Sashe 8
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har yanzu Asim baya ɗaukar wayarta, ta masa text ya fi a ƙirga, amman ba reply, kuma tun ranar da suka samu matsala bata sake saka shi a idonta ba, scul ma ya daina zuwa.
Hakan yasa ta yanke shawarar jan ƙawarta Amira su je gidan iyayensa, dan dubasa.
Haka kuwa akayi bayan an gama lacca, sun fito ita da classmates ɗin su, sai ta riƙa hannun Amira ta nufi hanyar library da ita.
Amira biye kawai take da ita, amman hankalinta na can wani gurin, sai tunani take.
Saman balcony suka zauna, kamin Namra ta yi magana sai Amira ta fara yi mata tambayar da ke cikin ranta.
“Namra kin ce da Uzair aka sa muku rana ko? Kuma kin ce baki son sa right?”
“Uhm”
“Ba taimakon ki zai yi ba?”
Namra ta yi mata kallon rashin fahimta
“Taimako kamar ya?”
“Haka dai na ji ana faɗa wai taimakon ki zai yi, dan Abbah ya bari ki auri wanda kike so”
“Kowa ya faɗa miki haka ƙarya ne, idan har zan nemi taimakon wani toh ke ce zaki riga kowa sani”
“Amman miyasa baki son sa?”
Shiru tayi, tana tunanin faɗa mata gaskiyar lamarin, sai dai tana jin har yanzu Amira bata kai matsayi da zata san sirrin gidan su ba, wannan matsalar ta cikin gida ce kawai, kuma ba komai bane zaka faɗawa ƙawa, dan ba kowa bane zai iya riƙe maka sirrinka, wani kuma zai yi kallon ka da abun ne, duk kuwa da amincin da ke tsakaninku.
“Amira so na ke ki raka ni gidan su Asim”
Ta ɗauko mata zancen ne, dan samun damar kawarda wancan tambayar da tayi mata.
Ajiyar zuciya Amira ta sauke, har yanzu kan ta kulle yake ta rasa dalilin da yasa Uzair ya yi mata ƙaryar yana son ta, kuma ya ƙulla alƙawarin zai aureta, lalai akwai wani abu a ƙasa.
“Zan raka ki mana, kwana biyu ya daina zuwa makaranta, nima ina tunani ko lafiya?”
Ta faɗa lokacin da Namra ta girgiza tana maimaita mata zancen.
“Tashi muje kamin four ta yi”
Namra taja hannunta suka tashi. Har suka isa gidan, Amira tunanin maganar Namra take, wani ɓangare na zuciyar na nuna mata lallai Uzair so yake ya yaudareta.
Namra nayin parking ta dafa Amira, ganin tun ɗazu hankalinta baya jikinta.
“Wai lafiya kike kuwa?”
Saurin buɗe motar ta yi, gudun kar Namra ta samu damar zargin wani abu.
“Lafiya ƙalau, fito muje”
Fitowa Namra ta yi gabanta na faɗuwa, a bakin ƙofar gidan ta tsaya tana tunanin abunda zata ce musu idan ta shiga.
Amira ce ta yi sallama taja hannun Namra suka kunna kai cikin gidan.
Ƙannen Asim ne suka amsa mata, mahaifiyarsa na haɗa ido da Namra, ta sauke kai ta cigaba da ƙullin zoɓonta kamar bata gansu ba.
Har ƙasa Namra ta risina ta gaisheta, yayinda Amira ta gaisheta a tsaye. Can ƙasan maƙoshinta ta amsa musu, fuska a haɗe kamar ta ga mutuwarta. Kasa magana Namra tayi, har sai da Amira ta ce
“Umma ko Asim na nan?”
Ɗago kai ta yi tana musu wani ƙazamin kallo.
