Sashe 80
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai kawai Anty ta ɗaga mata ta kwanta a kujera ta lumshe ido tana yaƙi da hawan jinin dake son taso mata. Yasmin na ganin hakan gabanta ya faɗi sai duk tsoro ya rufe ta kar wani abu ya samu anty ace ita ce, da sauri ta ɗauki makullin motarta da wayarta ta fice.
RASHIDA POV.
Tana aiki wayarta tayi ringing, amman bata ɗaga ba sai da ta kammala dukan abinda take. Sannan ta duba Number mai kiran.
Cousin ɗinta ce Shafa wacce suke aiki a asibiti ɗaya da Hilal.
Sai da ta kiran numbers ɗin da suka kira bayan ita suka gaisa suka yi maganar da za su yi sannan ta kira Shafa.
“Matar likita, ina ta kira baki ɗaga waya ba”
“Wallahi ina office ne aiki yayi min yawa, ya kike?”
“Au har kin samu damar aikin ɗan ki na kwamce asibiti”
“Ɗa na? Ɗa na na cikina ko na ƴan'uwa”
“Wai tsaya karki ce min baki sani ba”
“Wallahi ban sani ba me ya faru?”
“Wallahi ɗa zu da safe aka kawo shi guraren goma wai ya ci guba daker aka ceto shi”
“Guba...?! Garin ya?”
“Wallahi ban sani ba, mu dai muka taimaka masa gurin coto rayuwar yaron. Ni kam nayi mamakin rashin ganin ki a gurin”
“Guba ta bama ɗana kuma?”
Rashida ta faɗa cikin kuka.
“Au wai baki sani ba? Zance duk ya karaɗe asibiti ɗan doc ya ci guba an kawo shi asibiti, amman dan Allah ki rufa min Asiri karki ce gare ni kika ji”
Kashe wayar Rashida tayi ta tashi yana kuka ta fice daga office ɗin. Tana fitowa kowa ya soma tambayar ba'asi ganin tana kuka.
“Kishiya ta ce ta sama ɗana guba, yana can asibiti”
Kowa Amsar data ke basa kenan. Su kuma sai tsinewa Kalsoom Albarka suke suna aybantata. Kamin ta ƙarasa gurin motarta har ta kira su Momy ta faɗa musu.
Wani irin kuka take tana tuƙin motar har cikin ranta take jin abinda Shafa ta faɗa mata. Kamin ta ƙasara asibitin ana ta kiranta numbers ɗin ƴan'uwa da alama suma sun ji ne.
AMIRA POV.
Wani kalar daɗi ne ya baibaye ta tun lokacin data ji Ummi na labarta ma ƴaƴanta Abdool na nan zuwa dan sun gama meeting ɗin da zasu yi, ya samu free days zai dawo gida yayi su, daman tun faruwar abin nan be zo gida ba.
A ranta take shirya irin nata tabarda zata masa, wanda take tunanin zai ɗauki hankalinsa izuwa gareta. Girki ne abinda ta fara kawowa a ranta dan tasan ta ƙware a wannan fannin. Sai dai matsalarta ɗaya Amal dan itace mai cewa ba zata ci abinda Amira ta girka ba, a kullum idan Amira tasa hannunta a abincin gidan sai ta ce ba zata ci ba.
Ta baro part ɗin falon inda take zaune ta nufo gurin da Ummi take zaune ta zauna ƙasa kusa da Ummi kamar ta shige jikinta.
“Eh haka nek son ayi idan ya dawo sai kuje a duba gidan nan a gyara a zuba sabbin ƴan haya, dan gidan marayu ba a barinsa haka”
Sai da Ummi ta ƙare zancen da take sannan ta kalli Amira dake ƙasa zauna tana murmushi.
“Amira akwai da son jiki kamar Abdool”
Amira tayi murmushi idonta na cika da hawaye.
