Sashe 157
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ya ɓoye miki ne kawai ko kuma be san gaskiyar zancen ba, a da mahaifinshi abokin Mai Martaba ne kamin a bashi sarauta, sai dai mahaifinshi yana safarar ƙwayoyi ne daga wata ƙasar ana sakawa cikin kayanshi da yake oder, sai yace musu zai kai kaya kaduna alhalin ƙoyoyine yake safara, babu irin jan kunne da mahaifina be masa ba amman yaƙi ji, ranar da ya shirya dainawa sai ya aika duka kuɗinsa waje ya siyo kayan fasa ƙwairi,wanda sanadin hakan customs suka kama kayan, kuma aka bincika aka gano yana safarar ƙwayoyi sanadin hakan aka maka shi, amman sai yake ganin kamar mahaifina ne ya saka shi a matsalar”
“Amman daman ka san Lamido baka taɓa faɗa min ba?”
“Ban san shi ba Wallahi shi ma kuma be san ni ba, sai a lokacin da nasa aka kawo min shi daga Katsina, a lokacin ina gida ne gurin Ummi, Ummi ce ta ganshi ta gane shi, shi ma kuma ya ganeta bayan ya tafi take bani labari, dan ni ban san anyi abun ba ma, lokacin da aka yi abun ina waje gurin karatu, so duk wasu abokai na Mai Martaba ni ban sansu ba domin ban dawo naija ba sai da na yi digiri na biyu”
Namra ta jinjina lamarin sosai, daga nan zance ya cigaba, har ya ɗauko mata labarin labarin zamansa a England.
*** *** ****
A GURGUJE...
Gyara na musmman Anty tasa ake mata irin wanda ake ma amare, tun daga kan dilka da kuma kayan mata.
Daga Dubai Abbah yayi mata odar furniture aka kawo su ta jirgin sama, saboda jirgin ruwa za a iya ɗaukar watanin basu iso ba, gashi kuma aure ya maso kusa, duk da Mai Martaba yace kar su kashe kuɗinsu hakan be hana Abbah siya mata kaya mai shegen tsada ba dan nemawa ƴarshi mutumci da ƙima a idon manyan mutane.
Ranar da aka kayo lefen Namra ana sauran sati ɗaya, bikin ranar kowa ya sha mamaki, sai dai duk wanɗa ya ji labarin ɗan sarkin Katsina zata aura sai su daina mamakin dan sun sa waye mahaifinsa balle kuma shi ɗan da kansa, an kashe neira a ɓangaren Abbah saboda tarbar lefe yayi duk abunda ya kamata wajen ganin ya kashe kunya.
Bayan kowa ya watse Hajiya Barau da Anty suka zo suna ƙara duba kayan, daga ɗan kunne har ribbon babu wanda aka siya a naija duk daga waje Ummi taje ta ɗawa ɗan lelenta lefe. Akwati ashirin da bakwai ɗan ƙaramin akwatin zinari ma daban ne, motar da aka kawo lefen da ita ba a koma da ita ba wai ita tana cikin lefen, ga kuɗin tsintuwa da ake sakawa a gefen akwati su daloli suka saka. Ko kaɗan wannan be yi ma Anty Amarya daɗi ba, domin ta tsani bidi'a a rayuwarta, dukan wani abun da za'ayi almubazzaranci da kuɗi Anty bata son shi.
“Ai ƙara ma da ba za ayi wani Event ba, da Allah kaɗai yasan iya bidi'ar da za'ayi, shi kesa aure yaƙi yin ƙarƙo, ni wannan abun ba burgeni yake ba”
Hajiya Barau ta yi murmushi tana danne abunda ke zuciyarta.
“Ai ke baki ga komai ba ma, mu da muka je jere mu muka ga abu, kin ga gidan da ya ƙera mata kuwa? Kamar ba Katsina ba, wallahi an kashe kuɗi sosai”
“Uhm Allah ya kyauta”
“Amin ai kinsan su masu abun idan ba sun fitar da kuɗin ba ne sun kashe basa jin sun yi, kuma tun da har Allah ya hore ai ƙara ayi, abunda kawai ba a so a zubar da kuɗin kamar kari haka”
“Ke dai Allah ya kyauta kawai, amman bidi'ah bidi'ah ce”
Haka suka yi ta firarsu suna duba kayan da tsayawa ƙirga ko kala nawa ne ɓata lokaci ne. A daren ranar Abbah ya kira Lamido ya bashi offer kuma ya sanar masa aikinsa ya ƙare a gidan da sunan driving. Ba laifi yayi farinciki duk da ɗayan ɓangaren yana baƙinciki an kasashi. Sai dai matsalar rashin aikin yi ita ta fi damunshi fiye da kowace irin matsala.
