Sashe 79
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka ta fito asibitin hawaye na bin fuskarta amman bata damu ba, kamar ma bata san suna zuba ba. Bata iya gani sosai saboda hawayen daya cika idonta, sai dai hakan be hana ta tsayar da Mai a daidaita ba.
Tana shiga be sauke ta ko ina ba sai unguwar su Salma mai Napep ɗin ya sauketa, ɗari biyar ta miƙa masa bata tsaya karɓar canji ba ta smtura gate ɗin gidan ta shiga hawaye na bin fuskarta.
Ganin motar mijin salma yasa ta tsayawa a bakin ƙofar falon ta share hawayenta ta gyara tsayuwar hijabinta sannan ta tura ƙofar ta shiga tana sallama da muryar kuka.
Babu kowa a falon kasancewar yau monday ce yara basu dawo scul ba kuma ita da mijinta suna ɗaki. Saman kujera Kalsoom ta xauna ta dafe kanta tana sauraren hawayen da suke son zubo mata. Ta ɗauki mintuna talatin zuwa talatin da biyar a haka sannan Salma ta fito daga ɗakin mijinta tana dariya. Ganin Kalsoom ya razanata, dan da farko ta zata ko ba ita bace sai daga baya ta yarda Kalsoom ɗin ce jin sheshshekar kukanta. Ƙarasawa tayi ta dafata
“Ke miya same ki”
A maimakon ta yi magana sai kawai ta ƙara fashewa da kuka. Hakan yasa hankalin salma ya tashi sosai, har zauna kusa da ita tana girgiza ta
“Dan Allah ki yi magana ko wane ni ya mutu”
Daker ta samu natsuwar sai ta kanta sannan ta kalli salma ta soma mata bayani ba tare da hawayen sun daina mata zuba ba.
Salma ta girgiza da jin labarin har ta rasa yadda zata fassarashi tun da Kalsoom tace be ci guba ba.
“Kalsoom ko dai ya ci baki sani ba?”
“Wallahi be ci ba, bachi ma yake yi”
“Dole ne ya zarge ki Kalsoom ni kaina zan iya aikata kwatankwacin abinda Hilalya aikata, ba ze iya banbance ƙarya da gaskiya ba a yanzu, wata ƙila ya ci gubar ne ba tare da kin sani ba”
“Ba mu da abinda Rafiq zai yi saurin ɗauka ya ci a yanzu, he's just three years old, ni kuma ba zan dauka abu mai cuta na bashi ba, wallahi ban masa komai ba”
“Ba za ki masa ba Kalsoom ba halin ki ba ne, amman taya haka ta faru”
“Ban sani ba Salma wallahi ban sani ba”
Ta faɗa cikin wani irin kuka mai ban tausayi. Salma ta dafa ƙawarta tana hawaye ita tace
“Rashida bata zo gidan ba?”
“Bata zo ba, tun ranar daya sallameta bata sake zuwa gidan ba, kayanta ma sai daga baya ta turo ƙannenta suka ɗibi wasu”
“Allah kaɗai ya san ko mienen wannan abin. Amman abin akwai ban mamaki”
“Amman dai ɗazu na ji ana kirana a muryar Hilal lokacin dana leƙa ban ga kowa ba, har sau uku, a lokacin ne na ji ƙyalowar Rafiq”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah yasa ba lamarin iska ba ne, kar ace ke aka jefa ya faɗa kan yaron ko kuma tayi ma yaron jifa dan ya mutu ace ke ce”
Kalsoom ta kalleta da sauri
“Ɗan ta ne fa”
“Ko ɗan ta ne fa? Ai zata iya aikatawa, idan zuciyar mutum bata da imani komai zai iya aikatawa”
“Na ji ni zata iya yin amman ba zata iya yi ma ɗanta ba, mu riƙa kyuatata zato Salma”
“Hmmm Allah dai ya kyauta, yanzu ina zaki je?”
“Ni ban sani ba, idan naje gida ban san me zan faɗa musu ba, ba lalle bane suma su yarda da ni”
“Kar ma kije gida a yanzu ki koma ɗakin mijinki”
“Amman yace min basa buƙata a yanzu”
“Komai yace miki tun da be ce kije gida ba karki je, idan kin koma gidan ki sa masa ido shi da yaransa babu ruwanki da sha'aninsu, har sai idan ya saki, amman yanzu idan kika koma gida zai ƙara jin haushin ki ne, ki bashi lokaci ya huce ya fahimci komai shi da kansa zai dawo yayi miki magana”
“Idan kuma na koma gidan ya wulaƙanta ni fa?”
