Sashe 114
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata tsaya jiran Abunda zai ce ba ta juya ta shige ciki gidan. Shi har tsoro ta bashi cox the way da take bashi amsar kamar tana masa faɗa.
“Wow”
Ya faɗa yana shafa fuskarsa, kamin ya zuba hannayensa aljihu ya nufi motarsa.
Sorry for the short chapter 🙏🙏🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *70*
‘Manjo Usman Zamau, Manjo Usman Zamau’
Sunan yake ta maimaitawa, tana tunanin kamar ya san mai sunan amman ya kwanta masa, sai dai jin Manjo ma ya tattabatar masa da soja ne.
Murmushi ya samu kansa da yi lokacin daya tuna wasu kalamai da Namra ta yi masa.
“She's so Unique”
Rage gudun da yake, ya fido wayarsa ya nemo number Sadiq ya aika masa kira. Ringing ta yi sai da ta kusa katsewa sannan aka ɗaga.
“Shegen gari baka kira sai ta samu”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Chief Sadiq Northwest”
“Au yau Chief na samu kuma? Kai dai faɗa min abunda yasa ka kira ni”
“Kiran ka kawai na yi na gaishe ka, ko kuskure ne kiran manya kuma?”
“Na ji, ya gida ya hutu, ku ai kun samu hutu”
“Gaskiya ba laifi, amman ba wani mai yawa ba ne, ina Madam”
“Madam na nan ƙalau go straight to the point miyasa ka kira ni?”
Dariya sosai Abdool ya yi kamar ba shi ba, sam ba zaka za ci akwai mutumen da Abdool yake sakewa da shi ba, bayan mutanen gidansu.
“Kasan waye Manjo Usman Zamau?”
“Aha ni nasan akwai wata a ƙasa, ai baka kiran mutum hakan nan kawai”
“Ni dai amsa min kawai, ban ce ka min surutu ba”
“Na san shi, kai ma ai kasan shi, amman yanzu ya yi ritaya ai”
“Nima ina jin kamar na san shi amman sunan ya kwanta min”
“Ai mun yi zama barrack da shi ai, a Yola, shine mahaifin su Salwee and Abdulraman na manta sauran ɗiyansa dai, yanzu ina jin yana sokoto zaune, ance ya zama babban ɗan siyasa ma”
Abdool ya bugu sitiyari motarsa da ƙarfi.
“Yes I knew it!”
“Easy Man what happened to him?”
“Ba komai, kawai wani ɗan bincike na ke ne”
“Okay abokin su ekwieu ne tare suka yi aiki, suna shiri sosai”
“Amman kana da addireshinsa?”
“Kai Malam, tun da ba shi na ke wa aiki ba, haka kawai zan aje addireshinsa”
“Okay okay bye”
Sai kawai ya katse kiran zuciyarsa cike da farinciki. Wata number ya sake lalubowa ya aika mata kira.
“Salim a bincika min addireshin Manjo Usman Zamau mai ritiya, kuma a bincika min a cikin ƴaƴansa akwai Namra, aɗan min bincike akan ta”
Be jira abunda Salim ɗin zai bashi amsa ba ya katse wayar, dai-dai loƙacin daya faka a harabar gidan. A yanayin yadda ya shigo cikin gidan ba zaka ce shine ɗazu ya fita a haka ba, yadda ka san wanda aka yi bushara da aljanna haka ya dawo fuskarsa a sake, zuciyarsa fari ƙal.
Yana shigowa falo ya zauna saman cushion yana kallo falon kamar wani baƙo. Kallo ɗaya zaka masa ka fahimci yana ciki nishaɗi, dan hankalinsa ma baya gurin da yake kallo. Wayar hannunsa ya kallo kamar mai son magana da wayar, sai kuma ya watsa yatsunsa saman screen ɗin ya danna number Sadauki, bugu ɗa ya ya ɗauƙa.