RANAR JUMMA'AH...
Da misalin ƙarfe biyu na rana aka ɗaura auren Abdallah Ahmad Mai-doki da Khadija Usman Zamau, a masallacin Muhammadu Maccido da ke Amir Yahaya. Duk wanda ya wuce a gurin sai ya tambaya ɗaurin auren wa ake saboda yadda aka taru sosai, ga manya mutane minister da sarakuna da ɓangaren Mai Martaba, da kuma gwannan Katsina, da na kano wasu kuma basu samu damar zuwa ba suka tura akillansu. Mr Presiden ma Wakiltarsa aka yi, saboda baya ƙasar.
Bayan an ɗaura aure aka yi ƙiyafar cin abinci a Shukura Hotel. a ranar Mai Martaba da muƙarrabansa suka koma Katsina, da dare Mai Martaba yayi nasa liyafar shi da manyan baƙinsa, a faɗarsa da aka sauyawa hallita kamar ba a naija kake ba.
Ta Ɓangaren Namra bayan an ɗaura aure da rana. Da dare suka yi walima, saboda an sauya salo yanzu walimar dare ake, an raba kayanyaki masu ɗubin yawa da burgewa. Sai dai ƴan ɓangaren ango basu halarta ba saboda Ummi ta ce zata yi nata walimar idan an kawo Amarya, saboda wasu haka suke sai idan an kai amarya sannan suke nasu walimar...
KALSOOM POV.
FIVE YEARS LATER...
“Happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday dear Izzah Happy birthday to you”
Tana yanka birthday Cake ɗin suka saka ihu.
“EyyyyyPpppppppp”
Sai kawai tasa dariya ta yanki wani abu daga cake ɗin ta sakawa Kalsoom a baki, Kalsoom ma ta yanka ta saka mata a baki, sannan ta bi sauran mutanen da suke gurin tana feeding the ɗinsu suma suna bata, bayan an yi musu hotuna Kalsoom ta basu guri ita da ƙawayenta su cashe...
Kalsoom ta shigo falo ɗauke da ƴarta Amatullah da ke ta kuccekuccen a barta can ta yi wasa.
“Ba zan barki can ba Amatullah su ture min ke na koma zaune”
Faɗuwa ta yi ƙasa ta fara shureshure da ƙafafunta tana kiran sunan Ezzah.
“Ijca ijca....”
“Easy girl, Ijca yau bata da time ɗin ki casu suke”
Haka ta cigaba da kuka, Kalsoom ta share ta a gurin, ta hau whatsapp tana saka hotonsu a status. Sai ga Rafiq ya shigo da gudu ya shiga kitchen ya ɗauko plate ya fito.
“Kai Plate ɗin nan na Dadyn ku ne, karka fasa min kaya”
“Cake za a sa mana ni da Amatullah”
“Kai mata wayo ka cinye ko..?”
Yasa dariya har da ƙyalƙyatawa, ya saba duk abunda za a saka masa sai yace shi da Amatullah za a saka musu saboda ya cinye ya barta. Sai ga Ezzah ta shigo idonta tab da hawaye kamar ta fasa kuka.
“Anty kin ga Husna wai sai an bata wannan cake ɗin ɗayan, gaba daya, kuma bamu gama hotuna ba”
Kalsoom ta aje wayar hannunta ta riƙe baki.
“Yanzu Husna ce zata riƙa saki kuka gaban abokanki? Ke baki jin kunya su ga idonki ya cika da hawaye? Shekara goma sha hudu ace ƴar shekara uku tana saki ƙwalla gaban friends ɗin ki? Wallahi Izza ki rage wannan shagwaɓar”
Ta turo baki tana matsar ƙwalla.
“Je ki kirata ki ce tazo ga wayata ta yi game”
Ta amsa da to ta fice ita da Rafiq. Tana fita Ulfah ta shigo.
“Anty Momie ta kira?”
“Eh tace ba zata samu damar zuwa ba, yanzu suka taso daga Abuja”
“To Anty ki ce Ezzah ta ba mu cake ɗin mu ai Dady yace saboda mu yasa aka yi cake da yawa”
“Ku ara mata ta yi hoto, ku bari a gama nama, ai ba gudu zai yi ya barku ba”
Ta buga ƙafa tana son kuka.