“Ai ku zan tambaya, dan yau kusan sati uku kenan, ban saka Ibrahim a ido ba, tun ranar da ya zo nan yana hawaye yace kin cuceshi, ban sake ganinsa ba, ni kaina nemansa nake”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa idonta na ƙoƙarin cika da ƙwalla.
“Wani Innalillahi zaki yi? Ashe kin san Allah? Babu irin roƙon da ban miki ba akan ki rabu da Ibrahim amman kika ƙi, duk irin maganar da na masa a banza saboda idon sa, ya rufe akan ki”
Amira ta yi saurin saka bakinta.
“Wallahi Umma ba haka ba ne, ita kanta Namra tana son Asim, laifin mahaifinta ne”
“Ni ban tambaye ku laifin kowa ba, dan Allah ku fitar min daga gida, kuma wallahi sai Allah ya saka masa”
Har suka fito kuka Namra take, kasa tuƙa motar ta yi, sai Amira ce tayi driving ɗinsu.
“Yanzu ina Asim ya tafi? Duk abunda ya same shi ni ce sila, ba zan yafewa kai na ba”
“Namra ki daina kukan nan indai ba so kike muje gida a riƙa tambayar ki me ya faru ba. Ke ni fa ban ma yarda da zancen ta ba, ta ya za'a ce namiji kamar Asim ya bar gidan iyayensa dan kawai ya rabu da ke? Ai wannan fashion ɗin ya wuce”
“Zai iya saboda gudun waɗanda za su masa dariya, kuma ɓacin rai babu abunda ba ya sawa Amira”
“Amman ke dan Allah rabuwa da shi be fi miki alheri ba? Saboda shi kika ɓata da duk samarin ki, kuma mahaifinki ya ɓata da ke, shiyasa ma yanzu yake ƙoƙarin miki auren dole, abunda aka bar yayi tun kakanni”
Shiru Namra bata ƙara cewa komai ba har Amira ta yi parking a bakin gate ɗin gidansu Namra, dan bata jin shiga cikin gidan, ita ma kanta tana da nata damuwar.
“Ni dai zan wuce, idan kin gama kukan sai ki shiga da motar ciki”
Bata jira abunda zata ce ba, ta buɗe motar ta fice. Sai da Namra tayi kusan minti talatin a gurin sannan ta buɗe motar ta fito ta dawo mazaunin direba ta yi ma motar key tare da horn.
Mai gadin na buɗe mata gate, ta shiga da gudu har sai da tayi kaura da wata motar dake gabanta fake.
Buɗewa tayi ta fito, tana cigaba da kukan ta nufi part ɗinsu.
Anty Amarya na tsaye jikin window tana kallon abunda Namra ta yi, tasan Namra da zafin zuciya nan gaba har kanta zata iya jima ciwo da motar, ranta ya ɓace sosai, ita kanta ta damu da halin da ƴarta take ciki, sai dai babu abunda zata iya yi tun da ita ta jawo kanta haka tun farko.
Namra na shigowa Anty Amarya ta miƙa mata hannu.
“Bani makulin motar?”
Ba musu ta miƙa mata, tana share hawayenta, bayan Anty Amarya tace ta karɓi key ɗin tace
“ATM ɗin Abbanki yana nan na aje miki, shi ya aiko yace a baki yace ki ciri ko nawa kike so ki yi lalurarki, kuma yace ki samu ƙawayen ki ku rubuta events ɗin da zaku yi, on Wednesday za'a kawo lefen ki da IV”
Wani irin abu ta ji ya ratsa zuciyarta, idonta cike da ƙwalla ta kalli Anty Amarya.
“A tunani na uwa ce zata fi kowa fahimtar halin da ɗan ta yake ciki. Ke kika haife ni, ke kika raine ni har na kawo yanzu, ashe be isa yasa ki karance wacece ni ba? Ashe za'a iya zuwa a'ce miki nayi kisan kai kuma ki yarda? ”
Anty Amarya ta sauke ajiyar zuciya.