“Sadauki ga ni a falo ina jiran ka”
Be jira abunda Sadauki zai ce ba, ya katse kiran fuskarsa shinfide da murmushi. Ba ayi minti biyu ba sai ga Sadauki cikin falon da rawar jikinsa.
“Allah ya taimaki Yarima, Allah yaja kwanan ka, Allah ya baka abunda kake so”
Abdool ya kallesa fuskarsa da Murmushi.
“Amin Sadauki, addu'ah tana tasiri sosai, kaga Allah ya fara ba ni nasara. Yariman ka ya kusa samun gimbiya”
Sadauki ya riƙe baki tare ta washe da dariya
“Mashallah, babban goro sai magogin ƙarfi, Allah ya taimaki Yarima, Mai Martaba zai fi kowa jin farincikin wannan labari”
Abdool ya ɗan risino daga zaunen da yake
“Ya kake auna farincikin Mai Martaba idan ya samu labarin na samu matar aure?”
“Allah ya taimake ka kamar mutum ne, da yake cikin tsamman nin ƴanci, yake cikin baƙin ciki da damuwa, ga yunwa da ƙishin ruwa ya dame sa, masaukinsa kuma babu daɗin zama, me kake tsammani idan aka aka basa sabon masauki mai cike da ƙuramon wanka, ga kuma abinci da abun sha, bayan kuma an ƴanta shi?”
Komawa Abdool ya yi dai-dai saman cushion ɗin ya ɗora hannayensa saman kushin ɗin yana kallon silin.
“Zai kasance mai tsananin farinciki, har zai ji kamar ya haɗe zuciya ya mutu saboda jindaɗi”
“Toh haka zuciyar Mai Martaba zata kasance matuƙar ya samu labarin Yarimansa ya samu Gimbiya”
Murmushi mai ƙayatarwa Abdool ya yi, ba tare da ya kalli Sadauki ba ya ce
“Bana Sadauki da kai za'aje Umara”
Faɗuwa Sadauki ya yi yima Abdool godiya, yana zuba masa kirari, da yabo. Hannu Abdool ya ɗaga masa alamar ya tashi ya bashi guri, haka ya tashi ya fice baki har kunne tsabar murna da farinciki.
Sai da Sadauki ya fice sannan Abdool ya maida dubansa gurin wayar yana lalubo number Mai Martaba. A handsfree ya saka wayar ya ɗorata saman center center tebur ya nufi freezer ya bude ya ɗauko power horse, ya kai bakinsa.
Daga inda yake tsaye yana jiyo muryar Mai Martaba da yayi picking wayar tare da sallama.
“Allah ya taimaki Mai Martaba, i have a good news for you”
“I have good news for you too Son”
“Amman nawa ya fi na ka daɗi, dan nawa idan ka ji ma sai ka bani goro”
“Nima ai sai ka bani goro ba kuma ɗan ƙarami ba ma”
“Me zaka ba ni idan nayi maka albishir da abunda ka daɗe kana jira”
“Zan baka yankin Bakori da kewaye, kuma za a naɗa ka motar Mai Martaba kai fa wace kyauta zaka min?”
Zauna Abdool yayi saman kujera yana dariya har da buga ƙafa, ko ba komai Sarautar da Mai Martaba ya ce zai bashi ta sashi dariya balle kuma yau yana cikin nishaɗi.
“Ni kuma bana da gumi na zaka je Ummara gaida Ubangiji”
“Lallai yau Ɗan Sarki yana ciki farinciki, ɗan tsakura min kaɗan daga cikin labarin ka mana”
“ Ina ai ba tsakure, sai ga ni ga ka, gobe zan sauka sokoto cikin rahamar ubangiji, kuma ba zan kwana ba, har sai na labarta maka abunda zan labartawa Ummi”
“Allah ya kai mu, ya dawo da kai lafiya”
“Amin ya Rabbi. Na gode Mai Martaba, mu kwana lafiya”
Daga haka suka yi sallama, sai Abdool ya ɗauki wayarsa ya nufi bedroom yana kalle kallen gidan kamar yau ya fara shigo shi.
