Sashe 137
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin da ta bar gidan mijita sai ta nufo gida, sai dai bata yarda ta nunawa mahaifiyarta damuwarta ba, gudun kar ta hana ta aikata abunda take da niyar yi, wuni ta yi a gidan suka sha fira kamar ba komai sai dare ta fito suka koma gida ita da yaranta da kuma mai aikinta. Bata tarar da Uzair cikin gidan ba hakan yasa ta ɗan ji sanyi dan bata ƙaunar ganinsa a yanzu. Abunda kawai take da buƙata ya za'ayi ta haɗu da Namta akwai buƙatar ta tattauna da ita kamin ta fallasa Uzair, ma'ana ta jawa Namra haƙƙinta ko zata samu sanyin zuciya akan abunda ya aikatawa ɗan sa. Haka ta kwana tana tunanin mafita washe gari ma kasa zuwa aiki ta yi duk da tana da cases a kotu, da an kira ta sai tace bata da lafiya ne. Uzair kuma be kwana a gidan ba, da alama akwai gun da ya kwana, sai dai hakan be dame ta ba ko kaɗan tun da tasan wanene shi a yanzu. Bayan ta gama waya da wani Barrister, sai ga kiran Mahaifiyarta ya shigo wayarta.
Bayan sun gaisa take labarta mata ance Namra ta dawo, kuma wai Abbah ne yaje ya taho ta ita, Yasmin ta nuna murnarta sosai daman abun nema ya samu. Dan haka tana kashe wayar ta aje little Namra ta shiga wanka, tana fitowa ta yi ma mata sannan suka shirya daman Adnan yana makaranta. Ƴar aikinta kawai ta bari a gidan ta nufi gidansu Namra.
Tana fita Uzair na shigowa, ciki wani irin yanayi ya buga ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.
“Sannu da zuwa”
Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.
TEEMA POV.
Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.
Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.
Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.
“Kan Uban nan, uban wa zaku jefarwa da jaka nan? Ku kwashe su da sauri ku kai su ɗakin ku, kuma kar a sake zama min saman kujera, wannan ai rashin tarbiya ne manya su zauna a kujera ku ku zauna ni ba zan ɗauki wannan ba”
Ulfa ce uwar tsoro da sauri ta nufi jakarta ta ɗauka ta nufi ɗakinsu. Ezzah kan banza ta yi kuma ta ƙi sauka daga saman kujerar.
“Ke dan Ubanki ba da nake ba”
Sai a sannan ta ɗago kai ta kalleta.
“Mu a saman kujera muka saba zama”
Ta faɗa tana sauka ƙasa, badan hannun Teema da ke da rubutun ba da babu abunda zai hana ta dake ta.
“Wallahi kuka kuskura min rashin kunya zaki wahala a gidan nan”
Sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu, Ulfah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin tana leƙo ta shige da sauri.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *79*
Su Maryam na wucewa Zinatu ta rufa musu baya ita ma tana murmushi. Hajiya Barau kuma ta koma part ɗinta, bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki wayarta ta kira Uzair. Bugu biyu ya ɗauka, saman-sama ya gaisa da ita saboda shi ma be cikin daɗin rai, sannan ta labarta masa Namra ta dawo, he was shocked and surprise, sai ya ji maganar kamar daga sama.
“Da gaske kike yi?”
“Wallahi da ido na na gani, yanzun nan Alhaji ya dawo tare da ita, kasan na labarta maka ai Sarkin Katsina ya aiko ƴana nemansa ni na ɗauka ko wani abu ta yi, sai gashi kuma na ga sun dawo da ita”
“Aurenta ya mutu ne?”
