Sashe 106
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A yanayin yadda ta ga Namra yasa ita ma ta furta innalillahi tana riƙa ta.
“Inna waurei”
Ta faɗa da yaren fulatanta tana mai ɗaga murƴa ta yadda Neina zata ji ta. Aiko sai ga Neina cikin ɗakin da gudunta har da ɗayar maƙociyarsu mai ganin sanin abunda yake faruwa, Maryam ma tana bayansu tare da ƙanenta maza.
Neina na ganin halin da Namra take ciki ta yi saurin kora Maryam da ƙanenta da kuma maƙociyar waje, ta sauke ƙyauren ɗakin.
cikin ƙarfin hali ta riƙa Namra, tana ƙoƙarin zame mata uwa a wannan lokacin, aiko nan Namra ta kama hannun Neina ta riƙe gam tana hawaye.
“Sannu ƴata sannu Allah kawo miki sauƙi, uwani ki je ki ɗibo mana lafiya dubu da wasu itatatuwan gidan su Mama a'i”
Neina ta faɗawa Uwani tana kallon Namra cike da tausayawa. Cikin sauri uwani ta tashi ta fita, bata ɗauki lokaci ba sai gata ta shigo da ruwa a kwano daga ta dire gaban Neina daga bisani ta miƙa mata ganyayyakin. A cikin ruwan Neina ta mirza su, ta miƙawa Namra, daker ta ɗan kurɓa kaɗan, sannan Neina ta shafa mata lafiya dubu a goshi, sai ta maida kwanon ta aje gefe da taimakon Uwani suka riƙa ta ta miƙe tsaye.
“Tashi muje banɗaki”
Tana fara takawa jiri ya ɗibeta sai ta rafke a gurin ta faɗi ƙasa. Hakan yasa Neina ta tura ƙofar ɗakin, ta rufe gudun kar wani ya shigo.
Gaba ɗaya idonsa da hankalinsa ya tattara ya koma kan ƙofar ɗakin, baya buƙatar a faɗa masa komai tun shi ba ƙaramin yaro ba ne, tun daga yanayin ihun Namra da ya ji da kuma gayyen da ga Uwani ta samo, yasan abunda yake faruwa. Wani irin tausayinta Namra ne ya lulluɓe masa zuciya, gaba ɗaya ya manta da nasa ciwon, he feel her pain, masu shigo suna masa sannu ma ba jinsu yake ba, sai dai ya amsa masu sama-sama, dan gaba ɗaya hankalinsa yana can, ga masu shigowa sai tambayar Neina suke daga shi har su Maryam babu wanda ya iya furta ga inda take, sai duk suka yi kamar bata cikin gidan. Hankalinsa ya fara tashi ganin an ɗauki lokaci, daga Neina har uwsni babu wanda ya sake leƙowa, ya san duk wani abu da Neina zata mata ba zai kai na asibiti ba.
“Maryam zaki iya zuwa bank ki ciro kuɗi?”
Ya faɗa yana kallon Maryam ɗin dake zaune kusa da shi. Kai ta girgiza masa alamar a'a.
“Okay je gidan su Mustafa ki ga idan yana nan ki ce masa ya je ya samo mota kuma ya ciro min wannan kuɗin sai a kaita asibiti”
Ya miƙa masa takardar kuɗin da Yarima ya bashi na one million. Zuwa tayi ta karɓa sannan ta sakata cikin hijabin dake jikinta ta nufi ƙofar fita. Bata ɗauki lokaci ba sai gata ta dawo sai faman sauri take.
“Baya gida”
“Aro min wayar uwani na aro wayarta na kira shi”
Miƙa masa takardar ta yi sannan ta nufi ɗakin tana buga ƙofar.
Daga can cikin ɗakin Neina ta tambayi waye, sai Maryam ta amsa da.
“Ya Lamido yace Uwani ta aro masa wayarta zai kira mustafa a kai Namra asibiti”
“Ai ba sai anje asibiti ba, Allah ya kawo mata sauƙi”
Buɗe ƙofar Neina ta yi, sai ga Namra tana takawa a hankali Uwani na riƙe da ita an ɗaura mata zane saman wani zane suka fito. Kallo ɗaya Lamido ya yi mata ya ɗauke kai be sake kallon inda take ba, har suka shige banɗaki.