“A'a ni dai ta bamu abun mu, ko na kira Dady na faɗa masa”
“Duk kika faɗa masa sai na ɓata miki miyasa baki da nasiha ne ke? Kullum ke ce cikin rashin jituwa da ƴar'uwarki haba Ulfah”
“Ai itama bata raga min”
“To bari na ga kin ɓata mata party wallahi na ɓata miki rai”
Ta faɗa saman jikin Kalsoom tana kukan shagwaɓa.
“Yi ta kuka yarinya ki ɓata kwaliyarki”
Sai kawai ta zabura ta kaɓe rigarta ta koma gurin party. Amatullahi ta miƙe da saurinta ta bisu tana tafiyarta ta ta-ta-ta...
[7/27, 9:54 PM] Khadeeja Candy♥: *90*
On Sunday Amarya da muƙarrabanta suka kama hanyar Katsina, ta rigasu isa saboda ta jirgi suka je ita da Maryam da ƴan'uwan Anty Amarya su biyu.
A wani gidan Abdool da ke can bypass suka sauka daman tun kamin su zo Ummi ta yi masa wannna shawarar na su sauka a gidan saboda su samu damar sakewa su huta.
Tun lokacin da Abbah da Anty Amarya da Hajiya Barau suka saka ta gaba suna mata nasiha kan aure, ta fara kuka, sai duk ta ji wani yanayi na daban, kamar lokacin da za ayi aurenta na farin, banbanci wannan ba irin wacan auren ba ne.
Yasa an kawo musu komai daga hotel kama daga abinci har abun sha. Misalin ƙarfe uku Yarima ya kira wata ƙanwar Abbah wacce gwaggo ce gurin Namra ya faɗa mata zai aiko da motocin da zasu shiga ita da Namra da wasu mutun uku aje faɗar Mai Martaba.
Namra na zaune a ɗayan bedroom ɗin tare da Maryam da wasu Cousins ɗinta da Aysha da suka zo tare, gwaggo Ramatu ta shigo tana faɗin.
“Ki shirya angon zai aiko da mota a ɗauke mu muje faɗar mai martaba”
Maryam ta daka tsalle.
“Yeeee kaga daɗin abun malam, mu shiga cikin masarauta muna tinƙaho kowa yayi mana iskanci musa a tsire shi a gari”
Sai duk suka sa dariya, har Namra dake leƙa duniyar gizo. Gwaggo Ramatu ta juya ta fice tana jinjina kai.
Maryam ta nufi babban akwatin Namra da aka zo da shi ta buɗe tana duba irin tufafin da Namra zata saka. Wani tsadadden lace ta ɗauko red color da mayafi ta aje saman gado.
“Raihanatu duba min wannan lace ɗin yayi”
Wacce aka kira da Raihanatu ta miƙe tsaye tana duba lace ɗin.
“Kai wannan ai sai ace matar president ce gaba ɗaya”
“Gaskiya kam wannan lace ɗin yayi kyau sosai”
“Amman daman ka san Lamido baka taɓa faɗa min ba?”
“Ban san shi ba Wallahi shi ma kuma be san ni ba, sai a lokacin da nasa aka kawo min shi daga Katsina, a lokacin ina gida ne gurin Ummi, Ummi ce ta ganshi ta gane shi, shi ma kuma ya ganeta bayan ya tafi take bani labari, dan ni ban san anyi abun ba ma, lokacin da aka yi abun ina waje gurin karatu, so duk wasu abokai na Mai Martaba ni ban sansu ba domin ban dawo naija ba sai da na yi digiri na biyu”
Namra ta jinjina lamarin sosai, daga nan zance ya cigaba, har ya ɗauko mata labarin labarin zamansa a England.
*** *** ****
A GURGUJE...
Gyara na musmman Anty tasa ake mata irin wanda ake ma amare, tun daga kan dilka da kuma kayan mata.
Daga Dubai Abbah yayi mata odar furniture aka kawo su ta jirgin sama, saboda jirgin ruwa za a iya ɗaukar watanin basu iso ba, gashi kuma aure ya maso kusa, duk da Mai Martaba yace kar su kashe kuɗinsu hakan be hana Abbah siya mata kaya mai shegen tsada ba dan nemawa ƴarshi mutumci da ƙima a idon manyan mutane.
Ranar da aka kayo lefen Namra ana sauran sati ɗaya, bikin ranar kowa ya sha mamaki, sai dai duk wanɗa ya ji labarin ɗan sarkin Katsina zata aura sai su daina mamakin dan sun sa waye mahaifinsa balle kuma shi ɗan da kansa, an kashe neira a ɓangaren Abbah saboda tarbar lefe yayi duk abunda ya kamata wajen ganin ya kashe kunya.