“Haka nake jin ki kamar mamana kina tuna min da mamana sosai, yanayin rayuwarki”
Hawaye ya silalo daga idon Amira, wannan maganar har cikin zuciyar Amira take, tabbas tayi missing Ammy gashi kuma bata san ranar da zata sake haɗuwa da ita ba, bata san halin da take ciki ba.
Zubar hawayen Amira yasa Ummi ta ji babu daɗi, wannan karon da kanta tasa hannunta ta share mata hawaye.
“Ki daina kuka kin ji? Zan zame miki uwa inshallah, kuma nan gaba zaki koma gurin uwarki na miki alƙawari”
“Na gode”
Ta rumgume Ummi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya........
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *54*
Hankali a tashe ta isa asibitin, hawaye na bin fuskarta. Duk wanda ya ganta a lokacin sai ya tausaya mata dan sun san abinda ya kawo ta asibitin. Daman tuni labarin ya karaɗe asibitin cewa Amarya Doc ta saka ma ƙaramin ɗansa guba. Sai ma a yanzu ne wasu ne suke jin cewar Doc ya rabu da Rashida.
Kowa tsinewa Kalsoom yake wasu na faɗin daman kishiyoyin yanzu haka suke su shigo su kore uwargida kuma su mallake ƴaƴan miji da miji.
Wani irin banka tayi ma ƙofar office ɗin Hilal ta shiga kamar zata tashi ɗakin.
“Ina ɗa na yake?”
Shine abinda ta tambaya hawayen na bin fuskarta. Ɗagowa yayi daga dafe da kan da yake ya kalleta. Be yi msmakin ganinta ba daman yasan zata zo tun da akwai ƴan'uwanta a asibitin da zasu kai mata labari.
“Ina ɗa na yake Hilal?”
Ya sake tambaya ganin yayi mata ƙuri da ido kamar ba dashi take magana ba.
“Ɗan ki ko ɗa na?”
“Ɗa na, si kai baka san zafin sa ba da baka bari wata ta kai ga ba shi guba ba”
Miƙewa yayi tsaye ya daki teburin dake gabansa.
“How dare you, idan kin san zafinsa ai bs zaki taɓa zuwa wani gurin ki aikata zina ba, ba zaki taɓa bada kan ki ga kowa ba sai ubansu, amman haka kika taka igiyar aure Rashida kika tsallae ƴaƴanki kika aikata zina da namijin da ba muharramin ki ba, na ƴi nadamar haɗa zuri'ah dake da ace wats na aura ba da rayuwar ƴaƴana bata kasance a halin data kasance a yanzu ba”
Tun da yake maganar take baya baya har ta jingiya da ginin ƙofar idonta na hawaye.
“I need to my son”
“You won't see him”
Ta muna kanta yana mamakin yadda duniyar Hilal ta birkice mata.
“Hilal ni ce!”
“And so what? Get the hell out of my office”
“Kotu zata raba mu da kai ba zan ƙyale kai da matarka ku kashe min ɗa ba”
Ta buɗe ƙofar da ƙarfi ta fice. Be damu ba dan yasan ya riga ya kulle ɗakin da Rafiq yake ciki tun bayan tafiyar Kalsoom.
Ba shida wani aiki amman haka ya zauna a office ɗin dan baya son zuwa gida kwata-kwata gidan ya fita aransa.
Haka ya riƙa karɓar masu shigowa suna masa jajen abinda ya faru tare da masa Allah ya tsare gaba, wasu kan tambaye shi ta ya lamarin ya faru wasu kuma su kuma basa tambaya ganin kamar cin fuska ne.
Bayan yayi salla magariba ya koma ɗakin da Rafiq yake ya zauna yana kallonsa. Ga dukan alamu ya samu sauƙi dan bachinsa yake hankali kwance, humfashinsa na tafiya dai-dai kamar yadda ake so. Ana daf da kiran salla isha'i Hajiya ta iso tare da wasu ƙanensa.