Har cikin ransa yake aiyana irin zafin da Namra ta ji, a take wani irin tausayinta ya lulluɓe masa zuciya, idan kuma ya tuna irin rayuwar da ta fito ciki sai yaji kamar ya zubar mata da ƙwalla.
Uwani ce ta taimaka mata wajen gyara jikinta, sannan ta fito ta ɗauki kuɗi cikin jakar Namra ya aika Maryam ta siyo mata Pad, sai ta bi ta gidan maƙotansu ta karɓo mata bashin pant guda huɗu hannu Sadiya mai haja.
Neina ta gyara ɗakin sam kamar ba ayi komai ba, sannan taje ta ɗora mata ruwan wanka masu ɗan ɗumi ta kai mata banɗakin ki. A nan ne uwani ta bar mata banɗakin dan ta yi wanka.
Ta ɗan samu ƙarfin jikinta lokacin da ta yi wanka ta saka pad sannan ta ɗauki zanen da Uwani ta ɗora mata saman ƙofar banɗakin ta ɗaura ta saka hujabi, ta ɗan ɗauki lokaci zaune a banɗakin sannan ta unƙura ta fito. Da sauri uwani ta zo ta riƙa ta suka nufi ɗayan ɗakin da su Maryam suke kwana.
Saman katifar ta kwanta idonta tab da hawaye, tausayin kanta take ji irin ƙaddarar dake faɗa mata ɗaya bayan ɗaya, idan ta fita wannan sai kuma wannan. Bata da tabbacin cikin ya zube gaba ɗaya amman a yadda taga tsare tsaren jini bata zaton akwai abunda ya yi saura a cikinta. Bata bari Uwani taga hawayen da suka zubo mata ba, har sai da ta fita sannan tasa hannu ta shafa cikinta, tana tuna dalilin barin gidan Asim saboda cikin da yanzu babu shi, kuma bata da madafa, dan ba zai yiyu ta zo ta zauna musu a gida haka nan kawai ba, sai dai har yanzu tana tsoron komawa gurin Abbah, to tace masa me? Mutumen daya ce kar tayo fushi ma balle kuma saki ya shiga tsakaninta da Asim.
“Ba adili ba ne”
Ta furta a fili zuciyarta cike da ƙololon baƙinciki, tana tuna irin hallacin da tayi masa yayi mata wannan sakamakon.
Kai kawai take iya girgizawa tana tuna yadda ta rabu komai nata saboda shi, shi kuma a yau ya butulce mata. Dafata da Maryam tayi ne yasa ta dawo daga duniyar tunanin da take.
“Ki yi haƙuri Allah zai sake baki wani”
Kai ta ɗaga mata, tana mata kallon wacan Maryam ɗin ƙanwarta.
“Haka ne, babu abunda bata faɗa min ba, amman na ƙi na yarda na riƙa ƙaryata ta, yau gashi na ga komai daman duk wanda ya ƙi ji ba ya ƙi gani ba”
Da kuka ta ƙarasa maganar kamar wanda bata cikin hayyacinta. Maryam ta girgiza ta.
“Namra lafiya kike kuwa?”
Da sauri ta ɗaga mata kai tana ƙoƙarin share hawayanta.
“Lafiya ta ƙalau”
“Tau ga Maltina nan Ya yace ki sha da madara, mustafa zai karɓo kuɗi a kai ki asibiti”
Ta faɗa tana dire mata gwangwanin maltina guda biyu da madara.
“Ba sai an kai ni asibiti ba, na gode sosai Allah ya saka muku da alheri”
“Amin”
Maryam ɗin ta miƙe tsaye ta bar mata ɗakin. Dawowa tayi gurin da Neina take zaune da Uwani da Lamido, suke zaune ta zauna tana faɗin.