Bayan ya rage tufafin jikinsa ya aika ma wani yaronsa saƙo. Akan ya nema masa jirgin da zaije Katsina gobe.
Bayan kamar minti goma sha biyar yaron yayi masa reply da akwai wanda zai tashi da safe zuwa Katsina.
Daga nan Abdool ya aikama Sadauki da text na maganar tafiyarsu gobe gida, akan yayi duk abunda ya kamata cikin lokaci, duk da be so hakan ba, sai dan Ummi da ranta ya ɓaci.
NAMRA POV.
Da tunanin abunda zata faɗa ma su Neina ta shiga gida, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin bibiyar da Abdool yake mata. Babu abunda ya fi tsaya mata a rai kamar tambayoyin da ya yi mata.
“Har ya tafi?”
Tambayar da Neina ta yi mata ya firgita ta, har ta zabura, sam bata san ma ta kawo kusa da su ba.
“Eh ya wuce”
Karaf idonta cikin na Lamido da ke dannar waya, kasa kawar da idon ta yi, shi ma kuma ya kasa janye nasa, suka yi ta kallo kallo ita da shi, har sai da Uwani ta maimaita tambayar da take mata.
“Na ce shi ne wanda kika sani ɗin?”
Sannan ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta. Kamin daga bisani ta buɗe idon dake cike da hawaye ta kaɗawa Uwani kai alamar ‘Eh’ ta wuce ɗaki.
Samun kanta ta yi da kuka marar dalili, wani abu take ji yana ratsa mata zuciya mai wuyar fassara, numfashi take da ƙarfi kamin ta samu saita kanta, ta numfasa a hankali tana gode Ubangijinta.
Abdool ya tsaya mata a rai, tambayar ina ya fito ina zaije ya hana ta sukuni, wace manufa yake da ita akanta, shi ya hana ta rumtsawa har dare ya raba.
RASHIDA POV.
Hawaye ne suke mata masu zafi sosai suke mata zuba, keys ɗin dake hannunta take ta juyawa, tana mamakin irin abunda iyayenta suka mata.
‘Ashe akwai ranar da iyaye suke tsanar ƴar cikin su? Ashe rana zata zo da Momi da Dady zasu buƙaci na bar gidan nan? Ban ga laifin Hilal ba dan ya zaɓi rabuwa da ni, ga shi yanzu iyayena ma sun zaɓi haka’
Matsa ƙwallar tayi ta kai hannu ta ɗauki wayarta ta nemi number Teema ta aika mata kira.
“Ƴar gari”
“Teema kin ce zaki shigo kuma har yau baki zo ba, wallahi ina cikin matsala”
“Me ya faru wace irin matsala kuma?”
“Daddy na roƙa ya ba ni keys ɗin gidansa da yake by pass”
“Me hakan yake nufi?”
“Zan fi jindaɗi idan ina ni kaɗai, shiyasa na roƙa ya bani gidansa can na zauna, kuma ya anince min, yanzu matsalar da nake ciki ta rashin makama ne, Teema ina son na koma gidan miji na ko ta halin yayana”
Daga can cikin wayar Teema ta sauke ajiyar zuciya.
“Rashida miyasa ba zaki haƙura da mijin nan ki ba? Ya nuna miki ƙiyayya tsantsarta, ki ƙyale shi mana, Allah zai kawo miki wani”
“Teema har yanzu baki san miye so ba, saboda ba ki taɓa yi ba, bakin irin zafin da mace take ji idan ta rabu da uban ɗiyanta ba, dan Allah ki taimaka min”
“Gaskiya Rashida taimako ɗaya zan iya miki, kawai ki haƙura da shi, Allah zai saka miki, amman idan kuma baki ji ba, zan zo gobe na kai ki gurin wani malamin wanda zai taimaka miki ko Allah zai sa a dace”
“Eh ki zo dan Allah, da ƙarfe nawa zaki zo?”
“Tara da rabi?”
“Sai kin zo, daga nan ma sai ki taya ni maida kayana wacan gidan”
“Okay Allah ya kai mu”
“Amin Sai na ji ki”
Ta katse kiran tana share hawaye.
