Sashe 28
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tayi saurin sauke kanta, tana mai jin kunya, shi kuma ya watsa mata wani kallo ƙasa-ƙasa, zuciyarsa na ayyana masa abubuwa ƙala-ƙala.
Tashi yayi ya je ya siyo musu kayan tea, ita kuma ta hau gadon ta kwanta saboda ta gaji da yawa. Shi ya haɗa musu tea kamar jiya, har yayi ya gama tana bachi abunta.
Bayan ya kawo kayan tea falo wayarsa tayi ringing, ganin number mahaifiyarsa yasa ta fita daga harabar falo gaba ɗaya, ya nufi can bayan kitchen sannan ya ɗaga wayar.
“Mama ina kwana”
“Lafiya ƙalau Ibrahim ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya ƙalau muke, ina su Amma?”
“Kowa lafiya ƙalau, nace ba a aiko da komai ba ko?”
“Eh kin san ai yau kwana biyu da auren a ɗan jira tukuna kuma ko zasu aiko a nan gida zasu kawo sai ku aiko mana ko?”
“Eh toh haka ne, kasan dashen da aka shiga ne jiya ta aiko mana”
“A ɗan jira dai Mama na san suna kan hanya”
“Toh Allah ya taimaka, amman dai karka yi wasa da kuɗin nan ana kawo su ka samu wata sana'ah babba ka riƙa”
“Haka zan yi ai, ko abokaina haka suke cewa”
“Toh Allah ya taimaka, ina Namra ɗin take ne?”
“Bachi take”
“Toh idan ta tashi a gaishe ta”
Daga haka suka yi sallama, sai ya dawo falon ya cigaba da haɗa tea, sannan ya shiga ya tashe ta.
Sai da tayi brush shima yayi sannan suka dawo falo suka karya. Bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, ita kuma ta shiga kiran wayar Anty Amarya suka gaisa.
Kowa dai da ta kira a gida har Hajiya Barau, sannan ta kira Abbah, kira biyu tayi masa be ɗauka ba saboda sabon layi ne, sai a na uku yayi picking, be wani sake sosai ba sama sama suka gaisa, sannan ta kashe wayar.
Duk tsawon lokacin data ɗauka tana gaisawa da ƴan'gidan su Asim na kusa da ita yana lalabenta, tana aje wayar ya shiga saka mata hannu ƙasanta. Sanin abunda yake nufi da ita yasa ta unƙura ta tana tureshi, cikin yanayin damuwa take masa magana tana son ya fahimceta
“Asim, not now please, Wallahi na gaji kuma har yanzu zafi nake ji”
Kallonta kawai yayi ba dan yana da niyar fasa abunda yake yi ba, idonsa sun rikiɗe sun canja sosai, sai wani numfashi yake.
Ita kanta tasan a yanzu ko da wane yare tayi masa magana ba ganewa zai yi ba, a dole ta ƙyaleshi ya riƙa wasa da ɓangare jikinta, kamin ya jata su koma ɗaki.
Har yayi abunda zai yi gama, be ji ya gamsu ba, ita kuma duk ta ƙosa ya fita ma ya bata ɗakin, da ita kaɗai tasan irin azabar da take ji. Daker ta samu ya rabu da ita, ta tashi a wahale tayi wanka dan ta karanta ta gani kuma ta sha ji a wa'azi ana faɗar cewa ba kyau ka kwanta bachi da janaba a jikinka, ko yaya ne ƙara dai kayi wankan. Ta gasa jikinta sosai da sosai sannan ta fito kamar da rarrafe ta dawo bedroom ɗin. Ko tufafi bata tsaya sawa ba ta hau saman gado, sai bachi.
KALSOOM POV.
A cikin ƴan kwanakin nan kwata-kwata ta rasa gane kan mijinta, duk yabi ya birkice mata kamar ba shi ba, abu kaɗan sai ya hauta da faɗa, ko kuma yayi ta haɗe mata fuska yana nuna baya son tana zama kusa da shi. Sai dai a ɗayan ɓangaren ta samu sassauci gurin Rashida yanzu kan zamansu babu laifi tana ɗan sakewa da ita, har ma tayi mata godiya a wani lokacin.