Hilal na ganinta ya tashi a kujerar da yake zauna ya miƙa mata ta zauna, sannan ya soma miƙa mata gaisuwa. Bata karɓa ba ta kalli Rafiq cikin tausayi tace
“Hilal ya aka yi haka ta faru? Wai Kalsoom tasa masa guba?”
Shiru yayi yana tunanin ta ta inda zai soma maganar da bata daɗin faɗi. Idan har ya amsa da ita ɗin ce bashi da tabbaci ita ɗin ce idan kuma ba ita ba ce to wanene bayan daga ita sai Rafiq ne abin ya faru?
“Wallahi ina meeting ta kirana ni ban ɗaga ba sai daga baya na kirata sai ta ce min na zo fida Rafiq babu lafiya, ina zuwa na tarar bakinsa na kumfa ko da na ɗauko na kawo sa asibiti kamar ba zai yi rai ba, bincike dai ya nuna guba ya ci. Tun ɗazu aka masa hoto amman ban karɓo ba”
Hajiya ta taɓa hannu tana salati.
“O o ita kuma haka take? Hilal baka dace da matan ƙwarai, yanzu ɗan wannan ƙaramin yaro ko kashe tayi me zata ji? Kai duniya”
Shi dai yayi shiru be ce komai ba, hannyensa zube a aljihu. Kamin su ƙara cewa wani abu sai ga Ummu Faisak ta turo ƙofa ta shigo fuska babu annuri irin yau tana cikin masifa ɗin nan.
Hajiya tayi mata kallon marar kunya da tarbiya ganin yadda take huci kamar baƙin maciji.
“Haba Maman Faisak ai ko ɗakin kafirai ne kya dokko ƙofa kamin ki shigo balle musulmai”
Uffan bata cewa Hajiya dan tana cikin zafin rai tasan kuma idan har tace zata tsaya maidawa Hajiya magana to dukansu rayuwarsu sai ta ɓace dan Hilal ba ƙyalewa zai yi ba.
“Ɗa zu Adda Rashida ta zo nan ka hana ta shiga ta ga ɗan ta, akan wanenen dalili ko ita ba uwarsa bace? Ba zamu ɗauki tsarin wulaƙancin da kake son mana ba akan shegiyar matar ka, ta fitar da Rashida cikin gidan yanzu kuma tana son ta bi ƴaƴanta ya kashe, idan ba zaka iya wani abu ba mu za mu iya dan ba zamu zuba ido ta kashe mana ƴaƴa ba”
Wani wulaƙantancen kallo Hilal ya watsa mata kana yaja tsaki, sannan ya kai hannu ya kwaɓe wayar wata ƙanwar Rashida dake ɗaukar Rafiq a waya.
“Ku fita ku bani guri ko nasa ayi muku wulaƙanci, idan ita Rashida bata iya ba ke taya zaki iya, banza a banza, ko dan kina ƴar jarida? Ku fitar min daga office yanzu nan”
“Za mu fita ai bamu zo dan zama ba, amman ka jira sakamakon ka, ba za mu ɗauki a wulaƙanta mana ƴar'uwa ba”
Cewar Khady sannan ta duƙa ta ɗauki wayarta, Suka fice. Hajiya ta dafe kai.
“O Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, wannan masifa da me ta yi kama? Hilal ka rabu da matar nan ka huta daman masu tsantsar ladabi sun fi komai cuta”
Balki ta taɓe baki.
“Ni wallahi ban zata Kalsoom zata iya aikata haka ba, shiyasa ake cewa baka shedun mutum, mutum mugun ice”
“Hilal ka rabu da matar nan tun wuri kamar abin yayi maka yawa, ko ma shari'ah za su yi da ita suje can su yi amman ba tana gidan ka ba, sannan duk mace data fara da ƴaƴanka wata rana akan ka zata faɗa”
“Idan na rabu da ita kuma.. Da wa zan zauna”
“Sai ka nemi ƴar gidan malamai ka aura, kai ni ma zan nema maka ga mu da su a family masu hankali da natsuwa”
“Amman Hajiya zai zama ina ta aure aure”
RASHIDA POV.