“Wow”
Ya faɗa yana shafa fuskarsa, kamin ya zuba hannayensa aljihu ya nufi motarsa.
Sorry for the short chapter 🙏🙏🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *70*
‘Manjo Usman Zamau, Manjo Usman Zamau’
Sunan yake ta maimaitawa, tana tunanin kamar ya san mai sunan amman ya kwanta masa, sai dai jin Manjo ma ya tattabatar masa da soja ne.
Murmushi ya samu kansa da yi lokacin daya tuna wasu kalamai da Namra ta yi masa.
“She's so Unique”
Rage gudun da yake, ya fido wayarsa ya nemo number Sadiq ya aika masa kira. Ringing ta yi sai da ta kusa katsewa sannan aka ɗaga.
“Shegen gari baka kira sai ta samu”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Chief Sadiq Northwest”
“Au yau Chief na samu kuma? Kai dai faɗa min abunda yasa ka kira ni”
“Kiran ka kawai na yi na gaishe ka, ko kuskure ne kiran manya kuma?”
“Na ji, ya gida ya hutu, ku ai kun samu hutu”
“Gaskiya ba laifi, amman ba wani mai yawa ba ne, ina Madam”
“Madam na nan ƙalau go straight to the point miyasa ka kira ni?”
Dariya sosai Abdool ya yi kamar ba shi ba, sam ba zaka za ci akwai mutumen da Abdool yake sakewa da shi ba, bayan mutanen gidansu.
“Kasan waye Manjo Usman Zamau?”
“Aha ni nasan akwai wata a ƙasa, ai baka kiran mutum hakan nan kawai”
“Ni dai amsa min kawai, ban ce ka min surutu ba”
“Na san shi, kai ma ai kasan shi, amman yanzu ya yi ritaya ai”
“Nima ina jin kamar na san shi amman sunan ya kwanta min”
“Ai mun yi zama barrack da shi ai, a Yola, shine mahaifin su Salwee and Abdulraman na manta sauran ɗiyansa dai, yanzu ina jin yana sokoto zaune, ance ya zama babban ɗan siyasa ma”
Abdool ya bugu sitiyari motarsa da ƙarfi.
“Yes I knew it!”
“Easy Man what happened to him?”
“Ba komai, kawai wani ɗan bincike na ke ne”
“Okay abokin su ekwieu ne tare suka yi aiki, suna shiri sosai”
“Amman kana da addireshinsa?”
“Kai Malam, tun da ba shi na ke wa aiki ba, haka kawai zan aje addireshinsa”
“Okay okay bye”
Sai kawai ya katse kiran zuciyarsa cike da farinciki. Wata number ya sake lalubowa ya aika mata kira.
“Salim a bincika min addireshin Manjo Usman Zamau mai ritiya, kuma a bincika min a cikin ƴaƴansa akwai Namra, aɗan min bincike akan ta”
Be jira abunda Salim ɗin zai bashi amsa ba ya katse wayar, dai-dai loƙacin daya faka a harabar gidan. A yanayin yadda ya shigo cikin gidan ba zaka ce shine ɗazu ya fita a haka ba, yadda ka san wanda aka yi bushara da aljanna haka ya dawo fuskarsa a sake, zuciyarsa fari ƙal.
Yana shigowa falo ya zauna saman cushion yana kallo falon kamar wani baƙo. Kallo ɗaya zaka masa ka fahimci yana ciki nishaɗi, dan hankalinsa ma baya gurin da yake kallo. Wayar hannunsa ya kallo kamar mai son magana da wayar, sai kuma ya watsa yatsunsa saman screen ɗin ya danna number Sadauki, bugu ɗa ya ya ɗauƙa.
“Sadauki ga ni a falo ina jiran ka”
Be jira abunda Sadauki zai ce ba, ya katse kiran fuskarsa shinfide da murmushi. Ba ayi minti biyu ba sai ga Sadauki cikin falon da rawar jikinsa.