“Bari naje gurin Alhaji na ji”
“Okay ki sanar da ni duk abunda kika ji”
“Tau”
Tana kashe wayar ta nufi part ɗin Abbah. Ko da ta shiga yana banɗaki, har ta zauna sai kuma ta yi saurin tashi ta koma part ɗinta, fruit ta yankawa Abbah ta saka madara, ta ɗauka ta nufi koma part ɗinsa. Wannan karon zaune ya same shi saman gado yana waya, sai ta zauna kusa da shi tana riƙe da fruits, sai da ya gama wayar sannan ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.
“Hajiya fatar dai lafiya”
“Lafiya ƙalau bana da ikon da zan zo na ga miji na ne? Ga ɗan abunda na haɗa maka, abinci na kan wuta ban ƙarasa ba”
“Ai bama na ma jin yunwa kamin na taso sai da muka ci abinci”
“A can gidan Namra?”
“A'a a gidan Mai Martaba Ahmad Mai-doki Sarkin Katsina, dake Kaduna”
“Ban gane ba, baka labarta min zaka dawo da Namra ba, duk lokacin da na tambaye ka sai ka ce min wani babu wata matsala dai, ya akayi ka dawo da ita bayan kace ba zaka karɓe ta ba?”
Wani kallo Abbah yayi mata.
“Ya kike magana kamar wacece bata ji daɗin dawowar Namra ba? Komai ta yi min aduniyar nan she still my daughter, ko lalacewa ta yi dole za'ace ƴar gidan nan ce, ballantana ina son ta, kawai dai ta ɓata min rai ne kuma ta gane kuskurenta”
“Ta gane kuskurenta kamar ya? Alhaji yanzu baka tunanin mutane zasu zarge ka akan ka yi magana kuma ka zauna? Wannan ai talalace ka yi mata yarinya ta yi laifi kuma yanzu da miji ya wulaƙanta sai kace kayafe mata haka ake yi?”
Abbah yayi murmushi, yana gyara zamansa.
“Baki gane abun ba ne Hajiya wato da muka sauka Katsina...”
Ya kwashe labarin abunda ya faru ya faɗa mata, daman can Anty Amarya ce ta hana a faɗawa kowa wai tana son kawai su ganta ne. Mire baki Hajiya Barau ta yi ta miƙe tsaye.
“Yanzu Alhaji im ban da su mai da wani iri sai da Asim ya gama wulaƙanta ta ya sake ta sannan yanzu su haɗa baki da uwarta su nemo wani a kai ga Sarki, wannan ma ai rainin wayo ne, yarinyar ta yi wasa da hankalinka, yanzu kuma kai har ka yarda ta gane kuskurenta haba Alhaji wannan ai ka bata damar ƙara aikata abunda ta aikata ne kawai”
Wani wawan kallo Abbah ya watsa mata.
“Na bata damar, ko yanzu Namra ta kawo min wanda take so zan aura mata, daman na lura da ke ba son yarinyar nan kike ba, mi ko duk wanda be son Namra bana son shi, dan Namra jinina ce, ƴata ce, ina kula da yadda kika ɗauki matar nan ita ba haka ta ɗauke ki ba, baki son ta ita da yaran ta, ana gobe za mu bar garin nan nan cikin falon nan nawa kika saki wata magana wai Allah yasa Namra bata yi mana jaye-jaye ba, a gaban uwarta amman ta miki kawaici ta tashi ta bar miki falon bata ce komai ba, shiyasa na zaɓi zuwa da ita na ƙi na tafi da ke, iya haƙuri matar nan ta nayi yinsa da ke amman ke baki ga, ina kula da abun nan da Namra ta yi kamar daɗi yayi miki, ba zan ɗauka ba kar bakin ki ya sake furta mummun kalma akan ƴaƴana!”
Ta riƙe baki.