“Tace wai ba sai an kaita asibiti ba, ta gode Allah ya saka mana”
“A'a ba za'a barta haka ba kam, bari dai mustafa ya dawo”
“Ai taji sauƙi Lamido ko ba a kai ta ba, ko minene a cikinta be nina ba”
Neina ta faɗa, Lamido ya kaɗa kai.
“Ƙara dai aje asibiti nan ba zasu rasa abunda zasu mata ba”
“Kuɗin zaka ɗauka ka kashe kuma? Lamido kana ganin Napep ɗin nan taka ta lalace an baka ka siya wani ka samu na jari sai kuma ka ce zaka kashe”
“Haba ai kuɗin yayi yawan da ba zan iya kashesu duka a maganin baiwar Allah nan ba, kuma ko duka za a kashe mata wallahi zan iya badawa, kai ko Napep ɗin ce zan iya siyarwa dan nemaw yarinyar nan lafiya, wallahi mugun tausayi take ba ni”
Daga Uwani har Neina kallon juna suke da mamaki. Maryam ce ma tayi ƙoƙarin magana.
“Lallai Yaya kana tausayin yarinyar nan, Allah dai yasa labarin gaskiya ta ba mu dan kasan duniya yanzu yadda take”
“Amman ta miki kama da wacce zata baki labarin ƙarya? Haba Mairo ki duba yanayinta mana”
Har Neina zata yi magana sai ga Mustafa ya shigo, sai kawai ta sauya maganar da amsa masa sallamarsa. Kusa da abokinsa ya zauna yana bashi labarin yadda suka yi a bank.
“Wallahi akwai layi sosai, kuma naga rashin lafiya ne shiyasa sai nace bari na dawo sai ayi amfani da abunda yake aljihuna in yado idan aka ciro kuɗin sai na ɗauka, kuma kasan manyan kuɗi ne ba zan iya zuwa ni kaɗai ba, kar abiyo ni”
Duk da Lamido baya jin dariya hakan be hana shi darawa ba.
“Wallahi kai dai Mustafa kamar baka yi boko ba, ko da yake karatun naka iya diploma ya tsaya, amman miliyan ɗaya indai ƴan dubu dubu ne ai ba wasu kuɗi ba ne”
Neina ta girgiza kai.
“A a nan Alhaji Isa ba dubu ɗari ya zo dasu gida akan haka aka kashe shi balle mai miliyan ɗaya, ni tun ranar da Allah ya yi ni ban taɓa ganin dubu ɗari biyar a idona ba, balle kuma miliyan ɗaya”
Mustafa ya amsa.
“Wallahi fa ai zamani ne ya riga da ya lalace shiyasa komai sai an yi kafa kafa da shi”
“Allah dai ya shirya mana, ko bana ma son ana faɗar an fashi kuɗi har haka da yawa”
Cewar Neina tana miƙewa tsaye. Uwani ta ce
“Ai babu wanda ya sani idan ba mustafa ba, tun da ba mu faɗawa kowa ba”
“Allah dai ya tsare mu”
Duk suka amsa da Amin har Maryam dake ƙoƙarin tashi ita da Uwani su basu guri.
Bayan sun wuce Mustafa ya kalli Lamido.
“Wallahi babu wanda ya faɗa min haɗarin nan da ka yi in ba dan daka kira ni ba”
“Toh ai ba wani abun daɗi ba ne balle a riƙa yayatawa, kuma ba a daɗe da yin abun ba, Allah ma dai ya tsare”
“Allah ya ƙara tsarewa, amman dai wannan ɗan sarki ko sarki zan ce Allah be yi shi da rowa ba har miliyan ɗaya! Kamar wanda be san zafin kuɗi ba”
“Ya za'ayi ya san zafin kuɗi? Iyayensu suna kawashe kuɗin ƙasa, yanzu dai idan ka fita ka biya ka biya bilya kuɗin maltina da madara na aika am karɓo mata”
“Okay maganar asibitin fa?”