Tana aiki wayarta tayi ringing, amman bata ɗaga ba sai da ta kammala dukan abinda take. Sannan ta duba Number mai kiran.
Cousin ɗinta ce Shafa wacce suke aiki a asibiti ɗaya da Hilal.
Sai da ta kiran numbers ɗin da suka kira bayan ita suka gaisa suka yi maganar da za su yi sannan ta kira Shafa.
“Matar likita, ina ta kira baki ɗaga waya ba”
“Wallahi ina office ne aiki yayi min yawa, ya kike?”
“Au har kin samu damar aikin ɗan ki na kwamce asibiti”
“Ɗa na? Ɗa na na cikina ko na ƴan'uwa”
“Wai tsaya karki ce min baki sani ba”
“Wallahi ban sani ba me ya faru?”
“Wallahi ɗa zu da safe aka kawo shi guraren goma wai ya ci guba daker aka ceto shi”
“Guba...?! Garin ya?”
“Wallahi ban sani ba, mu dai muka taimaka masa gurin coto rayuwar yaron. Ni kam nayi mamakin rashin ganin ki a gurin”
“Guba ta bama ɗana kuma?”
Rashida ta faɗa cikin kuka.
“Au wai baki sani ba? Zance duk ya karaɗe asibiti ɗan doc ya ci guba an kawo shi asibiti, amman dan Allah ki rufa min Asiri karki ce gare ni kika ji”
Kashe wayar Rashida tayi ta tashi yana kuka ta fice daga office ɗin. Tana fitowa kowa ya soma tambayar ba'asi ganin tana kuka.
“Kishiya ta ce ta sama ɗana guba, yana can asibiti”
Kowa Amsar data ke basa kenan. Su kuma sai tsinewa Kalsoom Albarka suke suna aybantata. Kamin ta ƙarasa gurin motarta har ta kira su Momy ta faɗa musu.
Wani irin kuka take tana tuƙin motar har cikin ranta take jin abinda Shafa ta faɗa mata. Kamin ta ƙasara asibitin ana ta kiranta numbers ɗin ƴan'uwa da alama suma sun ji ne.
AMIRA POV.
Wani kalar daɗi ne ya baibaye ta tun lokacin data ji Ummi na labarta ma ƴaƴanta Abdool na nan zuwa dan sun gama meeting ɗin da zasu yi, ya samu free days zai dawo gida yayi su, daman tun faruwar abin nan be zo gida ba.
A ranta take shirya irin nata tabarda zata masa, wanda take tunanin zai ɗauki hankalinsa izuwa gareta. Girki ne abinda ta fara kawowa a ranta dan tasan ta ƙware a wannan fannin. Sai dai matsalarta ɗaya Amal dan itace mai cewa ba zata ci abinda Amira ta girka ba, a kullum idan Amira tasa hannunta a abincin gidan sai ta ce ba zata ci ba.
Ta baro part ɗin falon inda take zaune ta nufo gurin da Ummi take zaune ta zauna ƙasa kusa da Ummi kamar ta shige jikinta.
“Eh haka nek son ayi idan ya dawo sai kuje a duba gidan nan a gyara a zuba sabbin ƴan haya, dan gidan marayu ba a barinsa haka”
Sai da Ummi ta ƙare zancen da take sannan ta kalli Amira dake ƙasa zauna tana murmushi.
“Amira akwai da son jiki kamar Abdool”
Amira tayi murmushi idonta na cika da hawaye.
“Haka nake jin ki kamar mamana kina tuna min da mamana sosai, yanayin rayuwarki”
Hawaye ya silalo daga idon Amira, wannan maganar har cikin zuciyar Amira take, tabbas tayi missing Ammy gashi kuma bata san ranar da zata sake haɗuwa da ita ba, bata san halin da take ciki ba.