“Alhaji kai kake faɗa min wannan maganar akan Namra? Daga na faɗa maka gaskiya har kace wai bana son ta ita da uwarta? Kuma ka ce baka da so na saboda ƴarka? Anya banza matar nan ta barka Alhaji”
“Ba banza ta bar ni ba, ta kula da ni fiye da yadda kike tsammani, dan tana son ki ke da ƴaƴanki, ba kamar yadda kike nuna mata ba, kuma daga yau sai yau, kar wani munafurci da wata magana marar daɗi ta sake fitowa bakinki akan Ƴaƴa ko wannan matar tau a bakin auren ki! Kar wacce ta aake tadarmin fitina yadda na ga dama haka zan yi a gidana”
Mutuwar tsaye Hajiya Barau ta yi a gurin, tana mamakin Abbah ta ya juye kamar ba shi ba, wai yau shi yake faɗa mata wannan maganar, har yake cewa bakin aurenta. Uffan bata yarda ta sake cewa ba, ta nufi ƙofa cike da nauyin jiki fice sun-sun-sun, hannayenta a baya tana jin kamar an ɗora mata dutse saman kai.
NAMRA POV.
Cikin falo suka riƙa hugging ɗin juna ita da ƴan'uwanta, suna jin kamar su haɗe juna ita da su, sai faman kuka suke. Anty Amarya ta fito daga bedroom ɗinta fuskarta da dariya ta ce
“To ko haɗe ta zaku yi?”
“Anty Faɗa mana yadda aka yi ta yarda ta biyo ku kuma har Abbah ya amince”
Aisha ta faɗa tana laƙƙame da wuyan Namra.
“To ku sake ta taje ta yi wanka ta shirya zan baku labarin komai”
Aisha da Hindatu ne suka saketa yayinda Maryam ta laƙƙame hannunta suka nufi bedroom tare. Bayan sun tashi Zinatu ma ta tashi ta nufi part ɗin Mahaifiyarta. A sannan ne Anty take tambayarsu yaushe Zinatu ta zo.
“Tun ranar da kuka tafi, wai faɗa tayi da mijinta ya ce taje gida, shi ne wai ta baro masa yaransa”
“Subhallahi, miya haɗa su haka?”
“Wallahi bata faɗa ba, ai kin san Hajiya ba zata bari ta faɗi gaskiya ba, dan ita Hajiya ma ce mana ta yi bikin Maryam ta zo”
“Tau Allah ya sauwaƙe yayi mata mafita, ku tashi ku girka mana abinci dan ni dai ba zan ci taliya ba”
Hindatu ta mike tsaye tana dariya.
“Komai kuke so za a muku, sai ku ba mu labarin abunda ya faru”
A ɗaki da suka shiga Namra take labartawa Maryam irin abunda Asim yayi mata, da yadda ta yi rayuwa gidansu Lamido da kuma haɗuwarta da Abdool ya yadda ya haɗa ta da su Anty.
Bayan sun gaisa take labarta mata ance Namra ta dawo, kuma wai Abbah ne yaje ya taho ta ita, Yasmin ta nuna murnarta sosai daman abun nema ya samu. Dan haka tana kashe wayar ta aje little Namra ta shiga wanka, tana fitowa ta yi ma mata sannan suka shirya daman Adnan yana makaranta. Ƴar aikinta kawai ta bari a gidan ta nufi gidansu Namra.
Tana fita Uzair na shigowa, ciki wani irin yanayi ya buga ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.
“Sannu da zuwa”
Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.
TEEMA POV.
Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.
Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.
Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.
“Kan Uban nan, uban wa zaku jefarwa da jaka nan? Ku kwashe su da sauri ku kai su ɗakin ku, kuma kar a sake zama min saman kujera, wannan ai rashin tarbiya ne manya su zauna a kujera ku ku zauna ni ba zan ɗauki wannan ba”
Ulfa ce uwar tsoro da sauri ta nufi jakarta ta ɗauka ta nufi ɗakinsu. Ezzah kan banza ta yi kuma ta ƙi sauka daga saman kujerar.
“Ke dan Ubanki ba da nake ba”
Sai a sannan ta ɗago kai ta kalleta.