“Tace ba sai an jibe kuma naga kamar Neina bata son aje, ƙara mu ɗan saurara tukuna”
“Okay yayi Allah bata lafiya, amman ƴar'uwar ku ce ko? Naga kamar baƙuwar fuska ce”
“Inna waurei”
Ta faɗa da yaren fulatanta tana mai ɗaga murƴa ta yadda Neina zata ji ta. Aiko sai ga Neina cikin ɗakin da gudunta har da ɗayar maƙociyarsu mai ganin sanin abunda yake faruwa, Maryam ma tana bayansu tare da ƙanenta maza.
Neina na ganin halin da Namra take ciki ta yi saurin kora Maryam da ƙanenta da kuma maƙociyar waje, ta sauke ƙyauren ɗakin.
cikin ƙarfin hali ta riƙa Namra, tana ƙoƙarin zame mata uwa a wannan lokacin, aiko nan Namra ta kama hannun Neina ta riƙe gam tana hawaye.
“Sannu ƴata sannu Allah kawo miki sauƙi, uwani ki je ki ɗibo mana lafiya dubu da wasu itatatuwan gidan su Mama a'i”
Neina ta faɗawa Uwani tana kallon Namra cike da tausayawa. Cikin sauri uwani ta tashi ta fita, bata ɗauki lokaci ba sai gata ta shigo da ruwa a kwano daga ta dire gaban Neina daga bisani ta miƙa mata ganyayyakin. A cikin ruwan Neina ta mirza su, ta miƙawa Namra, daker ta ɗan kurɓa kaɗan, sannan Neina ta shafa mata lafiya dubu a goshi, sai ta maida kwanon ta aje gefe da taimakon Uwani suka riƙa ta ta miƙe tsaye.
“Tashi muje banɗaki”
Tana fara takawa jiri ya ɗibeta sai ta rafke a gurin ta faɗi ƙasa. Hakan yasa Neina ta tura ƙofar ɗakin, ta rufe gudun kar wani ya shigo.
Gaba ɗaya idonsa da hankalinsa ya tattara ya koma kan ƙofar ɗakin, baya buƙatar a faɗa masa komai tun shi ba ƙaramin yaro ba ne, tun daga yanayin ihun Namra da ya ji da kuma gayyen da ga Uwani ta samo, yasan abunda yake faruwa. Wani irin tausayinta Namra ne ya lulluɓe masa zuciya, gaba ɗaya ya manta da nasa ciwon, he feel her pain, masu shigo suna masa sannu ma ba jinsu yake ba, sai dai ya amsa masu sama-sama, dan gaba ɗaya hankalinsa yana can, ga masu shigowa sai tambayar Neina suke daga shi har su Maryam babu wanda ya iya furta ga inda take, sai duk suka yi kamar bata cikin gidan. Hankalinsa ya fara tashi ganin an ɗauki lokaci, daga Neina har uwsni babu wanda ya sake leƙowa, ya san duk wani abu da Neina zata mata ba zai kai na asibiti ba.
“Maryam zaki iya zuwa bank ki ciro kuɗi?”
Ya faɗa yana kallon Maryam ɗin dake zaune kusa da shi. Kai ta girgiza masa alamar a'a.
“Okay je gidan su Mustafa ki ga idan yana nan ki ce masa ya je ya samo mota kuma ya ciro min wannan kuɗin sai a kaita asibiti”
Ya miƙa masa takardar kuɗin da Yarima ya bashi na one million. Zuwa tayi ta karɓa sannan ta sakata cikin hijabin dake jikinta ta nufi ƙofar fita. Bata ɗauki lokaci ba sai gata ta dawo sai faman sauri take.
“Baya gida”
“Aro min wayar uwani na aro wayarta na kira shi”
Miƙa masa takardar ta yi sannan ta nufi ɗakin tana buga ƙofar.
Daga can cikin ɗakin Neina ta tambayi waye, sai Maryam ta amsa da.
“Ya Lamido yace Uwani ta aro masa wayarta zai kira mustafa a kai Namra asibiti”
“Ai ba sai anje asibiti ba, Allah ya kawo mata sauƙi”
Buɗe ƙofar Neina ta yi, sai ga Namra tana takawa a hankali Uwani na riƙe da ita an ɗaura mata zane saman wani zane suka fito. Kallo ɗaya Lamido ya yi mata ya ɗauke kai be sake kallon inda take ba, har suka shige banɗaki.
