran gidan”
Gabanta yayi mummunan faɗuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi dan Allah ku gyara babban gidan sai ku bar mana BQ ɗin wallahi ba mu da gurin zuwa idan muka bar nan, dan Allah ku taimaka mana”
Ta haɗe hannayenta idonta na son cika da ƙwalla.
“Da yaushe ake tarar da mijin ki?”
“Da safe ko kuma da dare guraren goma”
“Okay zan zo na yi magana da shi gobe”
“Allah ya kai mu na gode”
Be sake cewa wani abu ba, ya juyo hannayensa zube a aljihu ya fito gidan. Har lokacin Amira na cikin mota zaune tana jiransa, yana shiga motar yayi mata key suka juya. Wannan karon ita ce ta ke ɗan jansa da fira shi kuma jikinsa duk ya mutu baya ma iya amsa mata. yawancin tambayarta akan gidan ne da kuma unguwar, sai kuma yaba garin Katsina da take. Shi dai har suka isa gida sai dai ya ɗaga mata kai kawai.
Ta rigashi fita daga motar, dan yau ranta fes yake ta ta fita tare da sahibinta. Bata tsaya a falo ba sai kawai ya wuce ɗakinta tana ƙoƙarin ɓoye nishaɗinta. Shi kuma ya zauna a falo, kusa da Ummi da take zaune a inda ya barta ɗazu, sai dai wannan karon ita da Shukura ne kuma carrots take gyarawa.
“Har kun dawo?”
“Yeah ai ba wani nisa”
“Kaga gidan ko?”
“Eh duk ya lalace idan aka ce za a gyara shi sai anci kuɗi kam ”
“ Ai dole a gyara shi tun da gidan marainiya ce, a ciro kuɗinta ayi mata gyaran, daman kasan Amal bata da daɗi ta matsa min tuni kamar ni ce na ƙone gidan.Yanzu sai ci nawa idan za a gyara shi?”
“A lot, nawa kika siya mata shi?”
“Ba da kai aka yi cinikin ba, da Alhaji Ƙasimu da Mansur”
“Kai ai bana iya tunawa kin san abu da yawa”
“Nine million aka siye shi”
“Na siya 15 million”
Ummi tayi saurin dubansa.
“Joking abii?”
“I'm serious wallahi na siya”
“Ba zamu siyar ba”
“Saboda me?”
“Muka sani ko zinari aka gani a gidan zaka mana wayo”
Ta faɗa tana tashi ta nufi kitchen, dan ga dukan alamu yai da kanta zata yi girki. Dariya Abdool yayi ya cire hular kansa ya jingina da kujera yana faɗin
“Indai Amal ce ai abu mai sauƙi ne”
Lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya. Babu wacce yake gani sai Namra, da sauri ya buɗe ido ya tashi ta nufi Gardem.
FIVE READ MORE.....🙌🏻
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *57*
Bata taɓa sanin haka jikin da zuciya suke ba idan wani abu marar daɗi ya faru da mutum sai yau. Duk tashin hankalin da ta shiga lokacin da Rafiq ya kamu da ciwo be kai wanda take ciki ba yanzu.
Wannan karon kuka ma yayi ƙaura daga idonta duniyarta sai juya mata take. Gani take kamar mafarki take ba da gaske ba ne Hilal ya miƙa mata wannan takardar.
Miƙewa tayi tsaye sai gata ta dawo xaune saboda rashin ƙarfin jiki, ga wani sanyi da take jin ƙafafunta sun mata.
Wani abu taji yayi mata tsaye a zuciya, hango kanta take a bazarawa, irin rayuwar da tayi ta budurci kuma yanzu ace aurenta ya mutu bayan bata daɗe gidan mijin ba. Takardar ta ƙurawa ido tana auna yadda Mominta zata ji.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shi tai ta maimatawa sannan ta samu ƙarfin jiki, har ta unƙura ta tashi. Durowarta ta buɗe ta ɗauki canjin da yake ciki da Atm ta saka a jikarta tare da takardar ta saka hijabin ta fito falo. Saman kujera ta zauna tana maida numfashi kamar wanda tayi gudun fanfalaƙi. Hannu ta kai ta rufe bakinta saboda kukan daya zo mata gadan-gadan.