Yau ta kama weekend Rashida bata da aiki, kuma Doc yau a ɗakinta yake. Sai ta tashi tun da asuba ta haɗa musu breakfast, sai ta gama shirya komai sannan yaje ta tasheshi, ta shiga ɗakin Kalsoom ita ta taso ta.
Da gangan Rashida ta ɗauki dinner set mai plantain da kuma mai kifi ta aza gaban kujerar Kalsoom.
Sannan ta shiga haɗa masa tea dan tuni ya iso gurin yana duba chat ɗinsa na whatsapp. Har Kalsoom ta iso gurin ta zauna be kalli inda take ba, gaisuwar da tayi masa ma can ciki ya amsa mata still be kalle shi ba.
Rashida na lure da yanayin Kalsoom da Hilal zuciyarta cike da shauƙi, sai dai a zahiri sai tayi kamar bata gani ba, ta hidimar haɗa masa tea kawai take.
“Maman Rafiq miƙo masa plantain gata nan a gabanki”
Ta faɗa tana dire masa tea ɗin a gabansa. Ba tare da tunanin komai ba Kalsoom ta ɗauki kwanon ta dire masa a gabansa. Ta miƙa masa birede, sai a lokacin ya samu damar aje wayar har ya kalleta, sannan ya miƙa hannu ya karɓa. Yana buɗe kwanon yaga kifi sai yaja wani dogon tsaki ya kalleta.
“Ace ki miƙo min plantai sai ki bani kifi kifi kika san ina ci ne?”
Bata iya cewa komai ba, sai Rashida ce tayi magana.
“Haba Doc toh ai kwanukan biyu ne bata san wannenen a ciki ba”
Kallonta kawai yayi ya tashi a hasale ya nufi ɗakinsa. Daman haka ya koma mata abu kaɗan yasa shi zuciya indai ita ce tayi masa abu. Rashida taja wani dogon numfashi tana kallon Kalsoom da idonta ke ƙasa
“Tashi ki bi mijinki mana, haka halinsa yake sai kin yi haƙuri, nima fama nake da shi”
Murmushi Kalsoom tayi ta nuna mata kamar ba komai.
“Fushi fa yake da ni, dan nace masa ina buƙatar hutu, shine tun ranar yaƙi ya sauƙo”
Ta faɗa tare da tashi ta nufi ɗakin nasa. Hakan da tace ya ɓata ran Rashida kuma ya dagula mata lissafi.
Kwance ta tarrada da shi ya lumshe ido yana dafe da kai.
“Doc...”
Buɗe ido yayi ya kalleta, sai ya tashi zaune ya zaunar da ita.
“Sorry for what i did earlier, i just that... ”
Sai kuma yayi shiru. Hannunsa ta riƙa tasa yatsunta cikin nasa.
“Doc idan akwai abunda nayi maka kayi haƙuri kasan ɗan'adam ajizi ne, amman be kamata ace kullum kana fushi da ni ba, a zamantakewa kullum tattauna ake so da fahimtar juna, idan har wani abun nake maga kamata yayi ka faɗa min zan gyara inshaAllah”
Rumgumota yayi jikinsa.
“Baki min komai ba, kawai ina abu ne a ciki na mai ƙarfi, irin ii can't control myself when I'm angry at you, I'm sorry too”
Lafewa tayi jikinsa kamar wata mussa, sai toshe hanci take, dan warin turarensa yana son sata a mai. Duk yadda tayi ƙoƙarin daurewa sai ta kasa saboda aman daya ci ƙarfinta, da gudu ta tashi ta nufi bathroom ɗinsa. Sai ya rufa mata baya da sauri yana tambayar lafiya.