“Allah ya taimaki Yarima, Allah yaja kwanan ka, Allah ya baka abunda kake so”
Abdool ya kallesa fuskarsa da Murmushi.
“Amin Sadauki, addu'ah tana tasiri sosai, kaga Allah ya fara ba ni nasara. Yariman ka ya kusa samun gimbiya”
Sadauki ya riƙe baki tare ta washe da dariya
“Mashallah, babban goro sai magogin ƙarfi, Allah ya taimaki Yarima, Mai Martaba zai fi kowa jin farincikin wannan labari”
Abdool ya ɗan risino daga zaunen da yake
“Ya kake auna farincikin Mai Martaba idan ya samu labarin na samu matar aure?”
“Allah ya taimake ka kamar mutum ne, da yake cikin tsamman nin ƴanci, yake cikin baƙin ciki da damuwa, ga yunwa da ƙishin ruwa ya dame sa, masaukinsa kuma babu daɗin zama, me kake tsammani idan aka aka basa sabon masauki mai cike da ƙuramon wanka, ga kuma abinci da abun sha, bayan kuma an ƴanta shi?”
Komawa Abdool ya yi dai-dai saman cushion ɗin ya ɗora hannayensa saman kushin ɗin yana kallon silin.
“Zai kasance mai tsananin farinciki, har zai ji kamar ya haɗe zuciya ya mutu saboda jindaɗi”
“Toh haka zuciyar Mai Martaba zata kasance matuƙar ya samu labarin Yarimansa ya samu Gimbiya”
Murmushi mai ƙayatarwa Abdool ya yi, ba tare da ya kalli Sadauki ba ya ce
“Bana Sadauki da kai za'aje Umara”
Faɗuwa Sadauki ya yi yima Abdool godiya, yana zuba masa kirari, da yabo. Hannu Abdool ya ɗaga masa alamar ya tashi ya bashi guri, haka ya tashi ya fice baki har kunne tsabar murna da farinciki.
Sai da Sadauki ya fice sannan Abdool ya maida dubansa gurin wayar yana lalubo number Mai Martaba. A handsfree ya saka wayar ya ɗorata saman center center tebur ya nufi freezer ya bude ya ɗauko power horse, ya kai bakinsa.
Daga inda yake tsaye yana jiyo muryar Mai Martaba da yayi picking wayar tare da sallama.
“Allah ya taimaki Mai Martaba, i have a good news for you”
“I have good news for you too Son”
“Amman nawa ya fi na ka daɗi, dan nawa idan ka ji ma sai ka bani goro”
“Nima ai sai ka bani goro ba kuma ɗan ƙarami ba ma”
“Me zaka ba ni idan nayi maka albishir da abunda ka daɗe kana jira”
“Zan baka yankin Bakori da kewaye, kuma za a naɗa ka motar Mai Martaba kai fa wace kyauta zaka min?”
Zauna Abdool yayi saman kujera yana dariya har da buga ƙafa, ko ba komai Sarautar da Mai Martaba ya ce zai bashi ta sashi dariya balle kuma yau yana cikin nishaɗi.
“Ni kuma bana da gumi na zaka je Ummara gaida Ubangiji”
“Lallai yau Ɗan Sarki yana ciki farinciki, ɗan tsakura min kaɗan daga cikin labarin ka mana”
“ Ina ai ba tsakure, sai ga ni ga ka, gobe zan sauka sokoto cikin rahamar ubangiji, kuma ba zan kwana ba, har sai na labarta maka abunda zan labartawa Ummi”
“Allah ya kai mu, ya dawo da kai lafiya”
“Amin ya Rabbi. Na gode Mai Martaba, mu kwana lafiya”
Daga haka suka yi sallama, sai Abdool ya ɗauki wayarsa ya nufi bedroom yana kalle kallen gidan kamar yau ya fara shigo shi.
Bayan ya rage tufafin jikinsa ya aika ma wani yaronsa saƙo. Akan ya nema masa jirgin da zaije Katsina gobe.