Har cikin ransa yake aiyana irin zafin da Namra ta ji, a take wani irin tausayinta ya lulluɓe masa zuciya, idan kuma ya tuna irin rayuwar da ta fito ciki sai yaji kamar ya zubar mata da ƙwalla.
Uwani ce ta taimaka mata wajen gyara jikinta, sannan ta fito ta ɗauki kuɗi cikin jakar Namra ya aika Maryam ta siyo mata Pad, sai ta bi ta gidan maƙotansu ta karɓo mata bashin pant guda huɗu hannu Sadiya mai haja.
Neina ta gyara ɗakin sam kamar ba ayi komai ba, sannan taje ta ɗora mata ruwan wanka masu ɗan ɗumi ta kai mata banɗakin ki. A nan ne uwani ta bar mata banɗakin dan ta yi wanka.
Ta ɗan samu ƙarfin jikinta lokacin da ta yi wanka ta saka pad sannan ta ɗauki zanen da Uwani ta ɗora mata saman ƙofar banɗakin ta ɗaura ta saka hujabi, ta ɗan ɗauki lokaci zaune a banɗakin sannan ta unƙura ta fito. Da sauri uwani ta zo ta riƙa ta suka nufi ɗayan ɗakin da su Maryam suke kwana.
Saman katifar ta kwanta idonta tab da hawaye, tausayin kanta take ji irin ƙaddarar dake faɗa mata ɗaya bayan ɗaya, idan ta fita wannan sai kuma wannan. Bata da tabbacin cikin ya zube gaba ɗaya amman a yadda taga tsare tsaren jini bata zaton akwai abunda ya yi saura a cikinta. Bata bari Uwani taga hawayen da suka zubo mata ba, har sai da ta fita sannan tasa hannu ta shafa cikinta, tana tuna dalilin barin gidan Asim saboda cikin da yanzu babu shi, kuma bata da madafa, dan ba zai yiyu ta zo ta zauna musu a gida haka nan kawai ba, sai dai har yanzu tana tsoron komawa gurin Abbah, to tace masa me? Mutumen daya ce kar tayo fushi ma balle kuma saki ya shiga tsakaninta da Asim.
“Ba adili ba ne”
Ta furta a fili zuciyarta cike da ƙololon baƙinciki, tana tuna irin hallacin da tayi masa yayi mata wannan sakamakon.
Kai kawai take iya girgizawa tana tuna yadda ta rabu komai nata saboda shi, shi kuma a yau ya butulce mata. Dafata da Maryam tayi ne yasa ta dawo daga duniyar tunanin da take.
“Ki yi haƙuri Allah zai sake baki wani”
Kai ta ɗaga mata, tana mata kallon wacan Maryam ɗin ƙanwarta.
“Haka ne, babu abunda bata faɗa min ba, amman na ƙi na yarda na riƙa ƙaryata ta, yau gashi na ga komai daman duk wanda ya ƙi ji ba ya ƙi gani ba”
Da kuka ta ƙarasa maganar kamar wanda bata cikin hayyacinta. Maryam ta girgiza ta.
“Namra lafiya kike kuwa?”
Da sauri ta ɗaga mata kai tana ƙoƙarin share hawayanta.
“Lafiya ta ƙalau”
“Tau ga Maltina nan Ya yace ki sha da madara, mustafa zai karɓo kuɗi a kai ki asibiti”
Ta faɗa tana dire mata gwangwanin maltina guda biyu da madara.
“Ba sai an kai ni asibiti ba, na gode sosai Allah ya saka muku da alheri”
“Amin”
Maryam ɗin ta miƙe tsaye ta bar mata ɗakin. Dawowa tayi gurin da Neina take zaune da Uwani da Lamido, suke zaune ta zauna tana faɗin.