Amai ta riƙa kwararawa ba ji ga gani kamar zata amaye hanjinta, gashi komai bata ci ba da safen nan. Har tayi aman ta gama yana riƙe da da ita yana shafa bayanta.
Sai da ta gama ya wanke mata bakinta, sannan ya riƙota suka fito yana mata sannu.
__________________________________________
Share it please I'm busy 🙌
Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 22*
NOT EDITED ⚠️
Yau kusan two weeks kenan, babu gara babu labarinta. Sosai da sosai hakan ya dami Asim, sai dai ya ɓoye maitarsa, be yarda ya nuna mata komai ba. Ya kan yi ƙoƙarin siyo duk wani abu na buƙata wanda za'aci ko ayi amfani da shi a gidan. Sai dai duk tsawon wannan satin biyu Namra a wahale tayi su dan kullum yana manne da ita, bata da wani dogon hutu indai yana gida.
Bayan sun gama cin abinci ya aje Spoon ɗin hannunsa yana sauke ajiyar zuciya. Kallonsa tayi dan ta lura da yadda yanayinsa ya canja.
“Lafiya dai?”
Ya ɗan kalleta kaɗan ya ɗauke kai yana ɗan murmushi, fuskarsa na nuna alamun damuwa.
“Ba komai”
“Haba Hubby ai ni da kai yanzu mun zama ɗaya, ya kamata ace damuwarka ta zama nawa, babu wani ɓoye-ɓoye”
“Wato bana son nayi maganar ne kiyi mata wani ɗauka, wata ƙila ba zaki fahimce ni ba”
“Idan ban fahimce ka, wa kake tunanin zai fahimce ka? A tunanin ka idan ka ɓoye min damuwarka zan jidaɗi ne?”
Tashi yayi daga ginciren da yake ya gyara zamansa yana tsara kalamanta, ta yadda zasu zaunu a ƙwaƙwalwarta.
“Namra ina gudun ki shiga cikin irin rayuwar ta ne, kin min abubuwa da yawa, zuciyana bata da muradi illah na kyautata miki. A kullum tunani ina zan zam sama mana mafita muyi rayuwar jindaɗi, sai dai gaskiya I'm scared”
Sai yayi shiru be ƙarasa ba yana auna yadda kalamansa zasu kamata.
Ita kuma sai ta tambaya zuciyarta cike da shauƙin kalaman nasa.
“Scared of what?”
“Namra ba ni da wani aiki ko sana'ah mai ƙwari da zan iya riƙe ki da ita, ƴan kuɗi dana ke tunanin zasu ishe ni na kama sana'ah da su na kama hanayar gidan nan 50,0000 per year dan kawai na burge ƴan'uwanki da ke kan ki, nasan ke kika bada kuɗin amman naso nayi saving ɗin su dan mu samu wata madafa, sauran da suka rage min kuma gasu muna cin abinci da su kamin Abbah ya yi mana aike”
Ta ɗan ji babu daɗi da kalmar ta fito daga bakinsa, kusan kullum da tunanin take kwana take tashi, na rashin garar da Abbah yayi mata, a tunaninta hakan da Abbah yayi mata ya mata ne dan ta auri Asim, tun da ba haka yake ma sauran ƴaƴansa ba, ita kam ya kasa sai mata girma.
Can ƙasa-ƙasa ta fara magana, zuciyarta cike da rauni.
“Abbah ba zai aiko mana komai ba, da zai aiko da yanzu ya kawo mana ai, sai dai mu yi tunanin wata mafitar”
Sosai da sosai gabansa ya faɗi, kalamanta sun haddasa masa ciwon kai, har zufa na ƙoƙarin karyo masa. Janta yayi jikinsa ya rumgume.
“Toh Allah yayi mana mafita, ai Abbah ya gama mana komai tun da ya yarda na aure ki, Allah dai ya ƙara masa nisan kwana da ƙyaƙƙyawar rayuwa”
“Ameen”
Ta faɗa tana shafa rigarsa.
