Sashe 132
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Sunana Hajiya Sadiya kamar yadda ka sani, an haife ni a garin nan, amman ko da na tashi ban san iyayena ba, mahaifina da mahaifiyata duka Allah yayi musu rasuwar tun kamin na mallaki hankalin kai na, dan haka na tashi a gidan kakana Sarkin Katsina na wacan lokacin, na samu gata iya gata a gidan, duk da bani kaɗai bace wacce ake riƙo a gidan, amman saboda ni marainiyace, be yarda ya bar mu mun yi karatu a nan ba, a lokacin govnati na ɗaukar nauyin karatun saboda ana ƙyamar bokon ne, so duk wanda ke da ilmi za a ɗauki nauyinsa zuwa ƙasar waje karatu, Zuwaira da Murja da Sadiq su aka saka a ƙarƙashin govnati ni kuma shi ya biya min a cikin aljihunsa. Dukan mu mun yi karatu, duk da ba ƙasa ɗaya aka kai mu ba, dan ni na zaɓi London ne, su kuma Egypt aka kaisu suka yi karatun lafiya.
Na fi sawa shashanci gaba, saboda farar fatar da nake tare da su, na kan rakasu gurare daban-daban hakan yasa muka shaƙu da su sosai. Su san burina saboda ina yawan faɗa cewar nafi son nafi kowa ɗaukaka a makarantar nan, ranar sai wata take ce mun zata faɗa min wani sirri, zata kai ni inda za'a taimaka min na samu ilmin da ya fi na kowa, kuma na fi kowa ɗaukaka a makarantar. Ban yi musu ba, na biyeta ta sani a cikin wata ƙungiya, ashe ƙungiyar asirice, buƙatata ta biya tabbas, saboda a wannan shekarar ni nayi ta ɗaya a duk faɗin makarantar, daga haka sai abubuwa suka buɗe, duk abunda nake da bukata zan je ne kawai na faɗa kuma sai buƙata ta biya, a lokacin muna meet duk ƙarshen wata, amman lokacin dana ƙare karatun na dawo nan sai suka haɗi ni da manyan da suke abuja, a nan naga manyan mutane, maza da mata a cikin har da manyan ƙasar nan. Duk lokacin da za'ayi meeting ɗin, na kan bar Katsina na je abuja da sunan ganin wata Sister mu ƴar sarki, sai naje meeting idan an gama da kwana biyu na sai na dawo.
Na samu babban aiki a lokacin, nama fi kowa kuɗi a gidan mu, da haka na haɗu da baban su Nabila. Bayan mun yi aure yace baya son aiki, sai na haƙura, a nan su kuma suka soma saka min ƙa'idojin da ban san da su ba a wacan lokacin.
Sun ce min dole ne na riƙa neman mata ƴan'uwana, idan ba haka ba, ba su yarda na fitar da zakka ba. A dole na ɗauki ka'idar mu'amala da mata ƴan'uwana, tun ban saba ba har abun ya zame min jiki, ya koma bana jin daɗi mu'amala da mijina sai mata. Daga baya kuma suka ce suna son a riƙa kawo musu sabbin membobi saboda tsofin ciki suna mutuwa ne, kuma ina son a riƙa yaɗa abun.
A abuja nake zaune da mijina, ɗan haka duk lokacin da naso zuwa kawai nake gurin meeting ɗin ba tare da ya sani ba, wata rana da muka yi meeting sai suka ce suna da buƙatar na Sadaukar musu wani daga cikin iyalaina, ba ni da zaɓi dole na bada mijina, sai ya samu haɗarin mota ya mutu, daga nan kuma sai babban ɗa na, sai mai binsa, sannu-sannu suka cinye min duka ƴaƴana, Nabila ce kawai ta rage min. Shekaran jiya da nace maka zanje birnin keebi ba can naje ba, Abuja na je, gurin meeting ɗin. Yanzu kuma Nabila suke so, ko ɗanta. Ni ko da na bada ita ƙara na bayarda kai na, shiyasa nake son ka taimake ni, ka ceci rayuwata da ta ƴata saboda ita kaɗai ta rage min”
Asim ya sake miƙewa tsaye a karo na biyu.