“Tace wai ba sai an kaita asibiti ba, ta gode Allah ya saka mana”
“A'a ba za'a barta haka ba kam, bari dai mustafa ya dawo”
“Ai taji sauƙi Lamido ko ba a kai ta ba, ko minene a cikinta be nina ba”
Neina ta faɗa, Lamido ya kaɗa kai.
“Ƙara dai aje asibiti nan ba zasu rasa abunda zasu mata ba”
“Kuɗin zaka ɗauka ka kashe kuma? Lamido kana ganin Napep ɗin nan taka ta lalace an baka ka siya wani ka samu na jari sai kuma ka ce zaka kashe”
“Haba ai kuɗin yayi yawan da ba zan iya kashesu duka a maganin baiwar Allah nan ba, kuma ko duka za a kashe mata wallahi zan iya badawa, kai ko Napep ɗin ce zan iya siyarwa dan nemaw yarinyar nan lafiya, wallahi mugun tausayi take ba ni”
Daga Uwani har Neina kallon juna suke da mamaki. Maryam ce ma tayi ƙoƙarin magana.
“Lallai Yaya kana tausayin yarinyar nan, Allah dai yasa labarin gaskiya ta ba mu dan kasan duniya yanzu yadda take”
“Amman ta miki kama da wacce zata baki labarin ƙarya? Haba Mairo ki duba yanayinta mana”
Har Neina zata yi magana sai ga Mustafa ya shigo, sai kawai ta sauya maganar da amsa masa sallamarsa. Kusa da abokinsa ya zauna yana bashi labarin yadda suka yi a bank.
“Wallahi akwai layi sosai, kuma naga rashin lafiya ne shiyasa sai nace bari na dawo sai ayi amfani da abunda yake aljihuna in yado idan aka ciro kuɗin sai na ɗauka, kuma kasan manyan kuɗi ne ba zan iya zuwa ni kaɗai ba, kar abiyo ni”
Duk da Lamido baya jin dariya hakan be hana shi darawa ba.
“Wallahi kai dai Mustafa kamar baka yi boko ba, ko da yake karatun naka iya diploma ya tsaya, amman miliyan ɗaya indai ƴan dubu dubu ne ai ba wasu kuɗi ba ne”
Neina ta girgiza kai.
“A a nan Alhaji Isa ba dubu ɗari ya zo dasu gida akan haka aka kashe shi balle mai miliyan ɗaya, ni tun ranar da Allah ya yi ni ban taɓa ganin dubu ɗari biyar a idona ba, balle kuma miliyan ɗaya”
Mustafa ya amsa.
“Wallahi fa ai zamani ne ya riga da ya lalace shiyasa komai sai an yi kafa kafa da shi”
“Allah dai ya shirya mana, ko bana ma son ana faɗar an fashi kuɗi har haka da yawa”
Cewar Neina tana miƙewa tsaye. Uwani ta ce
“Ai babu wanda ya sani idan ba mustafa ba, tun da ba mu faɗawa kowa ba”
“Allah dai ya tsare mu”
Duk suka amsa da Amin har Maryam dake ƙoƙarin tashi ita da Uwani su basu guri.
Bayan sun wuce Mustafa ya kalli Lamido.
“Wallahi babu wanda ya faɗa min haɗarin nan da ka yi in ba dan daka kira ni ba”
“Toh ai ba wani abun daɗi ba ne balle a riƙa yayatawa, kuma ba a daɗe da yin abun ba, Allah ma dai ya tsare”
“Allah ya ƙara tsarewa, amman dai wannan ɗan sarki ko sarki zan ce Allah be yi shi da rowa ba har miliyan ɗaya! Kamar wanda be san zafin kuɗi ba”
“Ya za'ayi ya san zafin kuɗi? Iyayensu suna kawashe kuɗin ƙasa, yanzu dai idan ka fita ka biya ka biya bilya kuɗin maltina da madara na aika am karɓo mata”
“Okay maganar asibitin fa?”
“Tace ba sai an jibe kuma naga kamar Neina bata son aje, ƙara mu ɗan saurara tukuna”
“Okay yayi Allah bata lafiya, amman ƴar'uwar ku ce ko? Naga kamar baƙuwar fuska ce”