Sashe 17
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata zaton da wata manufar Amira take son ta saka rigar, dan ko a mafarki bata zaton Amira zata iya cutar ta ko kuma a haɗa kai da ita a cuce ta. Sai kawai ta kai hannu ta karɓa, a gaban Amira ta ɗaura zanen rigar kuma da zata saka sai da tayi Bismillah, hakan kuma ba ƙaramin tsoro ya bawa Amira ba, sai dai bata yarda ta nuna ba, har suka fito tare suka nufi garden ɗin.
Wayarta ta ciro ta aika ma Uzair da text.
‘Ta saka yanzu, amman Haila be zo mata ba, na san dai ze zo mata tana sanye da ita’
Ƙarkashin bishiyar mangoro Namra ta zauna, kasancewar ta riga Amira isa gurin, kamin ta zauna taji wayarta tayi ƙara alamar saƙo, sai kawai ta fasa zaman sai ta koma gefen tana ƙoƙarin buɗe saƙon.
‘Amira you fuck up’
Ba shiri ta zaro ido ganin irin reply ɗin da yayi mata.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12_28.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 13*
Hankalinta ya tashi sosai, har ta kasa jin kiran da Namra take mata, sai da ta yi mata kiran kusan sau huɗu sannan ta amsa kamar a firgice ta juyo ta kalleta.
“Lafiya?”
Namra ta tambaya ganin yanayinta duk ya canja.
Ƙasarowa tayi kusa da ita ta dafa ta tana faɗin.
“Ba komai, Yaya ne yayi min text ina jin Ammy ba lafiya bari naje gida”
“Ko na raka ki?”
“A'a No yi zamanki da sauƙi ai”
Bata tsaya jiran abunda Namra zata ƙara cewa ba, ta nufu hanyar fita da sauri. Hankalin Namra sai duk ya tashi tana jin kamar mahaifiyarta ta ce, har ta unƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna hango Maryam da tayi tafe ta doso inda take. Kusa da ita ta zauna ta aje hangout ɗinta gabanta tana ƙoƙarin cire hijabinta.
“Anty Namra yanzu shikenan kin yi watsi da karatun ki ko?”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Haba Maryam kina min wannan maganar kamar ba kisan halin da nake ciki ba?”
“Allah ya kyauta! Amman ai ke kika jawa kan ki, ya dai kamata ace kin fara yima kan ki karatun ta natsu, ba wai azo a zuga ki kawai ki hau kan layi ba”
“Maryam babu wanda ya zuga ni, kawai kisan bawa baya wuce kaɗɗararsa, dan Allah ki daina ganin laifin Amira”
“Ba laifi ta nake gani ba, amman dai ina tunatar da ke kiyi hankali da yarinyar nan, jikina yana bari babu alheri a abotar nan taku, dan ni tun ba yau na lura da irin shigo-shigo ba zurfi da Amira take miki, dan tana kishin ki”
“Amira bata da wannan Maryam baki fahimce bana”
“Bata da wannan, take kishin ki? Yai Amira tana baƙinciki ta ga kin ɗinka sabon kaya ita ata ɗinka ba, Amira tana baƙincikin ace kin fita zarra a jarabawa, Amira bata ƙaunar a tare ki a hanya ita ba'a tare ta ba, in yau kika saye sabon takalmi sai Amira ta siye, idan aBun farin ciki ya same ki a take Amira take canja fuska, idan wani abu kika samu sai tasan yadda ta shiga ta fita kika hallakarda da shi sannan hankalinta ya kwanta, ke duk baki lura da hakan ba?
Anty Namra ƙarshen duniya muke fa, kuma Annabi da kansa ya faɗa a cikin alamomin ƙarshen duniya akwai rashin amana da cin amana da rashin yarda, Wallahi kiyi hankalin da mutane.
In ma wani sirrin ki ne karki ƙara faɗawa Amira, dan daga lokacin da ke da kanki kika kasa ɓoye sirrinki a cikin cikinki, har kika faɗawa Amira Wallahi kamar kin faɗawa duniya ne”
Namra tayi shiru tana kallon yadda Maryam take tsire baki tana faɗin maganganun, zuciyarta na nazarin kalamanta. Ita kanta a yanzu tana zargin Amira tun daga abunda ya faru da ita, sai dai yadda Amira take nuna mata akwai Aminci a tsakanin su ya kan rikita zarginta.
“Forget about Amira, yanzu dai Abbah yace ki kawo Asim ze aura miki shi how do you feel?”