“Wallahi Allah yana so na, wato da yanzu sai dai ki bada ni? Dan nasan zasu ma iya cewa ki kawo yaron gidanki, ko kuma idan mun yi aure ace ko bada surikin ƴar ki, ai ni duk sun kuɗi na be kai na iya rayuwata ba kuma ni daga yau na barki har a bada wallahi”
“Kar kayi saurin yanke hukuncin Asim kaje ka yi tunani”
“Ba wani tunani da zan yi, salon ki sani cikin mugun hali”
“Da ina da niyar saka ka da na saka tun farkon dana saka tun farko dana fahimci kana da son kuɗi, amman ba kai nake target ba matarka, saboda nasan idan na sata cikin ƙungiyar zasu biya kuɗi mai yawa wata ƙila ma ya iya zama fansar ƴata, amman sai gashi ka saki matarka, da yanzu ace zaka iya kawo min matarka zasu iya ɗaga min ƙafa”
Tsayawa yayi kallonta.
“Indai har Namra zata iya zana fansar ƴarki to zan iya kawo miki ita, bisa sharaɗin zaki bani naira billion uku”
“Wallahi zan baka, kuɗi ba matsala ta bace idan na faɗa maka abunda na tara sai ka haukace, kuma Namra ba kasheta zamu yi ba Wallahi, cikin ƙungiyar kawai za mu sakata”
“Amman taya zan kawo miki ita?”
“Zaka maida aurenka, sannan duk abunda zai biyo baya ya biyo, kuma idan kana so zaka iya auren Nabila”
“Ƴarki kam na yafe, amman Namra zaki sameta kamar yadda kike buƙata”
Ta miƙe tsaye ta shiga ɗakinta bata jima.ba ta fito riƙe da amt ta miƙa masa.
“Akwai milion talatin a ciki kayi amfani da su”
Ya miƙa hannu ya karɓa sannan ya juya ya fice.
TEEMA POV.
Tana kwance saman jikinsa, shi kuma sai faman dannar waya yake yana murmushi. Azatonta dan tana shafa jikinsa yake murmushi, shi kam hankalinsa gaba ɗaya ya tafi kan waya sai faman chating yake da Kalsoom.
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya sannan ya kashe datarsa ya kalleta.
“Bari na leƙa office”
“Okay Allah ya tsare min kai”
“Amin dear. Amm anjima Hajiya tace zata aiko da su Ezzah”
Sam bata ji daɗi ba, duk da tasan dalilinsu aka auro ta, amman bata yarda ta nuna masa ba.
“Kai Amman ko na jidaɗi daman ina ta jiran su zo, Allah kawo su lafiya”
“Amin”
Ya faɗa yana ɗaukar hulal dake saman hannu kujera ya saka a kai.
“Okay I love you”
“Love you too”
Da kallo ta bishi sai da ya fice sannan ta miƙe tsaye.
“Sati uku da aure ace za a ɗauko yara a kawo maka, nifa ba bautarsu na zo yi ba, ko amarci ban gama ci ba za'a haɗa ni da ala ƙai ƙai, yara zaggan-zaggan da su, su riƙa sa maka ido idan ka yi ma miji wani abu, mtsssss”
Taja wani uban tsaki ta wuce bedroom ɗinta. Bata jima ba ta fito ta nufi kitchen, girki ta ɗora sai mita take ranta duk a ɓace, dan har ga Allah bata so a kawo su yanzu ba.
“Daman fa ance wasu uwayen miji ba son suruka suke ba, in banda sheri kin san ina Amarya ɗan Amarcin ma ba za'a bari na yi ba, kai kayi naka lokacin sai kace wani ba zai yi ba, nasan dan su aka auro ni amman ai a bari na ci lokacina, tun da can ba saman ƙaya suke ba, daga zuwanka da ƙurciya zaka fara aikin ƴaƴan kishiya”
Kamar mai faɗa da wani haka ta riƙa zuba surutanta har ta yi girkin ta gama mita take, sai da tasa komai a muhallinsa sannan ta shiga ciki ta yi wanka. Tana fitowa ta shirya cikin yellow atamfa, ta kashe ɗauri ta feshe jikinta da turare sannan ta fito falo ta zauna.