Zubar hawayen Amira yasa Ummi ta ji babu daɗi, wannan karon da kanta tasa hannunta ta share mata hawaye.
“Ki daina kuka kin ji? Zan zame miki uwa inshallah, kuma nan gaba zaki koma gurin uwarki na miki alƙawari”
“Na gode”
Ta rumgume Ummi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya........
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *54*
Hankali a tashe ta isa asibitin, hawaye na bin fuskarta. Duk wanda ya ganta a lokacin sai ya tausaya mata dan sun san abinda ya kawo ta asibitin. Daman tuni labarin ya karaɗe asibitin cewa Amarya Doc ta saka ma ƙaramin ɗansa guba. Sai ma a yanzu ne wasu ne suke jin cewar Doc ya rabu da Rashida.
Kowa tsinewa Kalsoom yake wasu na faɗin daman kishiyoyin yanzu haka suke su shigo su kore uwargida kuma su mallake ƴaƴan miji da miji.
Wani irin banka tayi ma ƙofar office ɗin Hilal ta shiga kamar zata tashi ɗakin.
“Ina ɗa na yake?”
Shine abinda ta tambaya hawayen na bin fuskarta. Ɗagowa yayi daga dafe da kan da yake ya kalleta. Be yi msmakin ganinta ba daman yasan zata zo tun da akwai ƴan'uwanta a asibitin da zasu kai mata labari.
“Ina ɗa na yake Hilal?”
Ya sake tambaya ganin yayi mata ƙuri da ido kamar ba dashi take magana ba.
“Ɗan ki ko ɗa na?”
“Ɗa na, si kai baka san zafin sa ba da baka bari wata ta kai ga ba shi guba ba”
Miƙewa yayi tsaye ya daki teburin dake gabansa.
“How dare you, idan kin san zafinsa ai bs zaki taɓa zuwa wani gurin ki aikata zina ba, ba zaki taɓa bada kan ki ga kowa ba sai ubansu, amman haka kika taka igiyar aure Rashida kika tsallae ƴaƴanki kika aikata zina da namijin da ba muharramin ki ba, na ƴi nadamar haɗa zuri'ah dake da ace wats na aura ba da rayuwar ƴaƴana bata kasance a halin data kasance a yanzu ba”
Tun da yake maganar take baya baya har ta jingiya da ginin ƙofar idonta na hawaye.
“I need to my son”
“You won't see him”
Ta muna kanta yana mamakin yadda duniyar Hilal ta birkice mata.
“Hilal ni ce!”
“And so what? Get the hell out of my office”
“Kotu zata raba mu da kai ba zan ƙyale kai da matarka ku kashe min ɗa ba”
Ta buɗe ƙofar da ƙarfi ta fice. Be damu ba dan yasan ya riga ya kulle ɗakin da Rafiq yake ciki tun bayan tafiyar Kalsoom.
Ba shida wani aiki amman haka ya zauna a office ɗin dan baya son zuwa gida kwata-kwata gidan ya fita aransa.
Haka ya riƙa karɓar masu shigowa suna masa jajen abinda ya faru tare da masa Allah ya tsare gaba, wasu kan tambaye shi ta ya lamarin ya faru wasu kuma su kuma basa tambaya ganin kamar cin fuska ne.
Bayan yayi salla magariba ya koma ɗakin da Rafiq yake ya zauna yana kallonsa. Ga dukan alamu ya samu sauƙi dan bachinsa yake hankali kwance, humfashinsa na tafiya dai-dai kamar yadda ake so. Ana daf da kiran salla isha'i Hajiya ta iso tare da wasu ƙanensa.
Hilal na ganinta ya tashi a kujerar da yake zauna ya miƙa mata ta zauna, sannan ya soma miƙa mata gaisuwa. Bata karɓa ba ta kalli Rafiq cikin tausayi tace
“Hilal ya aka yi haka ta faru? Wai Kalsoom tasa masa guba?”