Sai dai hakan be hana hawayenta zuba ba, ashe da gaske hawaye suna da zafi, sai a yau ta tabbatar dan yau ta ji hawayenta kamar ruwan zafi.
“Me yasa zan yi kuka akan abunda ba zai sauyu ba? Miyasa zan kuka akan mutumen daya zaɓi rabuwa da ni? Anya Hilal ya cancanci hawaye na?”
Sune tambayoyin da tayi ma kanta a fili, sai dai har ta tashi ta kai bakin ƙofar falon bata samu amsarsu ba. Kamin ta ƙarasa gate ta gyara fuskarta, ta goge idonta da Hijabin gudun kar wani ya gani ya zargi wani abu.
Sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta samu Napep, sai da ta shiga sannan ta faɗa masa inda zai kai ta. Har suka isa estate ɗin su idanuwanta basu daina cika da ƙwallah ba.
Tana biyan Mai Napep ɗin ta shiga gida hawaye na bin fuskarta. Bata samu kowa a falon ba, daman by this time ba zata samu kowa a gidan b Sai Momynta. A saman kujera ta zauna ta haɗe kai da gwuiwa tana kuka. Sautin kukanta ne tashi daga bachi da take ta fito da sauri falo. Ganin Kalsoom ya tashi hankalinta, tasan da maganar kotu da Rashida ta sata amman bata zaton shine zai sa Kalsoom wannan kukan bayan ko kotun ba'a shiga ba. Kusa da ita ta zauna tana ƙoƙarin ɗago kanta.
“Ke miya same ki?”
Ɗagowa tayi cikin kukan ta rumgume Mominta. Girgiza Momi tayi
“Ke ki min magana mana, waya mutu? Ko Rafiq ɗin ne ya mutu?”
“Ni ce Momi Hilal ya sake ni...!”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, me kika masa?”
Kasa magana tayi sai kuka take kamar zata shuɗe, Momi ma hawaye take, ita kanta bata jidaɗin maganar da Kalsoom ta faɗa mata ba, babu mace da zata so auren ƴarta ya mutu sai dole, balle Kalsoom da aka samu aka yi auren daker.
“Ya isa bari kuka, aure rai ne da shi idan lokacin yin sa yayi sai an yi, idan kuma mutuwarsa yayi dole ya mutu, ki kwantar da hankalinki”
Ta faɗa tana share mata hawaye, sai dai kuma ita na ta hawayen ba su daina zuba ba. Daker Momi ta lalaɓa Kalsoom tayi shiru, har ta shiga ɗakin Momi ta kwanta, kanta sai sarawa yake, ga wani ɗan banzan nauyi da yayi mata kamar an ɗora mata dutse, idonta kuma har ji take kamar ƙasa ce a ciki.
Momi kan cikin rashin kuzari tayi girkin yau, sai dai har tayi ta gama bata lasa miyar ba balle ma ta ci abincin. Sai da ta zuba a plate sannan ta kaiwa Kalsoom, banɗaki ta tararda ita tana alwala, dan lokacin ɗaya da rabi tayi, ta daɗe a banɗakin tana aikin kuka sannan ta fito.
“Haba Kalsoom ina ce kin saba da irin wannan jarrabawar, komai fa idan an yi haƙuri za'a ga riba”
Momi ta faɗa tana kallon fuskarta data kumbura. Kusa da ita Kalsoom ta zauna, idonta cike da ƙwalla ta ce
“Momi yanzu duniya zata ɗauka da gaske na aikata, yanzu kowa zai zarge ni akan ni ce ma bawa Rafiq guba, tun da ga shi har Mahaifinsa ya zaɓi rabuwa da ni”
“Amman baki masa bayani ba ne? Ko da yake ba lallai ne ya gamsu ba, saboda gidan daga ke sai yaron ne, kuma abun mamaki ne ace ya sha guba, dole duk wanda ya ji ya zarge ki, ni ba ma abunda ya ɓata min rai kamar zuwa kotun nan da za'ayi”
“Ya ce min babu maganar kotu, ɗazu da zai ba ni takarda”
“Allah ya sauwaƙe, idan auren ku akwai alheri a ciki Allah ya maida shi, idan babu kuma Allah ya kawo miki na ƙwarai, shi kuma ya haɗa shi da matar ƙwarai”