Tana jin tsayawar mota ta ƙara gyara ɗaurin ɗankwalinta, tana zaton ko Hilal sai kawai ta ji mota ta tashi, su Ezzah sun turo ƙofa sun shigo fuskarsu da far'ah bakinsu kuma ƙumshe da sallama.
Ciki-ciki ta amsa musu tana murmushin da be kai zuci ba.
“Maraba da ƴaƴana”
“Momi ina wuni? Momi ina wuni?”
“Lafiya ƙalau”
Sai suka zauna saman kujera. Daga nan bata sake bi ta kansu ba, sai da ta ji motar Hilal sannan ta tashi ta koma tsakiyarsu ta zauna ta jasu jikinta ta rumgume tana murmushi.
“Ku bani labarin Hajiya...”
ABDOOL POV.
Around ten ya sauka Katsina, sai da ya fara biyawa Mai Martaba ya ganshi sannan ya wuce gurin Ummi. Da murmushi ya shiga part ɗin Ummi, kamar yasan ita kaɗaice a falon, dan duk ƙannensa sun tafi makaranta.
“Ummi barka da safe”
Ya taɓe baki tana kallonsa.
“Ni ban ga amfanin wannan hutu naka ba, kullum kai ne yawo ba zama gida, yanzu da aure kake yi wace mace ce zata ɗauki wannan rayuwar”
Kusa da ita ya zauna yana dariya.
“To ai gurin matar na je, yau zan baki labarin komai saboda na samu mafitar matsala ta, amman fa nasha wuya but at the end yau tace min Thank you”
“Kana nan kana wahalar da ƴar mutane ai dole wata ta saka cin kwakwa, tun da ka tagi Amirar nan kuka take, na rasa gane kanta idan kuma na tambaye ta sai tace babu komai, yau ma ce min tayi gida zata je daker na hana ta”
“Ina take?”
“Tana ɗakinta”
Ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin Amal. Yana tura ƙofar ɗakin ta ɗago ta kalleshi sai kuma ta juya,
“Amira can we talk?”
“Maybe Later i need some space”
Ta faɗa da muryarta ta kuka.
“Okay but i just want you to know that i care for you, if you need someone to talk to, i'm downstairs”
Daga haka ya juya ya fice. Ita kuma. Ta fashe da kuka.
*78*
Kusa da Ummi ya sake zama yana kallon tv.
“Tana son ta saka kanta cikin matsala ne kawai Ummi amman tasan ba zan taɓa son ta ba”
“Nasan tana son ka har zuciyarta, amman sam ban yarda da yarinyar nan ba, mutanen da sukayi ƙoƙarin su kashe ka, waya sani ko plan ne aka yi ta yadda idan ta aure ka zata fin jindaɗin kashe ka”
Yayi murmushin gefen baki.
Na fi sawa shashanci gaba, saboda farar fatar da nake tare da su, na kan rakasu gurare daban-daban hakan yasa muka shaƙu da su sosai. Su san burina saboda ina yawan faɗa cewar nafi son nafi kowa ɗaukaka a makarantar nan, ranar sai wata take ce mun zata faɗa min wani sirri, zata kai ni inda za'a taimaka min na samu ilmin da ya fi na kowa, kuma na fi kowa ɗaukaka a makarantar. Ban yi musu ba, na biyeta ta sani a cikin wata ƙungiya, ashe ƙungiyar asirice, buƙatata ta biya tabbas, saboda a wannan shekarar ni nayi ta ɗaya a duk faɗin makarantar, daga haka sai abubuwa suka buɗe, duk abunda nake da bukata zan je ne kawai na faɗa kuma sai buƙata ta biya, a lokacin muna meet duk ƙarshen wata, amman lokacin dana ƙare karatun na dawo nan sai suka haɗi ni da manyan da suke abuja, a nan naga manyan mutane, maza da mata a cikin har da manyan ƙasar nan. Duk lokacin da za'ayi meeting ɗin, na kan bar Katsina na je abuja da sunan ganin wata Sister mu ƴar sarki, sai naje meeting idan an gama da kwana biyu na sai na dawo.
Na samu babban aiki a lokacin, nama fi kowa kuɗi a gidan mu, da haka na haɗu da baban su Nabila. Bayan mun yi aure yace baya son aiki, sai na haƙura, a nan su kuma suka soma saka min ƙa'idojin da ban san da su ba a wacan lokacin.