Shiru yayi yana tunanin ta ta inda zai soma maganar da bata daɗin faɗi. Idan har ya amsa da ita ɗin ce bashi da tabbaci ita ɗin ce idan kuma ba ita ba ce to wanene bayan daga ita sai Rafiq ne abin ya faru?
“Wallahi ina meeting ta kirana ni ban ɗaga ba sai daga baya na kirata sai ta ce min na zo fida Rafiq babu lafiya, ina zuwa na tarar bakinsa na kumfa ko da na ɗauko na kawo sa asibiti kamar ba zai yi rai ba, bincike dai ya nuna guba ya ci. Tun ɗazu aka masa hoto amman ban karɓo ba”
Hajiya ta taɓa hannu tana salati.
“O o ita kuma haka take? Hilal baka dace da matan ƙwarai, yanzu ɗan wannan ƙaramin yaro ko kashe tayi me zata ji? Kai duniya”
Shi dai yayi shiru be ce komai ba, hannyensa zube a aljihu. Kamin su ƙara cewa wani abu sai ga Ummu Faisak ta turo ƙofa ta shigo fuska babu annuri irin yau tana cikin masifa ɗin nan.
Hajiya tayi mata kallon marar kunya da tarbiya ganin yadda take huci kamar baƙin maciji.
“Haba Maman Faisak ai ko ɗakin kafirai ne kya dokko ƙofa kamin ki shigo balle musulmai”
Uffan bata cewa Hajiya dan tana cikin zafin rai tasan kuma idan har tace zata tsaya maidawa Hajiya magana to dukansu rayuwarsu sai ta ɓace dan Hilal ba ƙyalewa zai yi ba.
“Ɗa zu Adda Rashida ta zo nan ka hana ta shiga ta ga ɗan ta, akan wanenen dalili ko ita ba uwarsa bace? Ba zamu ɗauki tsarin wulaƙancin da kake son mana ba akan shegiyar matar ka, ta fitar da Rashida cikin gidan yanzu kuma tana son ta bi ƴaƴanta ya kashe, idan ba zaka iya wani abu ba mu za mu iya dan ba zamu zuba ido ta kashe mana ƴaƴa ba”
Wani wulaƙantancen kallo Hilal ya watsa mata kana yaja tsaki, sannan ya kai hannu ya kwaɓe wayar wata ƙanwar Rashida dake ɗaukar Rafiq a waya.
“Ku fita ku bani guri ko nasa ayi muku wulaƙanci, idan ita Rashida bata iya ba ke taya zaki iya, banza a banza, ko dan kina ƴar jarida? Ku fitar min daga office yanzu nan”
“Za mu fita ai bamu zo dan zama ba, amman ka jira sakamakon ka, ba za mu ɗauki a wulaƙanta mana ƴar'uwa ba”
Cewar Khady sannan ta duƙa ta ɗauki wayarta, Suka fice. Hajiya ta dafe kai.
“O Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, wannan masifa da me ta yi kama? Hilal ka rabu da matar nan ka huta daman masu tsantsar ladabi sun fi komai cuta”
Balki ta taɓe baki.
“Ni wallahi ban zata Kalsoom zata iya aikata haka ba, shiyasa ake cewa baka shedun mutum, mutum mugun ice”
“Hilal ka rabu da matar nan tun wuri kamar abin yayi maka yawa, ko ma shari'ah za su yi da ita suje can su yi amman ba tana gidan ka ba, sannan duk mace data fara da ƴaƴanka wata rana akan ka zata faɗa”
“Idan na rabu da ita kuma.. Da wa zan zauna”
“Sai ka nemi ƴar gidan malamai ka aura, kai ni ma zan nema maka ga mu da su a family masu hankali da natsuwa”
“Amman Hajiya zai zama ina ta aure aure”