“Ki jira har ya wulaƙanta ki ɗin amman yanzu gaskiya ban baki shawarar zuwa gida ba, Kalsoom ki koma ɗakin mijinki”
“Da nasan haka aure yake da ban yi ba, tun da na shiga gidan kullum da matsalar da take buɗe min sabon shafi, idan kuma ka zauna ba kayi auren ba jama'ah su zage ka, idan kuma auren ya mutu ace ka kaso auro ka dawo ma zaman gida, ba su san matsalar ka ba”
“Haƙuri zaki yi, haka LAMARIN DUNIYA (my previou novel) yake, kowa da yadda Allah ya tsara masa tasa rayuwarwa, no matter what you do how you try you can't escape your destiny and you can't change your past, all what you can do is wait for your future with hope and smiled behind your tears, rayuwar aure kala kala ce kowa wace ta kalar nata jarrabawar idan kika ji wani ma sai kin riƙe ba ki marriage is like going to a restaurant and order your choice from the menu, and then look at neighbouring table n wish you”d ordered that dole ki yi haƙuri babu komai a cikin rayuwar aure sai ƙalubale shiyasa kika ji akan ce kayi haƙuri haƙuri dai, kuma idan kika yi haƙuri tun a duniya sai Allah ya saka miki”
Kuka kawai take, bata iya cewa komai ba har Salma ta gama nusar da ita akan hanyar da take ganin kamar ita ce mafita a gareta.
Sai da tayi sallah la'asar sannan salma ta raka ta ta shiga Napep ta koma gidan mijinta, ba dan ranta yazo ba.
Cikin fargaba da tunani ta koma gidan a zatonta ko Hilal ya dawo, kar ya tambaye ta ina ta fito bata san me zata ce masa ba, tun da ba gida yaje ba. Sai ta tarar be ma dawo ba sai su Izzah da suka lalata falon da shinkafa suka watsar da uniform ɗin su a tsakar falon da scul shoes da bags duk a falon. Saman kujera ta zauna tana sauke ajiyar zuciya. Sai ga yaran sun fito cikin shirin islamiya sun, Ulfah ce taje ta rumgume ta, Izzah kam ko gefenta bata kalla ba ta fice.
“Anty mun dawo baki gida”
“Eh naje wani gurin ne”
Ta faɗa tana murmushin ƙarfin hali idonta duk ya cika da ƙwalla.
“To mun tafi makaranta kina da biyar ki ba ni?”
Ta tambaya tana cizon hijabinta. Naira ashirin Kalsoom ta ciro daga jakarta ta miƙa mata.
“Ki raba ke da Izzah”
“To mun gode”
Ta daka tsalle ta nufi ƙofa. Tana daf da ficewa Kalsoom ta kira, sai ta juyo tana kallon Kalsoom dake hawaye.
“Ki min addu'ah kin ji?”
“To mi zan ce?”
“Kice Allah yayi min mafita”
Sheƙowa tayi da gudu ta dawo ta rumgume Kalsoom tana share mata hawayenta.
“Ki daina kukan zan miki addu'ah i love you”
“I love you too”
Ta sake ta, ta juya da gudu ta fice tana kiran sunan ƴar'uwarta.
“Ezzah jira ni......”
Sai da suka fice sannan Kalsoom taja dogon numfashi ta cire hijabinta ta shiga gyaran falon.
YASMIN POV.
Duk irin jan kunne da kuma gargaɗin da Uxair yayi mata akan karta faɗawa kowa halin da Namra take ciki bata ji ba. Dan ta kada samun sukuni tun lokacin data ga halin da namra take ciki. Abin ya tsaya mata a rai, da ace ba Namra bace da kotu kawai zata saka Asim ta nemawa Namra haƙƙinta, an suna da ƙungiyar data hana cin zafin mata musmman mata hausawa da basa iya magana akan komai.
Daga kotu bata zame ko'ina ba sai gidan Anty. Daga Aisha sai Anty Amarya kawai ta tarar a gidan. Daga Hajiyia Barau har su Maryam sun je walima.
Anty Amarya tayi mamakin ganinta, duk dai ta kan biyo wani lokacin idan Uzair ya kawo ta gaishe da Hajiya Barau, sai dai ba kamar yau ba, dan ta sake sosai kamar ba ita, ta koma Normal kamar yadda take da.