Sun ce min dole ne na riƙa neman mata ƴan'uwana, idan ba haka ba, ba su yarda na fitar da zakka ba. A dole na ɗauki ka'idar mu'amala da mata ƴan'uwana, tun ban saba ba har abun ya zame min jiki, ya koma bana jin daɗi mu'amala da mijina sai mata. Daga baya kuma suka ce suna son a riƙa kawo musu sabbin membobi saboda tsofin ciki suna mutuwa ne, kuma ina son a riƙa yaɗa abun.
A abuja nake zaune da mijina, ɗan haka duk lokacin da naso zuwa kawai nake gurin meeting ɗin ba tare da ya sani ba, wata rana da muka yi meeting sai suka ce suna da buƙatar na Sadaukar musu wani daga cikin iyalaina, ba ni da zaɓi dole na bada mijina, sai ya samu haɗarin mota ya mutu, daga nan kuma sai babban ɗa na, sai mai binsa, sannu-sannu suka cinye min duka ƴaƴana, Nabila ce kawai ta rage min. Shekaran jiya da nace maka zanje birnin keebi ba can naje ba, Abuja na je, gurin meeting ɗin. Yanzu kuma Nabila suke so, ko ɗanta. Ni ko da na bada ita ƙara na bayarda kai na, shiyasa nake son ka taimake ni, ka ceci rayuwata da ta ƴata saboda ita kaɗai ta rage min”
Asim ya sake miƙewa tsaye a karo na biyu.
“Wallahi Allah yana so na, wato da yanzu sai dai ki bada ni? Dan nasan zasu ma iya cewa ki kawo yaron gidanki, ko kuma idan mun yi aure ace ko bada surikin ƴar ki, ai ni duk sun kuɗi na be kai na iya rayuwata ba kuma ni daga yau na barki har a bada wallahi”
“Kar kayi saurin yanke hukuncin Asim kaje ka yi tunani”
“Ba wani tunani da zan yi, salon ki sani cikin mugun hali”
“Da ina da niyar saka ka da na saka tun farkon dana saka tun farko dana fahimci kana da son kuɗi, amman ba kai nake target ba matarka, saboda nasan idan na sata cikin ƙungiyar zasu biya kuɗi mai yawa wata ƙila ma ya iya zama fansar ƴata, amman sai gashi ka saki matarka, da yanzu ace zaka iya kawo min matarka zasu iya ɗaga min ƙafa”
Tsayawa yayi kallonta.
“Indai har Namra zata iya zana fansar ƴarki to zan iya kawo miki ita, bisa sharaɗin zaki bani naira billion uku”
“Wallahi zan baka, kuɗi ba matsala ta bace idan na faɗa maka abunda na tara sai ka haukace, kuma Namra ba kasheta zamu yi ba Wallahi, cikin ƙungiyar kawai za mu sakata”
“Amman taya zan kawo miki ita?”
“Zaka maida aurenka, sannan duk abunda zai biyo baya ya biyo, kuma idan kana so zaka iya auren Nabila”
“Ƴarki kam na yafe, amman Namra zaki sameta kamar yadda kike buƙata”
Ta miƙe tsaye ta shiga ɗakinta bata jima.ba ta fito riƙe da amt ta miƙa masa.
“Akwai milion talatin a ciki kayi amfani da su”
Ya miƙa hannu ya karɓa sannan ya juya ya fice.
TEEMA POV.
Tana kwance saman jikinsa, shi kuma sai faman dannar waya yake yana murmushi. Azatonta dan tana shafa jikinsa yake murmushi, shi kam hankalinsa gaba ɗaya ya tafi kan waya sai faman chating yake da Kalsoom.
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya sannan ya kashe datarsa ya kalleta.
“Bari na leƙa office”
“Okay Allah ya tsare min kai”
“Amin dear. Amm anjima Hajiya tace zata aiko da su Ezzah”
Sam bata ji daɗi ba, duk da tasan dalilinsu aka auro ta, amman bata yarda ta nuna masa ba.
“Kai Amman ko na jidaɗi daman ina ta jiran su zo, Allah kawo su lafiya”
“Amin”
Ya faɗa yana ɗaukar hulal dake saman hannu kujera ya saka a kai.
