Sashe 109
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita ce ta riga tashi ta nufi hanyar da zata sadata da ɗakunan tana kuka. Hilal kuma ya miƙe tsaye jikinsa a sanyaye ya bar falon, zuciyarsa na raya masa Dady yayi fushi ne shiyasa har ya yanke wannan shawarar.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *67*
Rasa ya yi inda zai sa kansa, gaba ɗaya ganin yake gabas da yamma sun haɗe masa, musamman ma daya dawo gida.
Sai tunani ya taru ya yi masa yawa, wanka daya saba yi kamin ya kwanta yau kam be yi ba, ko kayan jikinsa ma be damu ya canja ba haka ya hau gado ya kwanta, bachi ya ƙwauracewa idonsa gaba ɗaya, har safe be rumtsa ba, sai juyi yake kan gado.
Biyar da rabi na safe ya yi sallah asuba, bayan ya gama tasbihinsa ya ɗauko alƙu'ane ya buɗe ya fara karatu.
Ƴar ƙara wayarsa ta yi alamar saƙo ya shigo, sai dai be duba wayar ba, har sai ya gama karatun nasa yayi addu'ah sannan ya maida ƙur'ane mazauninsa ya aje. Kayan dake jikinsa ya cire ya ɗaura tawul ya shiga wanka, ya daɗe zaune a bathroom ɗin sai tunane yake kamin ya samu kuzarin watsa ruwa ya fito. Cikin rashin daɗin rai ya shirya, Farar shadda ya saka, be damu da duba kansa ba a madubi ba, ya saka agogon hannunsa tare da hulla, sannan ya ɗauki wayarsa yana duba ya nufi ƙofa,
Tunawa yayi da be saka turare ba hakan yasa shi ya dawo ya saka turaren sannan ya fice.
_Ka yi blocking ɗin number na, ka raba ni da ƴaƴana, Hilal ka ci amana ta, ina roƙon ka alfarma, dan Allah dan Manzon Allah ka bar ƴaƴa su dawo a gare ni su ne kawai gata na_
Yana karanta saƙon yasan daga inda ya fito duk da ba number ba ta bace. Wani godon tsaki yaja.
“Duk halin dana shiga ke ce sanadi Rashida”
Sai da ya yi deleted ɗin saƙon sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Ya ɗauki hanyar da zata kai shi gidan Hajiyarsa.
Be iso mutane sosai a gidan ba, kasancesar Safiya ne, kuma mutum na ƙaramin yaro ɓe ba babba ba, ita kanta a lokacin da ya shiga cikin gidan tana can cikin ɗakinta tana shiryawa.
Guri ya samu a falonta ya zauna, yana kallon tv duk da hankalinsa baya gurin, ɗai da ɗai ƙannensa da mutanen gidan suka riƙa shigowa suna gaishe shi da yi masa ya haƙuri, shi kuma yana amsa musu kamar an cilasta masa.
Sai takwas saura Hajiyaraa ta fito daga ɗakinta. Ta yi mamakin ganinsa a falon kamar wani baƙo mutumen da ya saba shiga har ɗakinta idan ya shigo cikin gidan.
Ƙarara Hajiya ta ga damuwa da rashin bachi a idon ɗanta, ba ta yi mamaki ba, daman can ta tsammaci haka, sai dai ita aabunda yake duba mas ba shi yake hangowa ba.
“Hajiya ina kwana”
Ya gaishe ta ba tare da ya ɗaga ido ya kalleta ba.
“Lafiya ƙalau ya haƙurin mu?”
“Alhamdullah”
“Ka yi haƙuri Hilal haka rayuwa take zuwa wani lokacin, kai taka ƙaddarar ta rashin mata na gari ne, ta ɗayan ba daɗi wannan ma ba halin ƙwarai, amman inshallah zaka ji daɗi, zan nema maka mata mai hankali da ladabi, mun yi magana da mahaifin ka ma, da ba dan wannan gaisuwar ba da kaje ka ganta, dan bana son auren ku ya wuce wata biyu ko uku ba, yarinyar ƴar gidan mutunci ce”
“Duk yadda kika ce Hajiya haka za'ayi amman ina roƙon alfarmar zan je aiki idan da dama a yi addu'ah yau, tun da yaro ne kuma daman can sunna bata koyar da mu wannan zaman kwana ukun da ake ba....”