Bayan kowa ya watse Hajiya Barau da Anty suka zo suna ƙara duba kayan, daga ɗan kunne har ribbon babu wanda aka siya a naija duk daga waje Ummi taje ta ɗawa ɗan lelenta lefe. Akwati ashirin da bakwai ɗan ƙaramin akwatin zinari ma daban ne, motar da aka kawo lefen da ita ba a koma da ita ba wai ita tana cikin lefen, ga kuɗin tsintuwa da ake sakawa a gefen akwati su daloli suka saka. Ko kaɗan wannan be yi ma Anty Amarya daɗi ba, domin ta tsani bidi'a a rayuwarta, dukan wani abun da za'ayi almubazzaranci da kuɗi Anty bata son shi.
“Ai ƙara ma da ba za ayi wani Event ba, da Allah kaɗai yasan iya bidi'ar da za'ayi, shi kesa aure yaƙi yin ƙarƙo, ni wannan abun ba burgeni yake ba”
Hajiya Barau ta yi murmushi tana danne abunda ke zuciyarta.
“Ai ke baki ga komai ba ma, mu da muka je jere mu muka ga abu, kin ga gidan da ya ƙera mata kuwa? Kamar ba Katsina ba, wallahi an kashe kuɗi sosai”
“Uhm Allah ya kyauta”
“Amin ai kinsan su masu abun idan ba sun fitar da kuɗin ba ne sun kashe basa jin sun yi, kuma tun da har Allah ya hore ai ƙara ayi, abunda kawai ba a so a zubar da kuɗin kamar kari haka”
“Ke dai Allah ya kyauta kawai, amman bidi'ah bidi'ah ce”
Haka suka yi ta firarsu suna duba kayan da tsayawa ƙirga ko kala nawa ne ɓata lokaci ne. A daren ranar Abbah ya kira Lamido ya bashi offer kuma ya sanar masa aikinsa ya ƙare a gidan da sunan driving. Ba laifi yayi farinciki duk da ɗayan ɓangaren yana baƙinciki an kasashi. Sai dai matsalar rashin aikin yi ita ta fi damunshi fiye da kowace irin matsala.
RANAR JUMMA'AH...
Da misalin ƙarfe biyu na rana aka ɗaura auren Abdallah Ahmad Mai-doki da Khadija Usman Zamau, a masallacin Muhammadu Maccido da ke Amir Yahaya. Duk wanda ya wuce a gurin sai ya tambaya ɗaurin auren wa ake saboda yadda aka taru sosai, ga manya mutane minister da sarakuna da ɓangaren Mai Martaba, da kuma gwannan Katsina, da na kano wasu kuma basu samu damar zuwa ba suka tura akillansu. Mr Presiden ma Wakiltarsa aka yi, saboda baya ƙasar.
Bayan an ɗaura aure aka yi ƙiyafar cin abinci a Shukura Hotel. a ranar Mai Martaba da muƙarrabansa suka koma Katsina, da dare Mai Martaba yayi nasa liyafar shi da manyan baƙinsa, a faɗarsa da aka sauyawa hallita kamar ba a naija kake ba.
Ta Ɓangaren Namra bayan an ɗaura aure da rana. Da dare suka yi walima, saboda an sauya salo yanzu walimar dare ake, an raba kayanyaki masu ɗubin yawa da burgewa. Sai dai ƴan ɓangaren ango basu halarta ba saboda Ummi ta ce zata yi nata walimar idan an kawo Amarya, saboda wasu haka suke sai idan an kai amarya sannan suke nasu walimar...
KALSOOM POV.
FIVE YEARS LATER...
“Happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday dear Izzah Happy birthday to you”
Tana yanka birthday Cake ɗin suka saka ihu.
“EyyyyyPpppppppp”
Sai kawai tasa dariya ta yanki wani abu daga cake ɗin ta sakawa Kalsoom a baki, Kalsoom ma ta yanka ta saka mata a baki, sannan ta bi sauran mutanen da suke gurin tana feeding the ɗinsu suma suna bata, bayan an yi musu hotuna Kalsoom ta basu guri ita da ƙawayenta su cashe...
Kalsoom ta shigo falo ɗauke da ƴarta Amatullah da ke ta kuccekuccen a barta can ta yi wasa.
“Ba zan barki can ba Amatullah su ture min ke na koma zaune”
Faɗuwa ta yi ƙasa ta fara shureshure da ƙafafunta tana kiran sunan Ezzah.
“Ijca ijca....”
“Easy girl, Ijca yau bata da time ɗin ki casu suke”
Haka ta cigaba da kuka, Kalsoom ta share ta a gurin, ta hau whatsapp tana saka hotonsu a status. Sai ga Rafiq ya shigo da gudu ya shiga kitchen ya ɗauko plate ya fito.