“Amman yanzu wace sana'ah kake gani yafi? Nifa da zaka bi shawarana da ka koma makaranta, ka cigaba da karatun ka”
Tashi yayi ya je ya siyo musu kayan tea, ita kuma ta hau gadon ta kwanta saboda ta gaji da yawa. Shi ya haɗa musu tea kamar jiya, har yayi ya gama tana bachi abunta.
Bayan ya kawo kayan tea falo wayarsa tayi ringing, ganin number mahaifiyarsa yasa ta fita daga harabar falo gaba ɗaya, ya nufi can bayan kitchen sannan ya ɗaga wayar.
“Mama ina kwana”
“Lafiya ƙalau Ibrahim ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya ƙalau muke, ina su Amma?”
“Kowa lafiya ƙalau, nace ba a aiko da komai ba ko?”
“Eh kin san ai yau kwana biyu da auren a ɗan jira tukuna kuma ko zasu aiko a nan gida zasu kawo sai ku aiko mana ko?”
“Eh toh haka ne, kasan dashen da aka shiga ne jiya ta aiko mana”
“A ɗan jira dai Mama na san suna kan hanya”
“Toh Allah ya taimaka, amman dai karka yi wasa da kuɗin nan ana kawo su ka samu wata sana'ah babba ka riƙa”
“Haka zan yi ai, ko abokaina haka suke cewa”
“Toh Allah ya taimaka, ina Namra ɗin take ne?”
“Bachi take”
“Toh idan ta tashi a gaishe ta”
Daga haka suka yi sallama, sai ya dawo falon ya cigaba da haɗa tea, sannan ya shiga ya tashe ta.
Sai da tayi brush shima yayi sannan suka dawo falo suka karya. Bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, ita kuma ta shiga kiran wayar Anty Amarya suka gaisa.
Kowa dai da ta kira a gida har Hajiya Barau, sannan ta kira Abbah, kira biyu tayi masa be ɗauka ba saboda sabon layi ne, sai a na uku yayi picking, be wani sake sosai ba sama sama suka gaisa, sannan ta kashe wayar.
Duk tsawon lokacin data ɗauka tana gaisawa da ƴan'gidan su Asim na kusa da ita yana lalabenta, tana aje wayar ya shiga saka mata hannu ƙasanta. Sanin abunda yake nufi da ita yasa ta unƙura ta tana tureshi, cikin yanayin damuwa take masa magana tana son ya fahimceta
“Asim, not now please, Wallahi na gaji kuma har yanzu zafi nake ji”
Kallonta kawai yayi ba dan yana da niyar fasa abunda yake yi ba, idonsa sun rikiɗe sun canja sosai, sai wani numfashi yake.
Ita kanta tasan a yanzu ko da wane yare tayi masa magana ba ganewa zai yi ba, a dole ta ƙyaleshi ya riƙa wasa da ɓangare jikinta, kamin ya jata su koma ɗaki.
Har yayi abunda zai yi gama, be ji ya gamsu ba, ita kuma duk ta ƙosa ya fita ma ya bata ɗakin, da ita kaɗai tasan irin azabar da take ji. Daker ta samu ya rabu da ita, ta tashi a wahale tayi wanka dan ta karanta ta gani kuma ta sha ji a wa'azi ana faɗar cewa ba kyau ka kwanta bachi da janaba a jikinka, ko yaya ne ƙara dai kayi wankan. Ta gasa jikinta sosai da sosai sannan ta fito kamar da rarrafe ta dawo bedroom ɗin. Ko tufafi bata tsaya sawa ba ta hau saman gado, sai bachi.
KALSOOM POV.
A cikin ƴan kwanakin nan kwata-kwata ta rasa gane kan mijinta, duk yabi ya birkice mata kamar ba shi ba, abu kaɗan sai ya hauta da faɗa, ko kuma yayi ta haɗe mata fuska yana nuna baya son tana zama kusa da shi. Sai dai a ɗayan ɓangaren ta samu sassauci gurin Rashida yanzu kan zamansu babu laifi tana ɗan sakewa da ita, har ma tayi mata godiya a wani lokacin.