“I don't know, amman ina jin kamar ban kyautawa Abbah ba, kuma ba zai fahimce ni ba, idan kuma na kawo wani wanda ba Asim na aura Asim zai cigaba da kallo a matsayin mayaudariya, ban san yadda zan yi ba”
“Yanzu dai Uzair ya fasa auren ki, dan haka duk wanda zaki aura babu ruwan Abbah ba kuma ze karɓi wani excuse daga gare ki ba, kinga ƙara ma ki auri Asim ɗin, in yaso sai kiji da Abbah”
“Maryam ban san inda Asim yake ba, Mahaifiyarsa ma tace min bata san inda yake ba, saboda ni ya bar garin nan”
“Ƙarya take tace bata san inda yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai gudu be faɗawa mahaifiyarsa ba? Baya gari ya akayi Amira ta ganshi?”
“Nima ban sani ba, tace min kiranta yayi a waya”
“Kin gani ko? Wannan Amirar munafukace. Ni zan taya ki nemansa, har gurin uwarsa zanje idan kuma tayi min maganar banza na ci mata mutunci”
“A'a ni dai dan Allah karki mata rashin mutunci, ki bita da lalama”
“Ke fa Anty Namra kina da matsala, mutanen duniya in ka sake sai su ci maka tuwo a ka, kawai idan mutum ya maka zuma sai ka masa wuta, idan kuma ya maka yayyafi sai ka masa ruwa”
“Nidai na ji amman ban da rashin mutunci kinji?”
Ta tsire baki gefe.
“Naji tashi mu shiga ciki, ni yunwa ma nake ji ganin Amirar yasa na shigo nan”
Miƙewar da Namra zatayi sai taji abu ya gangaro mata a ƙafa, tana ɗaga zagen taga jini. Lumshe ido tayi ta buɗe ta kalli Maryam dake kallonta sannan ta riƙa hannunta suka shiga ciki.
Suna shiga Maryam ta nufi kitchen, Namra kuma ta nufi ɗakinta, ta cire kayan jikinta ta gyara jikinta ta saka pad sannan ta saka wasu tufafin.
UZAIR POV.
Sai safa da marwa yake, hankalinsa ya kasa kwanciya, tun lokacin da Amira ta masa text ɗin shirmen data aikata. What if aikin ya dawo gareshi? Tun da malamin yace indai akayi aikin dole ne ya ci.
Najeeb ya dafa shi
“Uzair ka kwantar da hankalin ka mana”
“Haba Najeeb wane irin kwantar da hankali kamar baka san yadda abun nan yake ba, kuma kana ganin taje ta aika mana shirme, ban san abunda yake damun ƴar iskar yarinyar nan ba”
“Ka natsu mana sai mu kira malamin mu faɗa masa abunda yake faruwa”
Sai a lokacin ya zauna, tashin hankali ƙarara a fuskarsa. Kira biyu Malamin ya ɗauka, sai Najeeb yayi masa bayanin komai. Malamin ya daɗe yana jimamin abun sai tambayar yadda akayi suka yi wannan kwaɓar yake.
“Yanzu dai mu saurara nan da kwana biyu mu gani”
“Yanzu Malam babu wani abu da za'a iya yi, babu wata mafita?”
“Mafita ɗaya ce, a nemo kurciyar nan acire layar da aka laƙa mata, kasan kuma mun riga mun saki kurciyar kamunta yanzu ba abu ne mai yiyu ba, sai dai kasan ai da sunan ita yarinyar mukayi dan haka ku ɗan dakata tukuna mai yiyuwa ya iya kamata”
“Ko asa ta cire rigar?”
“A'a duk ta cire rigar ba tare da aikin ya shiga jikinta ba, zai iya dawowa, kasan lamarin iska”
“Okay toh mun gode”
Najeeb na kashe wayar Uzair ya miƙe tsaye yana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah ka cece ni Allah”
Jafar ya aje wayar hannunsa ya kalli Uzair yace
“Haba be a Man mana, ai ko aiki zai dawo ba akanka zai koma ba akan Amirar zai koma”
Uzair ya kalleshi
“Amman ai ba ita tayi aikin ba”
“Easy Man ai ita tayi kuskuren, kirata muji yadda tayi wannan banzan shirmen”
Jafar na gama maganar, Uzair ya ciro wayarsa ya danna mata kira.
AMIRA POV.