“Yau Yasmin gidan mu? Hajiya ko bata nan”
“Eh Na sani ai, dan nasan zata je walimar Fateema, gurim ki na zo ma”
“Mashallah yau tafiyar tawa ce kenan”
Anty Amarya ta faɗa tana murmushi. Aisha ta dire mata drinks sai ta bar musu falon, daman can tun lokacin data na shiri da Namra jininta be haɗu da Aisha ba balle yanzu da suka koma zaman doya da manja.
Sai da ta sha lemun sai ta fara tunanin ta inda zata fillowa Anty dan bata jin zata iya faɗa mata maganar kai tsaye.
“Na ce when last kika je gurin Namra”
“An daɗe gaskiya tun mijinta na jinya, na so na koma sai tace na yi zamana ai za ta zo, lafiya dai ko?”
“Ayyah nima samina mukaje katsina sai na biya gidan ta”
“Ai ko kin kyauta Yasmin ko ke fa? Amman ace ɗan abu kaɗan dan ya shiga sai taren ku ya ɓace? Yadda kuke da Namra kamar wacce kuka fito ciki ɗaya da ita”
“Ni kai na da nasan haka rayuwar auren Namra zata kasance da ban hana Uzair aurenta ba...”
Jindaɗi da Murmushin dake fuskar Anty Amarya ya ɓata, ba tare da ta ƙarasa fahimtar gun da kalaman Yasmin suka dosa ba.
“Wani abin ne ya faru?”
“Anty da dai kin shirya kin je da kan ki kin ga Namra, kar na zama sheɗan”
“Babu wani Sheɗan Yasmin faɗa min, dan Allah ki faɗa min”
“Anty Namra tana cikin wani hali tana rayuwa irin rayuwar da babu wanda ya taɓa mafarkin zata shige ta, gidan da take ciki na ƙone a bq sune zaune, kuma mijinta ba shi da sana'ar yi, manja da magi take saidawa, kuma ko da naje fuskanta duk ya kumbura da alama dukanta yayi, tayi baƙi ta lalace kamar ba ita....”
Jikin Anty Amarya yayi sanyi sosai, har ta kasa furta kalma daga bakinta, mamakin labarin da Yasmin ta bata take ta sakarwa Yasmin ido tana kallonta har Yasmin ta koma.tunanin wata ƙila Anty bata yarda da maganar ta bane.
“Kishirya kije ki gano ma idon ki dan Allah karki ce ni na faɗa miki”
Tana shiga be sauke ta ko ina ba sai unguwar su Salma mai Napep ɗin ya sauketa, ɗari biyar ta miƙa masa bata tsaya karɓar canji ba ta smtura gate ɗin gidan ta shiga hawaye na bin fuskarta.
Ganin motar mijin salma yasa ta tsayawa a bakin ƙofar falon ta share hawayenta ta gyara tsayuwar hijabinta sannan ta tura ƙofar ta shiga tana sallama da muryar kuka.
Babu kowa a falon kasancewar yau monday ce yara basu dawo scul ba kuma ita da mijinta suna ɗaki. Saman kujera Kalsoom ta xauna ta dafe kanta tana sauraren hawayen da suke son zubo mata. Ta ɗauki mintuna talatin zuwa talatin da biyar a haka sannan Salma ta fito daga ɗakin mijinta tana dariya. Ganin Kalsoom ya razanata, dan da farko ta zata ko ba ita bace sai daga baya ta yarda Kalsoom ɗin ce jin sheshshekar kukanta. Ƙarasawa tayi ta dafata
“Ke miya same ki”
A maimakon ta yi magana sai kawai ta ƙara fashewa da kuka. Hakan yasa hankalin salma ya tashi sosai, har zauna kusa da ita tana girgiza ta
“Dan Allah ki yi magana ko wane ni ya mutu”
Daker ta samu natsuwar sai ta kanta sannan ta kalli salma ta soma mata bayani ba tare da hawayen sun daina mata zuba ba.
Salma ta girgiza da jin labarin har ta rasa yadda zata fassarashi tun da Kalsoom tace be ci guba ba.
“Kalsoom ko dai ya ci baki sani ba?”