“Kai Plate ɗin nan na Dadyn ku ne, karka fasa min kaya”
“Cake za a sa mana ni da Amatullah”
“Kai mata wayo ka cinye ko..?”
Yasa dariya har da ƙyalƙyatawa, ya saba duk abunda za a saka masa sai yace shi da Amatullah za a saka musu saboda ya cinye ya barta. Sai ga Ezzah ta shigo idonta tab da hawaye kamar ta fasa kuka.
“Anty kin ga Husna wai sai an bata wannan cake ɗin ɗayan, gaba daya, kuma bamu gama hotuna ba”
Kalsoom ta aje wayar hannunta ta riƙe baki.
“Yanzu Husna ce zata riƙa saki kuka gaban abokanki? Ke baki jin kunya su ga idonki ya cika da hawaye? Shekara goma sha hudu ace ƴar shekara uku tana saki ƙwalla gaban friends ɗin ki? Wallahi Izza ki rage wannan shagwaɓar”
Ta turo baki tana matsar ƙwalla.
“Je ki kirata ki ce tazo ga wayata ta yi game”
Ta amsa da to ta fice ita da Rafiq. Tana fita Ulfah ta shigo.
“Anty Momie ta kira?”
“Eh tace ba zata samu damar zuwa ba, yanzu suka taso daga Abuja”
“To Anty ki ce Ezzah ta ba mu cake ɗin mu ai Dady yace saboda mu yasa aka yi cake da yawa”
“Ku ara mata ta yi hoto, ku bari a gama nama, ai ba gudu zai yi ya barku ba”
Ta buga ƙafa tana son kuka.
“A'a ni dai ta bamu abun mu, ko na kira Dady na faɗa masa”
“Duk kika faɗa masa sai na ɓata miki miyasa baki da nasiha ne ke? Kullum ke ce cikin rashin jituwa da ƴar'uwarki haba Ulfah”
“Ai itama bata raga min”
“To bari na ga kin ɓata mata party wallahi na ɓata miki rai”
Ta faɗa saman jikin Kalsoom tana kukan shagwaɓa.
“Yi ta kuka yarinya ki ɓata kwaliyarki”
Sai kawai ta zabura ta kaɓe rigarta ta koma gurin party. Amatullahi ta miƙe da saurinta ta bisu tana tafiyarta ta ta-ta-ta...
[7/27, 9:54 PM] Khadeeja Candy♥: *90*
On Sunday Amarya da muƙarrabanta suka kama hanyar Katsina, ta rigasu isa saboda ta jirgi suka je ita da Maryam da ƴan'uwan Anty Amarya su biyu.
A wani gidan Abdool da ke can bypass suka sauka daman tun kamin su zo Ummi ta yi masa wannna shawarar na su sauka a gidan saboda su samu damar sakewa su huta.
Tun lokacin da Abbah da Anty Amarya da Hajiya Barau suka saka ta gaba suna mata nasiha kan aure, ta fara kuka, sai duk ta ji wani yanayi na daban, kamar lokacin da za ayi aurenta na farin, banbanci wannan ba irin wacan auren ba ne.
Yasa an kawo musu komai daga hotel kama daga abinci har abun sha. Misalin ƙarfe uku Yarima ya kira wata ƙanwar Abbah wacce gwaggo ce gurin Namra ya faɗa mata zai aiko da motocin da zasu shiga ita da Namra da wasu mutun uku aje faɗar Mai Martaba.
Namra na zaune a ɗayan bedroom ɗin tare da Maryam da wasu Cousins ɗinta da Aysha da suka zo tare, gwaggo Ramatu ta shigo tana faɗin.
“Ki shirya angon zai aiko da mota a ɗauke mu muje faɗar mai martaba”
Maryam ta daka tsalle.
“Yeeee kaga daɗin abun malam, mu shiga cikin masarauta muna tinƙaho kowa yayi mana iskanci musa a tsire shi a gari”
Sai duk suka sa dariya, har Namra dake leƙa duniyar gizo. Gwaggo Ramatu ta juya ta fice tana jinjina kai.
Maryam ta nufi babban akwatin Namra da aka zo da shi ta buɗe tana duba irin tufafin da Namra zata saka. Wani tsadadden lace ta ɗauko red color da mayafi ta aje saman gado.
“Raihanatu duba min wannan lace ɗin yayi”
Wacce aka kira da Raihanatu ta miƙe tsaye tana duba lace ɗin.
“Kai wannan ai sai ace matar president ce gaba ɗaya”
“Gaskiya kam wannan lace ɗin yayi kyau sosai”