Kuka take sosai, tun da ta baro gidan su Namra take kuka har ta iso gida. Bata bari Ammy taga shigowarta ba, sai kawai ta shige ɗakinta ta hau kuka baji ba gani. Ita kanta idan za'a tambayeta bata san dalilin kukan ba, ita dai tana jin kuka yana zo mata kawai.
Ganin Number Uzair ce yasa ta ɗauka ta kara a kunne.
“Amira taya kika yi wannan shirmen? Ban faɗa miki ba a son a samu matsala ba?”
“Ai tasa rigar”
“Toh Uban wa yace ki bari tasa ba tare da haila yazo mata ba? Wace irin mahaukaciya ce ke?”
“Yanzu idan ba a yi dai-dai ba me zai faru?”
“Ban sani ba”
Sai ya kashe wayar. A take zuciyarta ta soma raya mata Namra haukacewa zatayi. Kuma ita za a zarga tun da anga shigarta gidan gashi Maryam ta haɗu da ita, hakan yasa ta fashe da kuka zuciyarta na raya mata lallai asirinta na daf da tonuwa.
Haka ta wuni ta kwana da tunanin abunda ze samu Namra, gashi kukan yaƙi ya tsaya mata, ta takure kanta a ɗaki, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin inda zata samawa kanta mafita, dan ji take kamar wani zai faru da Namra, tun da batayi dai-dai ba, kuma ba makawa ita za a zarga. Ji take duk ta tsani kanta, zuciyarta na raya mata ta gudu kawai kamin asirinta ya tonu.
MARYAM POV.
Daga Makaranta ta wuce gidan iyayen Asim. Cikin ladabi tayi sallama ta shiga. Sai Mahaifiyarsa ta amsa mata dan ita kaɗaice yau a gidan. Har ƙasa Maryam ta risina ta gaishe ta. Ta ta ɗan kawarda fuskarta dan ta gane ƙanwar Namra ce tun da sun taɓa zuwa tare da ita.
“Lafiya ƙalau”
“Dan Allah ko Asim na nan?”
“Baya nan yayarki ta zo nan na faɗa mata baya nan, ni ma ban san inda yake ba”
Daga nan sai Maryam ta canja salo.
“Kin san inda yake kam, dan babu yadda za'ayi ace uwa kamar ki bata san inda ɗanta yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai bar gida yaje nesa ba tare daya faɗa miki ba”
“Au toh ko ƙarya zan miki, macuta maciya amana, bayan kun gama cin moriyar ɗana sannan zaku watsa masa ƙasa a ido, yanzu dan munafurci ne za ku wani zo nemansa kamar ya ci bashin ku?”
Wayarta ta ciro ta aika ma Uzair da text.
‘Ta saka yanzu, amman Haila be zo mata ba, na san dai ze zo mata tana sanye da ita’
Ƙarkashin bishiyar mangoro Namra ta zauna, kasancewar ta riga Amira isa gurin, kamin ta zauna taji wayarta tayi ƙara alamar saƙo, sai kawai ta fasa zaman sai ta koma gefen tana ƙoƙarin buɗe saƙon.
‘Amira you fuck up’
Ba shiri ta zaro ido ganin irin reply ɗin da yayi mata.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12_28.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 13*
Hankalinta ya tashi sosai, har ta kasa jin kiran da Namra take mata, sai da ta yi mata kiran kusan sau huɗu sannan ta amsa kamar a firgice ta juyo ta kalleta.
“Lafiya?”
Namra ta tambaya ganin yanayinta duk ya canja.
Ƙasarowa tayi kusa da ita ta dafa ta tana faɗin.
“Ba komai, Yaya ne yayi min text ina jin Ammy ba lafiya bari naje gida”
“Ko na raka ki?”
“A'a No yi zamanki da sauƙi ai”
Bata tsaya jiran abunda Namra zata ƙara cewa ba, ta nufu hanyar fita da sauri. Hankalin Namra sai duk ya tashi tana jin kamar mahaifiyarta ta ce, har ta unƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna hango Maryam da tayi tafe ta doso inda take. Kusa da ita ta zauna ta aje hangout ɗinta gabanta tana ƙoƙarin cire hijabinta.
“Anty Namra yanzu shikenan kin yi watsi da karatun ki ko?”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Haba Maryam kina min wannan maganar kamar ba kisan halin da nake ciki ba?”