“Okay I love you”
“Love you too”
Da kallo ta bishi sai da ya fice sannan ta miƙe tsaye.
“Sati uku da aure ace za a ɗauko yara a kawo maka, nifa ba bautarsu na zo yi ba, ko amarci ban gama ci ba za'a haɗa ni da ala ƙai ƙai, yara zaggan-zaggan da su, su riƙa sa maka ido idan ka yi ma miji wani abu, mtsssss”
Taja wani uban tsaki ta wuce bedroom ɗinta. Bata jima ba ta fito ta nufi kitchen, girki ta ɗora sai mita take ranta duk a ɓace, dan har ga Allah bata so a kawo su yanzu ba.
“Daman fa ance wasu uwayen miji ba son suruka suke ba, in banda sheri kin san ina Amarya ɗan Amarcin ma ba za'a bari na yi ba, kai kayi naka lokacin sai kace wani ba zai yi ba, nasan dan su aka auro ni amman ai a bari na ci lokacina, tun da can ba saman ƙaya suke ba, daga zuwanka da ƙurciya zaka fara aikin ƴaƴan kishiya”
Kamar mai faɗa da wani haka ta riƙa zuba surutanta har ta yi girkin ta gama mita take, sai da tasa komai a muhallinsa sannan ta shiga ciki ta yi wanka. Tana fitowa ta shirya cikin yellow atamfa, ta kashe ɗauri ta feshe jikinta da turare sannan ta fito falo ta zauna.
Tana jin tsayawar mota ta ƙara gyara ɗaurin ɗankwalinta, tana zaton ko Hilal sai kawai ta ji mota ta tashi, su Ezzah sun turo ƙofa sun shigo fuskarsu da far'ah bakinsu kuma ƙumshe da sallama.
Ciki-ciki ta amsa musu tana murmushin da be kai zuci ba.
“Maraba da ƴaƴana”
“Momi ina wuni? Momi ina wuni?”
“Lafiya ƙalau”
Sai suka zauna saman kujera. Daga nan bata sake bi ta kansu ba, sai da ta ji motar Hilal sannan ta tashi ta koma tsakiyarsu ta zauna ta jasu jikinta ta rumgume tana murmushi.
“Ku bani labarin Hajiya...”
ABDOOL POV.
Around ten ya sauka Katsina, sai da ya fara biyawa Mai Martaba ya ganshi sannan ya wuce gurin Ummi. Da murmushi ya shiga part ɗin Ummi, kamar yasan ita kaɗaice a falon, dan duk ƙannensa sun tafi makaranta.
“Ummi barka da safe”
Ya taɓe baki tana kallonsa.
“Ni ban ga amfanin wannan hutu naka ba, kullum kai ne yawo ba zama gida, yanzu da aure kake yi wace mace ce zata ɗauki wannan rayuwar”
Kusa da ita ya zauna yana dariya.
“To ai gurin matar na je, yau zan baki labarin komai saboda na samu mafitar matsala ta, amman fa nasha wuya but at the end yau tace min Thank you”
“Kana nan kana wahalar da ƴar mutane ai dole wata ta saka cin kwakwa, tun da ka tagi Amirar nan kuka take, na rasa gane kanta idan kuma na tambaye ta sai tace babu komai, yau ma ce min tayi gida zata je daker na hana ta”
“Ina take?”
“Tana ɗakinta”
Ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin Amal. Yana tura ƙofar ɗakin ta ɗago ta kalleshi sai kuma ta juya,
“Amira can we talk?”
“Maybe Later i need some space”
Ta faɗa da muryarta ta kuka.
“Okay but i just want you to know that i care for you, if you need someone to talk to, i'm downstairs”
Daga haka ya juya ya fice. Ita kuma. Ta fashe da kuka.
*78*
Kusa da Ummi ya sake zama yana kallon tv.
“Tana son ta saka kanta cikin matsala ne kawai Ummi amman tasan ba zan taɓa son ta ba”
“Nasan tana son ka har zuciyarta, amman sam ban yarda da yarinyar nan ba, mutanen da sukayi ƙoƙarin su kashe ka, waya sani ko plan ne aka yi ta yadda idan ta aure ka zata fin jindaɗin kashe ka”
Yayi murmushin gefen baki.