“Mu a saman kujera muka saba zama”
Ta faɗa tana sauka ƙasa, badan hannun Teema da ke da rubutun ba da babu abunda zai hana ta dake ta.
“Wallahi kuka kuskura min rashin kunya zaki wahala a gidan nan”
Sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu, Ulfah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin tana leƙo ta shige da sauri.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *79*
Su Maryam na wucewa Zinatu ta rufa musu baya ita ma tana murmushi. Hajiya Barau kuma ta koma part ɗinta, bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki wayarta ta kira Uzair. Bugu biyu ya ɗauka, saman-sama ya gaisa da ita saboda shi ma be cikin daɗin rai, sannan ta labarta masa Namra ta dawo, he was shocked and surprise, sai ya ji maganar kamar daga sama.
“Da gaske kike yi?”
“Wallahi da ido na na gani, yanzun nan Alhaji ya dawo tare da ita, kasan na labarta maka ai Sarkin Katsina ya aiko ƴana nemansa ni na ɗauka ko wani abu ta yi, sai gashi kuma na ga sun dawo da ita”
“Aurenta ya mutu ne?”
“Bari naje gurin Alhaji na ji”
“Okay ki sanar da ni duk abunda kika ji”
“Tau”
Tana kashe wayar ta nufi part ɗin Abbah. Ko da ta shiga yana banɗaki, har ta zauna sai kuma ta yi saurin tashi ta koma part ɗinta, fruit ta yankawa Abbah ta saka madara, ta ɗauka ta nufi koma part ɗinsa. Wannan karon zaune ya same shi saman gado yana waya, sai ta zauna kusa da shi tana riƙe da fruits, sai da ya gama wayar sannan ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.
“Hajiya fatar dai lafiya”
“Lafiya ƙalau bana da ikon da zan zo na ga miji na ne? Ga ɗan abunda na haɗa maka, abinci na kan wuta ban ƙarasa ba”
“Ai bama na ma jin yunwa kamin na taso sai da muka ci abinci”
“A can gidan Namra?”
“A'a a gidan Mai Martaba Ahmad Mai-doki Sarkin Katsina, dake Kaduna”
“Ban gane ba, baka labarta min zaka dawo da Namra ba, duk lokacin da na tambaye ka sai ka ce min wani babu wata matsala dai, ya akayi ka dawo da ita bayan kace ba zaka karɓe ta ba?”
Wani kallo Abbah yayi mata.
“Ya kike magana kamar wacece bata ji daɗin dawowar Namra ba? Komai ta yi min aduniyar nan she still my daughter, ko lalacewa ta yi dole za'ace ƴar gidan nan ce, ballantana ina son ta, kawai dai ta ɓata min rai ne kuma ta gane kuskurenta”
“Ta gane kuskurenta kamar ya? Alhaji yanzu baka tunanin mutane zasu zarge ka akan ka yi magana kuma ka zauna? Wannan ai talalace ka yi mata yarinya ta yi laifi kuma yanzu da miji ya wulaƙanta sai kace kayafe mata haka ake yi?”
Abbah yayi murmushi, yana gyara zamansa.
“Baki gane abun ba ne Hajiya wato da muka sauka Katsina...”
Ya kwashe labarin abunda ya faru ya faɗa mata, daman can Anty Amarya ce ta hana a faɗawa kowa wai tana son kawai su ganta ne. Mire baki Hajiya Barau ta yi ta miƙe tsaye.
“Yanzu Alhaji im ban da su mai da wani iri sai da Asim ya gama wulaƙanta ta ya sake ta sannan yanzu su haɗa baki da uwarta su nemo wani a kai ga Sarki, wannan ma ai rainin wayo ne, yarinyar ta yi wasa da hankalinka, yanzu kuma kai har ka yarda ta gane kuskurenta haba Alhaji wannan ai ka bata damar ƙara aikata abunda ta aikata ne kawai”
Wani wawan kallo Abbah ya watsa mata.