“Wallahi be ci ba, bachi ma yake yi”
“Dole ne ya zarge ki Kalsoom ni kaina zan iya aikata kwatankwacin abinda Hilalya aikata, ba ze iya banbance ƙarya da gaskiya ba a yanzu, wata ƙila ya ci gubar ne ba tare da kin sani ba”
“Ba mu da abinda Rafiq zai yi saurin ɗauka ya ci a yanzu, he's just three years old, ni kuma ba zan dauka abu mai cuta na bashi ba, wallahi ban masa komai ba”
“Ba za ki masa ba Kalsoom ba halin ki ba ne, amman taya haka ta faru”
“Ban sani ba Salma wallahi ban sani ba”
Ta faɗa cikin wani irin kuka mai ban tausayi. Salma ta dafa ƙawarta tana hawaye ita tace
“Rashida bata zo gidan ba?”
“Bata zo ba, tun ranar daya sallameta bata sake zuwa gidan ba, kayanta ma sai daga baya ta turo ƙannenta suka ɗibi wasu”
“Allah kaɗai ya san ko mienen wannan abin. Amman abin akwai ban mamaki”
“Amman dai ɗazu na ji ana kirana a muryar Hilal lokacin dana leƙa ban ga kowa ba, har sau uku, a lokacin ne na ji ƙyalowar Rafiq”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah yasa ba lamarin iska ba ne, kar ace ke aka jefa ya faɗa kan yaron ko kuma tayi ma yaron jifa dan ya mutu ace ke ce”
Kalsoom ta kalleta da sauri
“Ɗan ta ne fa”
“Ko ɗan ta ne fa? Ai zata iya aikatawa, idan zuciyar mutum bata da imani komai zai iya aikatawa”
“Na ji ni zata iya yin amman ba zata iya yi ma ɗanta ba, mu riƙa kyuatata zato Salma”
“Hmmm Allah dai ya kyauta, yanzu ina zaki je?”
“Ni ban sani ba, idan naje gida ban san me zan faɗa musu ba, ba lalle bane suma su yarda da ni”
“Kar ma kije gida a yanzu ki koma ɗakin mijinki”
“Amman yace min basa buƙata a yanzu”
“Komai yace miki tun da be ce kije gida ba karki je, idan kin koma gidan ki sa masa ido shi da yaransa babu ruwanki da sha'aninsu, har sai idan ya saki, amman yanzu idan kika koma gida zai ƙara jin haushin ki ne, ki bashi lokaci ya huce ya fahimci komai shi da kansa zai dawo yayi miki magana”
“Idan kuma na koma gidan ya wulaƙanta ni fa?”
“Ki jira har ya wulaƙanta ki ɗin amman yanzu gaskiya ban baki shawarar zuwa gida ba, Kalsoom ki koma ɗakin mijinki”
“Da nasan haka aure yake da ban yi ba, tun da na shiga gidan kullum da matsalar da take buɗe min sabon shafi, idan kuma ka zauna ba kayi auren ba jama'ah su zage ka, idan kuma auren ya mutu ace ka kaso auro ka dawo ma zaman gida, ba su san matsalar ka ba”
“Haƙuri zaki yi, haka LAMARIN DUNIYA (my previou novel) yake, kowa da yadda Allah ya tsara masa tasa rayuwarwa, no matter what you do how you try you can't escape your destiny and you can't change your past, all what you can do is wait for your future with hope and smiled behind your tears, rayuwar aure kala kala ce kowa wace ta kalar nata jarrabawar idan kika ji wani ma sai kin riƙe ba ki marriage is like going to a restaurant and order your choice from the menu, and then look at neighbouring table n wish you”d ordered that dole ki yi haƙuri babu komai a cikin rayuwar aure sai ƙalubale shiyasa kika ji akan ce kayi haƙuri haƙuri dai, kuma idan kika yi haƙuri tun a duniya sai Allah ya saka miki”
Kuka kawai take, bata iya cewa komai ba har Salma ta gama nusar da ita akan hanyar da take ganin kamar ita ce mafita a gareta.
Sai da tayi sallah la'asar sannan salma ta raka ta ta shiga Napep ta koma gidan mijinta, ba dan ranta yazo ba.
Cikin fargaba da tunani ta koma gidan a zatonta ko Hilal ya dawo, kar ya tambaye ta ina ta fito bata san me zata ce masa ba, tun da ba gida yaje ba. Sai ta tarar be ma dawo ba sai su Izzah da suka lalata falon da shinkafa suka watsar da uniform ɗin su a tsakar falon da scul shoes da bags duk a falon. Saman kujera ta zauna tana sauke ajiyar zuciya. Sai ga yaran sun fito cikin shirin islamiya sun, Ulfah ce taje ta rumgume ta, Izzah kam ko gefenta bata kalla ba ta fice.