“Namra kin yi furucin ne a idan ba zan iya goge zanen rubutun ba, ba zan iya musu da Baban ki ba, idan har na goya miki baya wajen butulce masa duniya zata zage mu, shi kuma ayi masa dariya ace ƴar waje na tafi ƙarfin sa. Ban san dalilinki ba, amman nasan na za ki yi ma Uzair irin wannan sheirin ba haka kawai ba, amman ni da ke duk babu abunda za mi iya yi”
“Na gode da kika fahimta, na gode da zuciyarki ta raya miki ba ƙazafi na yi ma Uzair ba, Allah ya fahimtar da Abbah”
Anty Amarya tace
“Namra ina nan ina miki addu'ah, idan auren ki da Uzair ba alheri ba ne kada Allah ya bari ayi shi”
Da kuka ta rumgune Anty Amarya
“Na gode”
Anty Amarya ta riƙa hannunta suka zauna, ta soma tambayarta taya ta ga Uzair yana aikata wannan mummunan aiki na luwaɗi, kuma miye hujjarta.
Babu abunda Namra ta ɓoye Anty Amarya, tun daga lokacin daya fara nemanta, har zuwa lokacin data kamashi da friends ɗinsa da irin gargaɗin da ya yi mata.
Anty Amarya taja wani dogon numfashi ta sauke tana jinjina lamarin.
“Lallai Uzair ya cika tantiri, shine kuma ya zagayo ya zo neman aurenki?”
“Ina tunanin yayi hakan ne dan Anty Namra ta rufa masa asiri, tun da mijinta ne ai ba zata tona masa asiri ba, kuma kin ga yanzu data faɗa sai ta zama ita ce mai laifi”
Cewar Maryam tana riƙe ƙoƙarin zama kusa da Namra.
“Amman miyasa baki faɗa min ba tun farko? Miyasa kika kirashi a waya kika masa cin mutunci? da wannan ne ya zagayo yazo ya ɗaure ki a gurin Abbanki, miyasa ba ku shawara idan zaku yi abu?”
Namra ta share hawayenta.
“Ban zaci abun zai zame min haka ba, nayi tunanin zai ji tsoro ya janye maganar auren ne”
“A ƙasashen yahudawa Uzair yayi karatu, ya fiki iya makirci, kuma mai son abun ka ya fi ka dabara”
Maryam ta kalli Anty Amarya
“Yanzu meye abun yi?”
“Abun yi kawai mu duƙufa da addu'ah, daga ke har ita, kuma In'shallahu wannan aure Allah ba zai bari a yi shi ba, tun da akwai zalumci a ciki”
Sun daɗe zaune a falo suna firar, sannan Namra ta tashi ta nufi ɗakinta zuciyarta cike da sassauci. Daf da zata shige Maryam ta kira ta
“Anty Namra”
Juyowa ta yi, ta amsa murya a daƙishe
“Na'am”
“Ki sawa zuciyarki sanyi, Mama na tare da ke, nima ina tare da ke, Allah ma yana tare dake, kuma zai kawo miki mafita”
Daga inda take tsaye ta ɗan murmusa
“Na gode Maryam”
Ko ba komai ƴar hirar da suka yi, da goyan bayan da suka nuna mata, yasa ta samu kanta da ɗan sakewa, tsaɓanin baya da take ganin kamar ita kaɗai ce a cikin matsalar.
Daman komai na duniya yana son tattaunawa, ta haka ne zaka fahimci wasu, wasu kuma su fahimce ka, matuƙar kace zaka kulle sirrinka a zuciyarka, shine mataki na farko wajen gurɓata tunaninka, da jawa kanka ciwo.
Sai dai duk da haka maganar da Mahaifiyar Asim ta yi mata ɗazu ta tsaya mata a rai, cewar Allah sai ya saka masa, yasa jikinta sanyi, da kuma zancen bata san inda ɗanta yake ba.