“Na bata damar, ko yanzu Namra ta kawo min wanda take so zan aura mata, daman na lura da ke ba son yarinyar nan kike ba, mi ko duk wanda be son Namra bana son shi, dan Namra jinina ce, ƴata ce, ina kula da yadda kika ɗauki matar nan ita ba haka ta ɗauke ki ba, baki son ta ita da yaran ta, ana gobe za mu bar garin nan nan cikin falon nan nawa kika saki wata magana wai Allah yasa Namra bata yi mana jaye-jaye ba, a gaban uwarta amman ta miki kawaici ta tashi ta bar miki falon bata ce komai ba, shiyasa na zaɓi zuwa da ita na ƙi na tafi da ke, iya haƙuri matar nan ta nayi yinsa da ke amman ke baki ga, ina kula da abun nan da Namra ta yi kamar daɗi yayi miki, ba zan ɗauka ba kar bakin ki ya sake furta mummun kalma akan ƴaƴana!”
Ta riƙe baki.
“Alhaji kai kake faɗa min wannan maganar akan Namra? Daga na faɗa maka gaskiya har kace wai bana son ta ita da uwarta? Kuma ka ce baka da so na saboda ƴarka? Anya banza matar nan ta barka Alhaji”
“Ba banza ta bar ni ba, ta kula da ni fiye da yadda kike tsammani, dan tana son ki ke da ƴaƴanki, ba kamar yadda kike nuna mata ba, kuma daga yau sai yau, kar wani munafurci da wata magana marar daɗi ta sake fitowa bakinki akan Ƴaƴa ko wannan matar tau a bakin auren ki! Kar wacce ta aake tadarmin fitina yadda na ga dama haka zan yi a gidana”
Mutuwar tsaye Hajiya Barau ta yi a gurin, tana mamakin Abbah ta ya juye kamar ba shi ba, wai yau shi yake faɗa mata wannan maganar, har yake cewa bakin aurenta. Uffan bata yarda ta sake cewa ba, ta nufi ƙofa cike da nauyin jiki fice sun-sun-sun, hannayenta a baya tana jin kamar an ɗora mata dutse saman kai.
NAMRA POV.
Cikin falo suka riƙa hugging ɗin juna ita da ƴan'uwanta, suna jin kamar su haɗe juna ita da su, sai faman kuka suke. Anty Amarya ta fito daga bedroom ɗinta fuskarta da dariya ta ce
“To ko haɗe ta zaku yi?”
“Anty Faɗa mana yadda aka yi ta yarda ta biyo ku kuma har Abbah ya amince”
Aisha ta faɗa tana laƙƙame da wuyan Namra.
“To ku sake ta taje ta yi wanka ta shirya zan baku labarin komai”
Aisha da Hindatu ne suka saketa yayinda Maryam ta laƙƙame hannunta suka nufi bedroom tare. Bayan sun tashi Zinatu ma ta tashi ta nufi part ɗin Mahaifiyarta. A sannan ne Anty take tambayarsu yaushe Zinatu ta zo.
“Tun ranar da kuka tafi, wai faɗa tayi da mijinta ya ce taje gida, shi ne wai ta baro masa yaransa”
“Subhallahi, miya haɗa su haka?”
“Wallahi bata faɗa ba, ai kin san Hajiya ba zata bari ta faɗi gaskiya ba, dan ita Hajiya ma ce mana ta yi bikin Maryam ta zo”
“Tau Allah ya sauwaƙe yayi mata mafita, ku tashi ku girka mana abinci dan ni dai ba zan ci taliya ba”
Hindatu ta mike tsaye tana dariya.
“Komai kuke so za a muku, sai ku ba mu labarin abunda ya faru”
A ɗaki da suka shiga Namra take labartawa Maryam irin abunda Asim yayi mata, da yadda ta yi rayuwa gidansu Lamido da kuma haɗuwarta da Abdool ya yadda ya haɗa ta da su Anty.