“Anty mun dawo baki gida”
“Eh naje wani gurin ne”
Ta faɗa tana murmushin ƙarfin hali idonta duk ya cika da ƙwalla.
“To mun tafi makaranta kina da biyar ki ba ni?”
Ta tambaya tana cizon hijabinta. Naira ashirin Kalsoom ta ciro daga jakarta ta miƙa mata.
“Ki raba ke da Izzah”
“To mun gode”
Ta daka tsalle ta nufi ƙofa. Tana daf da ficewa Kalsoom ta kira, sai ta juyo tana kallon Kalsoom dake hawaye.
“Ki min addu'ah kin ji?”
“To mi zan ce?”
“Kice Allah yayi min mafita”
Sheƙowa tayi da gudu ta dawo ta rumgume Kalsoom tana share mata hawayenta.
“Ki daina kukan zan miki addu'ah i love you”
“I love you too”
Ta sake ta, ta juya da gudu ta fice tana kiran sunan ƴar'uwarta.
“Ezzah jira ni......”
Sai da suka fice sannan Kalsoom taja dogon numfashi ta cire hijabinta ta shiga gyaran falon.
YASMIN POV.
Duk irin jan kunne da kuma gargaɗin da Uxair yayi mata akan karta faɗawa kowa halin da Namra take ciki bata ji ba. Dan ta kada samun sukuni tun lokacin data ga halin da namra take ciki. Abin ya tsaya mata a rai, da ace ba Namra bace da kotu kawai zata saka Asim ta nemawa Namra haƙƙinta, an suna da ƙungiyar data hana cin zafin mata musmman mata hausawa da basa iya magana akan komai.
Daga kotu bata zame ko'ina ba sai gidan Anty. Daga Aisha sai Anty Amarya kawai ta tarar a gidan. Daga Hajiyia Barau har su Maryam sun je walima.
Anty Amarya tayi mamakin ganinta, duk dai ta kan biyo wani lokacin idan Uzair ya kawo ta gaishe da Hajiya Barau, sai dai ba kamar yau ba, dan ta sake sosai kamar ba ita, ta koma Normal kamar yadda take da.
“Yau Yasmin gidan mu? Hajiya ko bata nan”
“Eh Na sani ai, dan nasan zata je walimar Fateema, gurim ki na zo ma”
“Mashallah yau tafiyar tawa ce kenan”
Anty Amarya ta faɗa tana murmushi. Aisha ta dire mata drinks sai ta bar musu falon, daman can tun lokacin data na shiri da Namra jininta be haɗu da Aisha ba balle yanzu da suka koma zaman doya da manja.
Sai da ta sha lemun sai ta fara tunanin ta inda zata fillowa Anty dan bata jin zata iya faɗa mata maganar kai tsaye.
“Na ce when last kika je gurin Namra”
“An daɗe gaskiya tun mijinta na jinya, na so na koma sai tace na yi zamana ai za ta zo, lafiya dai ko?”
“Ayyah nima samina mukaje katsina sai na biya gidan ta”
“Ai ko kin kyauta Yasmin ko ke fa? Amman ace ɗan abu kaɗan dan ya shiga sai taren ku ya ɓace? Yadda kuke da Namra kamar wacce kuka fito ciki ɗaya da ita”
“Ni kai na da nasan haka rayuwar auren Namra zata kasance da ban hana Uzair aurenta ba...”
Jindaɗi da Murmushin dake fuskar Anty Amarya ya ɓata, ba tare da ta ƙarasa fahimtar gun da kalaman Yasmin suka dosa ba.
“Wani abin ne ya faru?”
“Anty da dai kin shirya kin je da kan ki kin ga Namra, kar na zama sheɗan”
“Babu wani Sheɗan Yasmin faɗa min, dan Allah ki faɗa min”
“Anty Namra tana cikin wani hali tana rayuwa irin rayuwar da babu wanda ya taɓa mafarkin zata shige ta, gidan da take ciki na ƙone a bq sune zaune, kuma mijinta ba shi da sana'ar yi, manja da magi take saidawa, kuma ko da naje fuskanta duk ya kumbura da alama dukanta yayi, tayi baƙi ta lalace kamar ba ita....”
Jikin Anty Amarya yayi sanyi sosai, har ta kasa furta kalma daga bakinta, mamakin labarin da Yasmin ta bata take ta sakarwa Yasmin ido tana kallonta har Yasmin ta koma.tunanin wata ƙila Anty bata yarda da maganar ta bane.
“Kishirya kije ki gano ma idon ki dan Allah karki ce ni na faɗa miki”