“Ina ka shiga Asim? Miyasa zaka yi haka? Zaka lalata karatun ka, ka guji iyayenka saboda ni Asim?”
Hakan yasa ta yanke shawarar jan ƙawarta Amira su je gidan iyayensa, dan dubasa.
Haka kuwa akayi bayan an gama lacca, sun fito ita da classmates ɗin su, sai ta riƙa hannun Amira ta nufi hanyar library da ita.
Amira biye kawai take da ita, amman hankalinta na can wani gurin, sai tunani take.
Saman balcony suka zauna, kamin Namra ta yi magana sai Amira ta fara yi mata tambayar da ke cikin ranta.
“Namra kin ce da Uzair aka sa muku rana ko? Kuma kin ce baki son sa right?”
“Uhm”
“Ba taimakon ki zai yi ba?”
Namra ta yi mata kallon rashin fahimta
“Taimako kamar ya?”
“Haka dai na ji ana faɗa wai taimakon ki zai yi, dan Abbah ya bari ki auri wanda kike so”
“Kowa ya faɗa miki haka ƙarya ne, idan har zan nemi taimakon wani toh ke ce zaki riga kowa sani”
“Amman miyasa baki son sa?”
Shiru tayi, tana tunanin faɗa mata gaskiyar lamarin, sai dai tana jin har yanzu Amira bata kai matsayi da zata san sirrin gidan su ba, wannan matsalar ta cikin gida ce kawai, kuma ba komai bane zaka faɗawa ƙawa, dan ba kowa bane zai iya riƙe maka sirrinka, wani kuma zai yi kallon ka da abun ne, duk kuwa da amincin da ke tsakaninku.
“Amira so na ke ki raka ni gidan su Asim”
Ta ɗauko mata zancen ne, dan samun damar kawarda wancan tambayar da tayi mata.
Ajiyar zuciya Amira ta sauke, har yanzu kan ta kulle yake ta rasa dalilin da yasa Uzair ya yi mata ƙaryar yana son ta, kuma ya ƙulla alƙawarin zai aureta, lalai akwai wani abu a ƙasa.
“Zan raka ki mana, kwana biyu ya daina zuwa makaranta, nima ina tunani ko lafiya?”
Ta faɗa lokacin da Namra ta girgiza tana maimaita mata zancen.
“Tashi muje kamin four ta yi”
Namra taja hannunta suka tashi. Har suka isa gidan, Amira tunanin maganar Namra take, wani ɓangare na zuciyar na nuna mata lallai Uzair so yake ya yaudareta.
Namra nayin parking ta dafa Amira, ganin tun ɗazu hankalinta baya jikinta.
“Wai lafiya kike kuwa?”
Saurin buɗe motar ta yi, gudun kar Namra ta samu damar zargin wani abu.
“Lafiya ƙalau, fito muje”
Fitowa Namra ta yi gabanta na faɗuwa, a bakin ƙofar gidan ta tsaya tana tunanin abunda zata ce musu idan ta shiga.
Amira ce ta yi sallama taja hannun Namra suka kunna kai cikin gidan.
Ƙannen Asim ne suka amsa mata, mahaifiyarsa na haɗa ido da Namra, ta sauke kai ta cigaba da ƙullin zoɓonta kamar bata gansu ba.
Har ƙasa Namra ta risina ta gaisheta, yayinda Amira ta gaisheta a tsaye. Can ƙasan maƙoshinta ta amsa musu, fuska a haɗe kamar ta ga mutuwarta. Kasa magana Namra tayi, har sai da Amira ta ce
“Umma ko Asim na nan?”
Ɗago kai ta yi tana musu wani ƙazamin kallo.
“Ai ku zan tambaya, dan yau kusan sati uku kenan, ban saka Ibrahim a ido ba, tun ranar da ya zo nan yana hawaye yace kin cuceshi, ban sake ganinsa ba, ni kaina nemansa nake”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa idonta na ƙoƙarin cika da ƙwalla.