“Eh Mahaifinka ma yayi wannan maganar amman naga tun da kwana uku ne, kuma kaga yanzu kwana ɗaya ya rage ai ƙara ka yi haƙuri kawai,amman kai zaka iya juwa aikin ai”
Kamin yayi magana sai ga Ezzah da Ulfah sun fito cikin shirin makaranta, da gudu suka zo suka rumgume shi.
“Dady i miss you”
Ulfah ta faɗa. Ita Ezzah sai tasa kuka.
“Dady shikenan Rafiq ba zai dawo ba?”
Kansu ya shafa cike da ƙaunar ƴaƴan nasa, da kewarsu kamar ba jiya ya rabu da su ba.
“Kin taɓa ganin wanda ya rasu ya dawo? Sai dai ki yi masa addu'ah”
“Ni kam i hate Anty Kalsoom ita ta kashe mana Rafiq”
Ya buge mata baki kaɗan.
“Kar na sake ji, akwai mai kashe wani bayan Allah ne? Kar bakinki ya sake irin wannan furucin”
“Dady wallahi ita ce ta kashe shi”
Ulfah ma ta faɗa, ta fuskanta kamar za ta yi kuka.
“Kuje driver na jiran ku zaku je school”
Hannu yasa aljihu ya ciro dari biyu ya mika musu, suka karɓa da far'ah suna godiya.
Da kallo Hajiya ta bi su har suka fice sannan ta ce
“Ni wallahi tausayi suke ba ni, shiyasa nake son ka auri yarinyar nan dan ga alama tana da natsuwa zata kula da su”
miƙewa ya yi tsaye yana dai-daita hular kansa.
“Zan leƙa office, idan na gama abunda na ke zan dawo”
“Amman ka karya kuwa?”
“A a zan karya a can”
“Allah ya tsare amman da ka tsaya ka karya a nan dan na san a can ba komai za ka ci ba”
“Zan ci”
Daga haka yasa kai ya fice, ransa a jagule.
NAMRA POV.
A ɗakin ta wuni har yamma, tun tana kuka mai hawayen har hawayen suka daina zuba, sai dai tayi kukan kawai babu hawaye.
Gaba ɗaya yanzu hankalinta ya tattara ya koma gida, tana kewar ƴan'uwanta sosai, duk da tadan itace bata kyauta musu ba, sai dai tana jin son mahaifiyarta a ranta tana kewarta.
“Bana jin ina daga cikin masu daɗewa a duniya, ina ji kamar mutuwa ta tana kusa da ni, ina da bukatar ki Mama, Abbah ka yafe min na tuba”
Magana take da kanta kamar wata taɓɓabiya. Miƙewa ta yi tsaye ciki da ƙargin hali dan bata jin karfi sosai a jikinta, fitowa ta yi waje, tana sun sun da kai kamar mai jin kunyar kallon inda su Neina suke.
“Ba wuta ai ƙara ki fito nan kam ki sha iska”
Neina ta faɗa tana gyara mata gurin da zata zauna. Ita kuma har ga Allah kunyar haɗa ido takw da Lamido balle kuma ta zauna inuwa ɗaya da shi.
“Zo ki zauna mana, jiri zai iya ɗaukar ki idan kina tsaye”
Ya faɗa ganin yadda ta tsaya a bakin kofar kamar ba zata zo ɗin ba, sosai gabansa yake faɗuwa, har murƴarsa na ƙoƙarin gargadar a maganar da yake mata saboda faɗuwan gabansa da ya tsananta.
Tana fara takawa gabansa ya fara fisgarsa yana wani zillo, da zaka tsaida idonka a lokacin da kyau a ƙirjinsa zaka ga yadda zuciyarsa take bugawa. Saurin ɗauke kansa ya yi daga kallo tafiyarta da yake kamin ta ƙaraso kusa da su.
Tana ƙaraso gurin sai kawai ta ɗauki filon da Neina ta aje mata, ta kalli Uwani ta ce.
“Dan Allah dan duba cikin jaka na akwai waya sai ki ɗauko min”
Ba musu Uwani ta tashi nufi ɗakin. Bata ɗauki tsawon lokaci ba ta fito da wayar a hannu ta miƙa wa Namra.
“Na gode”
Ta faɗa sai ta juya da zimmar komawa.
“Ai da kin zauna a nan”
“A.a daman wayar kawai nake son ɗauko wa”
“Zauna a ɗakin kawai, make yourself comfortable”
Kai kawai ya iya ɗaga masa, ta juya ta koma cikin ɗakin. