← Book details Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 173

Sashe 34

Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Allah sarki, Allah ya sauwaƙe, amman duk da haka zan zo da ɗana sai yayi mana takarda guda biyu saboda gudun matsala”

“Ba matsala, kuɗin fa?”

“Kuɗi gaskiya sai zuwa gobe na kawo miki sai na ɗauki gadon, dan yanzu ƙuɗin da suke hannuna ba su wuce ɗari biyu ba”

“Bani haka gobe sai ki kawo min sauran ki ɗauki gadon”

“To ba matsala amman sai kin biyo ni gida na baki ga ban ƴan gidan mu saboda shedu”

Sai da Namra ta bawa Mardiya abincin da za a kai ma Mama sannan ta saka hijabinta ta kulle gidan suka fita tare.

Gida matar suka shiga, ta ƙirgo kuɗin gaban mutanen da suke gidan ta bawa Namra bayan ta faɗa musu yadda suka yi, da Namra tun a gida. Sannan tasa ɗanta ya ɗauko takarda yayi shedu guda biyu ya bata ɗaya ya bawa Namra ɗaya.

Tare da Mardiya Namra ta fito gidan, suka tare napep ta kai su Asibiti. Mardiya ce ta wuce kai musu abincin Namra ta nufi gurin biyan kuɗin magani. Dubu ɗari da talati ta biya na aikin, sannan ta biya na magani suka zo suka ɗibi jininsa suka auna sannan suka tura ta lab gurin siyen jini, tayi sa'ah an samu irin wanda ake so, gora uku ta siyo sannan ta dawo ta kawo musu.

Cikin dubu ɗari biyu, kuɗin daya rage be wuce dubu bakwai da ƴan canji ba. A kasale ta shiga ɗakin da yake, sai ta tararda shi cike ƴan'uwan Asim na Sokoto da Bakori sun zo dubiya.

Cikin far'ah da ƙarfin hali ta gaisa da su, sannan tayi ma Mama ina kwana. Sai kusan azahar wasu suka koma aka bar mutum biyu su wai ba yau zasu ba.
Ganin azahar tayi yasa Namra ta ba Mardiya makulli taje ta girka mata abincin rana, ita kuma ta dawo kusa da Asim ta zauna, ta zuba masa ido kamar ba gobe. Daker ya ɗaga ido ya kalleta ya sake rufewa ji yake kamar ba duniya yake ba.

Ita kuma wani irin tausayinsa take ji take ciwon kamar a jikinta yake.
Uku dai-dai nurses suka shigo suka fita da shi zuwa ɗakin da za'ayi masa aikin.

ABDOOL POV.

Hannu ya kai ya kunna air conditioner dake ɗakin sannan, ya rage tufafin jikinsa, ya buɗe freezer ya ɗauko power horse ya sha.
Sai ya dawo saman sofa ya zauna, yana kallon window. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ya miƙa gurin windowdake garden yana sauraren birds singing.

Yana jindaɗin saurarensu sosai da sosai, hakan yasa lokuta da dama idan ba shi da wani aikin ya kan tare a garden dan kawai sauraren sautin na su.
Hannayensa ya zuba a aljihu ya tashi yana wani irin taku na sarauta da ƙasaita ya nufi window, Peacock ɗin dake ƙarƙashin apple tree yana sha'aninsa ya tsurawa ido. Kamar wanda ya tuno wani abu sai kawai yayi wani ƙayataccen murmushi ya wanda ya sanya dimples ɗinsa fitowa, lumshe ido yayi yana shafa fuskarsa.

“Because of her, half the time I don't even know that I'm smiling, she insult me but i still need to see, who's she?”

Abund ya furta kenan a fili sai kuma ya bawa kansa amsa.

“The Unique one”

Murmushi yayi mai sauti, ya rumgume hannayensa yana ƙara saita tunaninsa.

Taya akayi ya zure haka? Mema ya kai shi kula wata har yayi ƙoƙarin mata magana, shi da bay da lokacin wasu mata. Hannu yasa a aljihun wandonsa na Army, ya ɗauko wayarsa ya kira wata number, bugu ɗaya ya ɗauka.

“Ali ya ake ciki?”

“Naje har gurin shugaban masu Napep ɗin na bincika, sai aka kawo min mutumen yace shi be santa ba kuma a bakin babbar asibitin funtua ya sauke ta, wai yana ganin jinya take”

“So what's the solution?”

“Sir want i think is better mu shiga cikin asibitin mu bincika”

“No”

Ya girgiza kai alamar shawarar bata masa ba, ya ɗan ɗauki dogon lokaci, be ce masa komai ba, ba dan kuma baya da abun cewar ba, sai dan isa da izza.

“Ka cire kuɗin da zai isa, a shirya takeaway da five thousand sai muje mu raba ma Patients ko Allah zai sa mu samu ganinta”

“Okay but Sir Akwai meeting da zaka je gobe Abuja, kuma the next day akwai meeting ɗin Mr President ya shirya za ku yi akan matsalar tsaron nan na Maiduguri da Zamfara”

Lumshe ido yayi ya buɗe.

“I know that, nasan end of this month ina da free days, a cikin wannan rana ku zamu je, sai ka saka mana date”

“Alright Sir zan duba the most expensive free day na ka”

“Good of you”

Sai kawai ya kashe wayar, ya mayar aljihu. Da ƙarfi aka banko ƙofar ɗakinsa, sai kawai yayi murmushi.

“Hey Dude”

Wanda ya kira da sunan ta fito daga cikin labule tana dariya, yarinya matashi wanda ba zata wuce fourteen to sixteen years.

“Yarima Ummi na kiran ka”

Ta faɗa tana taɓa hannayenta. Hannayen nata ya riƙa yana murmushi.

“Dude Yarima has finally found his princess”

Ta zaro ido

“Wow, when? How? Who?”

“At funtua i don't know who's she”

“Is she really cute?”

Wa wara manyan idanuwansa.

“Yeah she's so pretty, she had that diamond eyes, her lips is so cute, i like her face, she's tall, she wearing Hijab and she's black, Dude you know how i love black girls huh?”

“Yes Dude so how are we going to meet her?”

“I don't know, she slap me Dude”

Ya wani ɓata fuska kamar ƙaramin yaro. Itama ta ɓata fuska kamar tayi kuka.

“So heart touching”

“Don't worry i will slap her heart when i have a chance, but i still feel her soft fingers on my cheek”

“ I will be the first one to tell Ummi”

Ta faɗa tana dariya. Sai yayi saurin rufe mata baki

“No Dude wannan sirrin mu ne, no one will ever know”

“Yes I won't tell”

Ta faɗa tana ɗaga hannu sama alamar tayi alƙawari.

“So tell me why Ummi take son gani na?”

“She want you to go and meet Cute Eysha, daughter of Hajiya Saratu”

“What? Please tell her I'm sick”

Har ta buɗe baki sai kuma ta rufe ta saki hannunsa ta fita. Batayi minti biyar da fitar ba yaji alamun shigowar Ummi.
Da sauri ya haye saman gado yaja bedsheet ya lulluɓe ya makore kamar da gaske ba shida lafiya.

“Ai dole ka riƙa ciwo, kullum baka da hutu kai ne agogo sarkin aiki, idan an maka maganar aure kamar ance ka faɗi ka mutu, duk yaran garin nan kace basu maka ba, ko so kake ni da Mai martana mu mutu ba muga auren ka ba?”

Ɗan ɗagowa yayi kaɗan yana pretending like he's really sick.

“Ummi yanzu kuma miye nawa? ”

“Ƴar wajen Hajiya Saratu nace kaje ka gani, tace min jiya ta dawo daga Kaduna”

“Ummi ko na yi aure babu wanda zata zauna da ni, saboda ina da lalura ta rashin lafiya yanzu haka Dr Alex ya ɗora ni akan magani”

Ya faɗa yana ƙoƙarin mayarda ƙaryarsa ta zama gaskiya. Ita kuma sai ta amsa da ƙarfi.

“What?”

Sai kuma ta kalli ƙanwarsa.

“Afrah go and watch your favorite channel”

Sai da suka yi ido biyu da yayan nata sannan ta fice.

ANTY AMARYA POV.

Ji take bata kyautawa Namra ba, idan har bata mata ba babu wanda zai mata sai Allah, soyayya irin ta ƴa da uwa ta hana Anty Amarya ƙyale Namra har sai da tasa Maryam ta tura mata dubu ɗari da Hansi.

A gajiye Maryam ta shigo falon ta zauna kusa da Anty Amarya tana miƙa mata atm ɗin ta.

“Kai yau nasha wahala Wallahi, sai kusan 4 muka tashi lacca, naje back kuma na tararda layi”

“Kin tura mata?”

“Eh but her phone is still switch off ”

“Maybe ta siyar ita ma”

“Kai why not su dawo nan garin? Zama acan zai mata wuya”

“Leave here ita ta so ai, sai taje tayi abunda take ganin yafi mata”

“Amman Anty Namra zata sha wahala tun da tana gudun zuciyar mutane”

Ajiyar zuciya Anty Amarya ta sauke, tana wani nazarin na daban.

_________________________________________

Five words for this chapter... 😻
Waiting for your comments... 😘
Best regards to you all... 💖

CANDY🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

                            Website
www.khadeejacandy.com.ng

This page is for Birthday Girl Salwees. Happy Birthday Dear 💖

*PAGE - 26*

NOT EDITED ⚠️

Hankalin Namra be kwanta ba har sai da aka fito da shi daga ɗakin da aka masa aikin.
Sai suka dawo da shi, ɗakin da yake, anyi aiki cikin nasara da taimakon Allah.

Sai da yamma Mama ta je gidan Namra ita da Hajara dan yin wanka ta kuma ɗan huta, Mardiya Namra ta bawa keys ɗin gidan dan ta taba musu abinci kuma ta taya su zama. Ita kuma ta kwana da Asim a asibitin.

Babu irin inda Mama bata shiga ba a gidan, sai baya kyau gidan take da girmansa. Mardiyace ta faɗa mata Namra ta siyar da gadon har an bata wani abu daga ciki.
Babu irin tsinuwar da Mama bata yi ma iyayen Namra ba, a zatonta sune suka turo mata da kuɗin aiki dana magani, a nan ne Mardiya ta ƙara fayyace mata matar data taimaka ta kawo Asim asibiti ba yar'uwarsu bace, nan ma Mama ta cika da mamaki, dan a zatonta ita yar'uwarsu.

“Kai tirr da wasu mutune Wallahi, wato su babu ruwansu da lamarin mijinta tun da ba ita bace ko? Hmmm ni ban taɓa ganin iyaye irin nata ba, daman ba son auren su ke”

Taja wani godon tsaki sannan ta fito daga ɗakin, ta shiga kitchen ta fito ta shiga ɗayan ɗakin. Mardiya dai na biye da ita har ta gama duba gidan. Shikafa da miya Mardiya ta dafa tare da Hajara.
Washe gari ma wani abincin Mardiya ta sake dafa musu, bayan sun ci ta zuba wanda zasu tafi dashi a asibiti, sannan suka wanka suna cikin shiri Dillaliyar ta zo Mardiya tace mata bata nan, sannan ta rufe gidan suka nufi asibitin.
Chapter 34 · 0% Book details