Yau ta kama weekend Rashida bata da aiki, kuma Doc yau a ɗakinta yake. Sai ta tashi tun da asuba ta haɗa musu breakfast, sai ta gama shirya komai sannan yaje ta tasheshi, ta shiga ɗakin Kalsoom ita ta taso ta.
Da gangan Rashida ta ɗauki dinner set mai plantain da kuma mai kifi ta aza gaban kujerar Kalsoom.
Sannan ta shiga haɗa masa tea dan tuni ya iso gurin yana duba chat ɗinsa na whatsapp. Har Kalsoom ta iso gurin ta zauna be kalli inda take ba, gaisuwar da tayi masa ma can ciki ya amsa mata still be kalle shi ba.
Rashida na lure da yanayin Kalsoom da Hilal zuciyarta cike da shauƙi, sai dai a zahiri sai tayi kamar bata gani ba, ta hidimar haɗa masa tea kawai take.
“Maman Rafiq miƙo masa plantain gata nan a gabanki”
Ta faɗa tana dire masa tea ɗin a gabansa. Ba tare da tunanin komai ba Kalsoom ta ɗauki kwanon ta dire masa a gabansa. Ta miƙa masa birede, sai a lokacin ya samu damar aje wayar har ya kalleta, sannan ya miƙa hannu ya karɓa. Yana buɗe kwanon yaga kifi sai yaja wani dogon tsaki ya kalleta.
“Ace ki miƙo min plantai sai ki bani kifi kifi kika san ina ci ne?”
Bata iya cewa komai ba, sai Rashida ce tayi magana.
“Haba Doc toh ai kwanukan biyu ne bata san wannenen a ciki ba”
Kallonta kawai yayi ya tashi a hasale ya nufi ɗakinsa. Daman haka ya koma mata abu kaɗan yasa shi zuciya indai ita ce tayi masa abu. Rashida taja wani dogon numfashi tana kallon Kalsoom da idonta ke ƙasa
“Tashi ki bi mijinki mana, haka halinsa yake sai kin yi haƙuri, nima fama nake da shi”
Murmushi Kalsoom tayi ta nuna mata kamar ba komai.
“Fushi fa yake da ni, dan nace masa ina buƙatar hutu, shine tun ranar yaƙi ya sauƙo”
Ta faɗa tare da tashi ta nufi ɗakin nasa. Hakan da tace ya ɓata ran Rashida kuma ya dagula mata lissafi.
Kwance ta tarrada da shi ya lumshe ido yana dafe da kai.
“Doc...”
Buɗe ido yayi ya kalleta, sai ya tashi zaune ya zaunar da ita.
“Sorry for what i did earlier, i just that... ”
Sai kuma yayi shiru. Hannunsa ta riƙa tasa yatsunta cikin nasa.
“Doc idan akwai abunda nayi maka kayi haƙuri kasan ɗan'adam ajizi ne, amman be kamata ace kullum kana fushi da ni ba, a zamantakewa kullum tattauna ake so da fahimtar juna, idan har wani abun nake maga kamata yayi ka faɗa min zan gyara inshaAllah”
Rumgumota yayi jikinsa.
“Baki min komai ba, kawai ina abu ne a ciki na mai ƙarfi, irin ii can't control myself when I'm angry at you, I'm sorry too”
Lafewa tayi jikinsa kamar wata mussa, sai toshe hanci take, dan warin turarensa yana son sata a mai. Duk yadda tayi ƙoƙarin daurewa sai ta kasa saboda aman daya ci ƙarfinta, da gudu ta tashi ta nufi bathroom ɗinsa. Sai ya rufa mata baya da sauri yana tambayar lafiya.
Amai ta riƙa kwararawa ba ji ga gani kamar zata amaye hanjinta, gashi komai bata ci ba da safen nan. Har tayi aman ta gama yana riƙe da da ita yana shafa bayanta.