Bayan kamar minti goma sha biyar yaron yayi masa reply da akwai wanda zai tashi da safe zuwa Katsina.
Daga nan Abdool ya aikama Sadauki da text na maganar tafiyarsu gobe gida, akan yayi duk abunda ya kamata cikin lokaci, duk da be so hakan ba, sai dan Ummi da ranta ya ɓaci.
NAMRA POV.
Da tunanin abunda zata faɗa ma su Neina ta shiga gida, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin bibiyar da Abdool yake mata. Babu abunda ya fi tsaya mata a rai kamar tambayoyin da ya yi mata.
“Har ya tafi?”
Tambayar da Neina ta yi mata ya firgita ta, har ta zabura, sam bata san ma ta kawo kusa da su ba.
“Eh ya wuce”
Karaf idonta cikin na Lamido da ke dannar waya, kasa kawar da idon ta yi, shi ma kuma ya kasa janye nasa, suka yi ta kallo kallo ita da shi, har sai da Uwani ta maimaita tambayar da take mata.
“Na ce shi ne wanda kika sani ɗin?”
Sannan ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta. Kamin daga bisani ta buɗe idon dake cike da hawaye ta kaɗawa Uwani kai alamar ‘Eh’ ta wuce ɗaki.
Samun kanta ta yi da kuka marar dalili, wani abu take ji yana ratsa mata zuciya mai wuyar fassara, numfashi take da ƙarfi kamin ta samu saita kanta, ta numfasa a hankali tana gode Ubangijinta.
Abdool ya tsaya mata a rai, tambayar ina ya fito ina zaije ya hana ta sukuni, wace manufa yake da ita akanta, shi ya hana ta rumtsawa har dare ya raba.
RASHIDA POV.
Hawaye ne suke mata masu zafi sosai suke mata zuba, keys ɗin dake hannunta take ta juyawa, tana mamakin irin abunda iyayenta suka mata.
‘Ashe akwai ranar da iyaye suke tsanar ƴar cikin su? Ashe rana zata zo da Momi da Dady zasu buƙaci na bar gidan nan? Ban ga laifin Hilal ba dan ya zaɓi rabuwa da ni, ga shi yanzu iyayena ma sun zaɓi haka’
Matsa ƙwallar tayi ta kai hannu ta ɗauki wayarta ta nemi number Teema ta aika mata kira.
“Ƴar gari”
“Teema kin ce zaki shigo kuma har yau baki zo ba, wallahi ina cikin matsala”
“Me ya faru wace irin matsala kuma?”
“Daddy na roƙa ya ba ni keys ɗin gidansa da yake by pass”
“Me hakan yake nufi?”
“Zan fi jindaɗi idan ina ni kaɗai, shiyasa na roƙa ya bani gidansa can na zauna, kuma ya anince min, yanzu matsalar da nake ciki ta rashin makama ne, Teema ina son na koma gidan miji na ko ta halin yayana”
Daga can cikin wayar Teema ta sauke ajiyar zuciya.
“Rashida miyasa ba zaki haƙura da mijin nan ki ba? Ya nuna miki ƙiyayya tsantsarta, ki ƙyale shi mana, Allah zai kawo miki wani”
“Teema har yanzu baki san miye so ba, saboda ba ki taɓa yi ba, bakin irin zafin da mace take ji idan ta rabu da uban ɗiyanta ba, dan Allah ki taimaka min”
“Gaskiya Rashida taimako ɗaya zan iya miki, kawai ki haƙura da shi, Allah zai saka miki, amman idan kuma baki ji ba, zan zo gobe na kai ki gurin wani malamin wanda zai taimaka miki ko Allah zai sa a dace”
“Eh ki zo dan Allah, da ƙarfe nawa zaki zo?”
“Tara da rabi?”
“Sai kin zo, daga nan ma sai ki taya ni maida kayana wacan gidan”
“Okay Allah ya kai mu”
“Amin Sai na ji ki”
Ta katse kiran tana share hawaye.