“Allah ya kyauta! Amman ai ke kika jawa kan ki, ya dai kamata ace kin fara yima kan ki karatun ta natsu, ba wai azo a zuga ki kawai ki hau kan layi ba”
“Maryam babu wanda ya zuga ni, kawai kisan bawa baya wuce kaɗɗararsa, dan Allah ki daina ganin laifin Amira”
“Ba laifi ta nake gani ba, amman dai ina tunatar da ke kiyi hankali da yarinyar nan, jikina yana bari babu alheri a abotar nan taku, dan ni tun ba yau na lura da irin shigo-shigo ba zurfi da Amira take miki, dan tana kishin ki”
“Amira bata da wannan Maryam baki fahimce bana”
“Bata da wannan, take kishin ki? Yai Amira tana baƙinciki ta ga kin ɗinka sabon kaya ita ata ɗinka ba, Amira tana baƙincikin ace kin fita zarra a jarabawa, Amira bata ƙaunar a tare ki a hanya ita ba'a tare ta ba, in yau kika saye sabon takalmi sai Amira ta siye, idan aBun farin ciki ya same ki a take Amira take canja fuska, idan wani abu kika samu sai tasan yadda ta shiga ta fita kika hallakarda da shi sannan hankalinta ya kwanta, ke duk baki lura da hakan ba?
Anty Namra ƙarshen duniya muke fa, kuma Annabi da kansa ya faɗa a cikin alamomin ƙarshen duniya akwai rashin amana da cin amana da rashin yarda, Wallahi kiyi hankalin da mutane.
In ma wani sirrin ki ne karki ƙara faɗawa Amira, dan daga lokacin da ke da kanki kika kasa ɓoye sirrinki a cikin cikinki, har kika faɗawa Amira Wallahi kamar kin faɗawa duniya ne”
Namra tayi shiru tana kallon yadda Maryam take tsire baki tana faɗin maganganun, zuciyarta na nazarin kalamanta. Ita kanta a yanzu tana zargin Amira tun daga abunda ya faru da ita, sai dai yadda Amira take nuna mata akwai Aminci a tsakanin su ya kan rikita zarginta.
“Forget about Amira, yanzu dai Abbah yace ki kawo Asim ze aura miki shi how do you feel?”
“I don't know, amman ina jin kamar ban kyautawa Abbah ba, kuma ba zai fahimce ni ba, idan kuma na kawo wani wanda ba Asim na aura Asim zai cigaba da kallo a matsayin mayaudariya, ban san yadda zan yi ba”
“Yanzu dai Uzair ya fasa auren ki, dan haka duk wanda zaki aura babu ruwan Abbah ba kuma ze karɓi wani excuse daga gare ki ba, kinga ƙara ma ki auri Asim ɗin, in yaso sai kiji da Abbah”
“Maryam ban san inda Asim yake ba, Mahaifiyarsa ma tace min bata san inda yake ba, saboda ni ya bar garin nan”
“Ƙarya take tace bata san inda yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai gudu be faɗawa mahaifiyarsa ba? Baya gari ya akayi Amira ta ganshi?”
“Nima ban sani ba, tace min kiranta yayi a waya”
“Kin gani ko? Wannan Amirar munafukace. Ni zan taya ki nemansa, har gurin uwarsa zanje idan kuma tayi min maganar banza na ci mata mutunci”
“A'a ni dai dan Allah karki mata rashin mutunci, ki bita da lalama”
“Ke fa Anty Namra kina da matsala, mutanen duniya in ka sake sai su ci maka tuwo a ka, kawai idan mutum ya maka zuma sai ka masa wuta, idan kuma ya maka yayyafi sai ka masa ruwa”
“Nidai na ji amman ban da rashin mutunci kinji?”
Ta tsire baki gefe.
“Naji tashi mu shiga ciki, ni yunwa ma nake ji ganin Amirar yasa na shigo nan”
Miƙewar da Namra zatayi sai taji abu ya gangaro mata a ƙafa, tana ɗaga zagen taga jini. Lumshe ido tayi ta buɗe ta kalli Maryam dake kallonta sannan ta riƙa hannunta suka shiga ciki.
Suna shiga Maryam ta nufi kitchen, Namra kuma ta nufi ɗakinta, ta cire kayan jikinta ta gyara jikinta ta saka pad sannan ta saka wasu tufafin.
UZAIR POV.
Sai safa da marwa yake, hankalinsa ya kasa kwanciya, tun lokacin da Amira ta masa text ɗin shirmen data aikata. What if aikin ya dawo gareshi? Tun da malamin yace indai akayi aikin dole ne ya ci.