“Wani Innalillahi zaki yi? Ashe kin san Allah? Babu irin roƙon da ban miki ba akan ki rabu da Ibrahim amman kika ƙi, duk irin maganar da na masa a banza saboda idon sa, ya rufe akan ki”
Amira ta yi saurin saka bakinta.
“Wallahi Umma ba haka ba ne, ita kanta Namra tana son Asim, laifin mahaifinta ne”
“Ni ban tambaye ku laifin kowa ba, dan Allah ku fitar min daga gida, kuma wallahi sai Allah ya saka masa”
Har suka fito kuka Namra take, kasa tuƙa motar ta yi, sai Amira ce tayi driving ɗinsu.
“Yanzu ina Asim ya tafi? Duk abunda ya same shi ni ce sila, ba zan yafewa kai na ba”
“Namra ki daina kukan nan indai ba so kike muje gida a riƙa tambayar ki me ya faru ba. Ke ni fa ban ma yarda da zancen ta ba, ta ya za'a ce namiji kamar Asim ya bar gidan iyayensa dan kawai ya rabu da ke? Ai wannan fashion ɗin ya wuce”
“Zai iya saboda gudun waɗanda za su masa dariya, kuma ɓacin rai babu abunda ba ya sawa Amira”
“Amman ke dan Allah rabuwa da shi be fi miki alheri ba? Saboda shi kika ɓata da duk samarin ki, kuma mahaifinki ya ɓata da ke, shiyasa ma yanzu yake ƙoƙarin miki auren dole, abunda aka bar yayi tun kakanni”
Shiru Namra bata ƙara cewa komai ba har Amira ta yi parking a bakin gate ɗin gidansu Namra, dan bata jin shiga cikin gidan, ita ma kanta tana da nata damuwar.
“Ni dai zan wuce, idan kin gama kukan sai ki shiga da motar ciki”
Bata jira abunda zata ce ba, ta buɗe motar ta fice. Sai da Namra tayi kusan minti talatin a gurin sannan ta buɗe motar ta fito ta dawo mazaunin direba ta yi ma motar key tare da horn.
Mai gadin na buɗe mata gate, ta shiga da gudu har sai da tayi kaura da wata motar dake gabanta fake.
Buɗewa tayi ta fito, tana cigaba da kukan ta nufi part ɗinsu.
Anty Amarya na tsaye jikin window tana kallon abunda Namra ta yi, tasan Namra da zafin zuciya nan gaba har kanta zata iya jima ciwo da motar, ranta ya ɓace sosai, ita kanta ta damu da halin da ƴarta take ciki, sai dai babu abunda zata iya yi tun da ita ta jawo kanta haka tun farko.
Namra na shigowa Anty Amarya ta miƙa mata hannu.
“Bani makulin motar?”
Ba musu ta miƙa mata, tana share hawayenta, bayan Anty Amarya tace ta karɓi key ɗin tace
“ATM ɗin Abbanki yana nan na aje miki, shi ya aiko yace a baki yace ki ciri ko nawa kike so ki yi lalurarki, kuma yace ki samu ƙawayen ki ku rubuta events ɗin da zaku yi, on Wednesday za'a kawo lefen ki da IV”
Wani irin abu ta ji ya ratsa zuciyarta, idonta cike da ƙwalla ta kalli Anty Amarya.
“A tunani na uwa ce zata fi kowa fahimtar halin da ɗan ta yake ciki. Ke kika haife ni, ke kika raine ni har na kawo yanzu, ashe be isa yasa ki karance wacece ni ba? Ashe za'a iya zuwa a'ce miki nayi kisan kai kuma ki yarda? ”
Anty Amarya ta sauke ajiyar zuciya.