Sai da ta gama ya wanke mata bakinta, sannan ya riƙota suka fito yana mata sannu.
__________________________________________
Share it please I'm busy 🙌
Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 22*
NOT EDITED ⚠️
Yau kusan two weeks kenan, babu gara babu labarinta. Sosai da sosai hakan ya dami Asim, sai dai ya ɓoye maitarsa, be yarda ya nuna mata komai ba. Ya kan yi ƙoƙarin siyo duk wani abu na buƙata wanda za'aci ko ayi amfani da shi a gidan. Sai dai duk tsawon wannan satin biyu Namra a wahale tayi su dan kullum yana manne da ita, bata da wani dogon hutu indai yana gida.
Bayan sun gama cin abinci ya aje Spoon ɗin hannunsa yana sauke ajiyar zuciya. Kallonsa tayi dan ta lura da yadda yanayinsa ya canja.
“Lafiya dai?”
Ya ɗan kalleta kaɗan ya ɗauke kai yana ɗan murmushi, fuskarsa na nuna alamun damuwa.
“Ba komai”
“Haba Hubby ai ni da kai yanzu mun zama ɗaya, ya kamata ace damuwarka ta zama nawa, babu wani ɓoye-ɓoye”
“Wato bana son nayi maganar ne kiyi mata wani ɗauka, wata ƙila ba zaki fahimce ni ba”
“Idan ban fahimce ka, wa kake tunanin zai fahimce ka? A tunanin ka idan ka ɓoye min damuwarka zan jidaɗi ne?”
Tashi yayi daga ginciren da yake ya gyara zamansa yana tsara kalamanta, ta yadda zasu zaunu a ƙwaƙwalwarta.
“Namra ina gudun ki shiga cikin irin rayuwar ta ne, kin min abubuwa da yawa, zuciyana bata da muradi illah na kyautata miki. A kullum tunani ina zan zam sama mana mafita muyi rayuwar jindaɗi, sai dai gaskiya I'm scared”
Sai yayi shiru be ƙarasa ba yana auna yadda kalamansa zasu kamata.
Ita kuma sai ta tambaya zuciyarta cike da shauƙin kalaman nasa.
“Scared of what?”
“Namra ba ni da wani aiki ko sana'ah mai ƙwari da zan iya riƙe ki da ita, ƴan kuɗi dana ke tunanin zasu ishe ni na kama sana'ah da su na kama hanayar gidan nan 50,0000 per year dan kawai na burge ƴan'uwanki da ke kan ki, nasan ke kika bada kuɗin amman naso nayi saving ɗin su dan mu samu wata madafa, sauran da suka rage min kuma gasu muna cin abinci da su kamin Abbah ya yi mana aike”
Ta ɗan ji babu daɗi da kalmar ta fito daga bakinsa, kusan kullum da tunanin take kwana take tashi, na rashin garar da Abbah yayi mata, a tunaninta hakan da Abbah yayi mata ya mata ne dan ta auri Asim, tun da ba haka yake ma sauran ƴaƴansa ba, ita kam ya kasa sai mata girma.
Can ƙasa-ƙasa ta fara magana, zuciyarta cike da rauni.
“Abbah ba zai aiko mana komai ba, da zai aiko da yanzu ya kawo mana ai, sai dai mu yi tunanin wata mafitar”
Sosai da sosai gabansa ya faɗi, kalamanta sun haddasa masa ciwon kai, har zufa na ƙoƙarin karyo masa. Janta yayi jikinsa ya rumgume.
“Toh Allah yayi mana mafita, ai Abbah ya gama mana komai tun da ya yarda na aure ki, Allah dai ya ƙara masa nisan kwana da ƙyaƙƙyawar rayuwa”
“Ameen”
Ta faɗa tana shafa rigarsa.
“Amman yanzu wace sana'ah kake gani yafi? Nifa da zaka bi shawarana da ka koma makaranta, ka cigaba da karatun ka”