Najeeb ya dafa shi
“Uzair ka kwantar da hankalin ka mana”
“Haba Najeeb wane irin kwantar da hankali kamar baka san yadda abun nan yake ba, kuma kana ganin taje ta aika mana shirme, ban san abunda yake damun ƴar iskar yarinyar nan ba”
“Ka natsu mana sai mu kira malamin mu faɗa masa abunda yake faruwa”
Sai a lokacin ya zauna, tashin hankali ƙarara a fuskarsa. Kira biyu Malamin ya ɗauka, sai Najeeb yayi masa bayanin komai. Malamin ya daɗe yana jimamin abun sai tambayar yadda akayi suka yi wannan kwaɓar yake.
“Yanzu dai mu saurara nan da kwana biyu mu gani”
“Yanzu Malam babu wani abu da za'a iya yi, babu wata mafita?”
“Mafita ɗaya ce, a nemo kurciyar nan acire layar da aka laƙa mata, kasan kuma mun riga mun saki kurciyar kamunta yanzu ba abu ne mai yiyu ba, sai dai kasan ai da sunan ita yarinyar mukayi dan haka ku ɗan dakata tukuna mai yiyuwa ya iya kamata”
“Ko asa ta cire rigar?”
“A'a duk ta cire rigar ba tare da aikin ya shiga jikinta ba, zai iya dawowa, kasan lamarin iska”
“Okay toh mun gode”
Najeeb na kashe wayar Uzair ya miƙe tsaye yana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah ka cece ni Allah”
Jafar ya aje wayar hannunsa ya kalli Uzair yace
“Haba be a Man mana, ai ko aiki zai dawo ba akanka zai koma ba akan Amirar zai koma”
Uzair ya kalleshi
“Amman ai ba ita tayi aikin ba”
“Easy Man ai ita tayi kuskuren, kirata muji yadda tayi wannan banzan shirmen”
Jafar na gama maganar, Uzair ya ciro wayarsa ya danna mata kira.
AMIRA POV.
Kuka take sosai, tun da ta baro gidan su Namra take kuka har ta iso gida. Bata bari Ammy taga shigowarta ba, sai kawai ta shige ɗakinta ta hau kuka baji ba gani. Ita kanta idan za'a tambayeta bata san dalilin kukan ba, ita dai tana jin kuka yana zo mata kawai.
Ganin Number Uzair ce yasa ta ɗauka ta kara a kunne.
“Amira taya kika yi wannan shirmen? Ban faɗa miki ba a son a samu matsala ba?”
“Ai tasa rigar”
“Toh Uban wa yace ki bari tasa ba tare da haila yazo mata ba? Wace irin mahaukaciya ce ke?”
“Yanzu idan ba a yi dai-dai ba me zai faru?”
“Ban sani ba”
Sai ya kashe wayar. A take zuciyarta ta soma raya mata Namra haukacewa zatayi. Kuma ita za a zarga tun da anga shigarta gidan gashi Maryam ta haɗu da ita, hakan yasa ta fashe da kuka zuciyarta na raya mata lallai asirinta na daf da tonuwa.
Haka ta wuni ta kwana da tunanin abunda ze samu Namra, gashi kukan yaƙi ya tsaya mata, ta takure kanta a ɗaki, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin inda zata samawa kanta mafita, dan ji take kamar wani zai faru da Namra, tun da batayi dai-dai ba, kuma ba makawa ita za a zarga. Ji take duk ta tsani kanta, zuciyarta na raya mata ta gudu kawai kamin asirinta ya tonu.
MARYAM POV.
Daga Makaranta ta wuce gidan iyayen Asim. Cikin ladabi tayi sallama ta shiga. Sai Mahaifiyarsa ta amsa mata dan ita kaɗaice yau a gidan. Har ƙasa Maryam ta risina ta gaishe ta. Ta ta ɗan kawarda fuskarta dan ta gane ƙanwar Namra ce tun da sun taɓa zuwa tare da ita.
“Lafiya ƙalau”
“Dan Allah ko Asim na nan?”
“Baya nan yayarki ta zo nan na faɗa mata baya nan, ni ma ban san inda yake ba”
Daga nan sai Maryam ta canja salo.
“Kin san inda yake kam, dan babu yadda za'ayi ace uwa kamar ki bata san inda ɗanta yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai bar gida yaje nesa ba tare daya faɗa miki ba”
“Au toh ko ƙarya zan miki, macuta maciya amana, bayan kun gama cin moriyar ɗana sannan zaku watsa masa ƙasa a ido, yanzu dan munafurci ne za ku wani zo nemansa kamar ya ci bashin ku?”