“Namra kin yi furucin ne a idan ba zan iya goge zanen rubutun ba, ba zan iya musu da Baban ki ba, idan har na goya miki baya wajen butulce masa duniya zata zage mu, shi kuma ayi masa dariya ace ƴar waje na tafi ƙarfin sa. Ban san dalilinki ba, amman nasan na za ki yi ma Uzair irin wannan sheirin ba haka kawai ba, amman ni da ke duk babu abunda za mi iya yi”
“Na gode da kika fahimta, na gode da zuciyarki ta raya miki ba ƙazafi na yi ma Uzair ba, Allah ya fahimtar da Abbah”
Anty Amarya tace
“Namra ina nan ina miki addu'ah, idan auren ki da Uzair ba alheri ba ne kada Allah ya bari ayi shi”
Da kuka ta rumgune Anty Amarya
“Na gode”
Anty Amarya ta riƙa hannunta suka zauna, ta soma tambayarta taya ta ga Uzair yana aikata wannan mummunan aiki na luwaɗi, kuma miye hujjarta.
Babu abunda Namra ta ɓoye Anty Amarya, tun daga lokacin daya fara nemanta, har zuwa lokacin data kamashi da friends ɗinsa da irin gargaɗin da ya yi mata.
Anty Amarya taja wani dogon numfashi ta sauke tana jinjina lamarin.
“Lallai Uzair ya cika tantiri, shine kuma ya zagayo ya zo neman aurenki?”
“Ina tunanin yayi hakan ne dan Anty Namra ta rufa masa asiri, tun da mijinta ne ai ba zata tona masa asiri ba, kuma kin ga yanzu data faɗa sai ta zama ita ce mai laifi”
Cewar Maryam tana riƙe ƙoƙarin zama kusa da Namra.
“Amman miyasa baki faɗa min ba tun farko? Miyasa kika kirashi a waya kika masa cin mutunci? da wannan ne ya zagayo yazo ya ɗaure ki a gurin Abbanki, miyasa ba ku shawara idan zaku yi abu?”
Namra ta share hawayenta.
“Ban zaci abun zai zame min haka ba, nayi tunanin zai ji tsoro ya janye maganar auren ne”
“A ƙasashen yahudawa Uzair yayi karatu, ya fiki iya makirci, kuma mai son abun ka ya fi ka dabara”
Maryam ta kalli Anty Amarya
“Yanzu meye abun yi?”
“Abun yi kawai mu duƙufa da addu'ah, daga ke har ita, kuma In'shallahu wannan aure Allah ba zai bari a yi shi ba, tun da akwai zalumci a ciki”
Sun daɗe zaune a falo suna firar, sannan Namra ta tashi ta nufi ɗakinta zuciyarta cike da sassauci. Daf da zata shige Maryam ta kira ta
“Anty Namra”
Juyowa ta yi, ta amsa murya a daƙishe
“Na'am”
“Ki sawa zuciyarki sanyi, Mama na tare da ke, nima ina tare da ke, Allah ma yana tare dake, kuma zai kawo miki mafita”
Daga inda take tsaye ta ɗan murmusa
“Na gode Maryam”
Ko ba komai ƴar hirar da suka yi, da goyan bayan da suka nuna mata, yasa ta samu kanta da ɗan sakewa, tsaɓanin baya da take ganin kamar ita kaɗai ce a cikin matsalar.
Daman komai na duniya yana son tattaunawa, ta haka ne zaka fahimci wasu, wasu kuma su fahimce ka, matuƙar kace zaka kulle sirrinka a zuciyarka, shine mataki na farko wajen gurɓata tunaninka, da jawa kanka ciwo.
Sai dai duk da haka maganar da Mahaifiyar Asim ta yi mata ɗazu ta tsaya mata a rai, cewar Allah sai ya saka masa, yasa jikinta sanyi, da kuma zancen bata san inda ɗanta yake ba.
“Ina ka shiga Asim? Miyasa zaka yi haka? Zaka lalata karatun ka, ka guji iyayenka saboda ni Asim?”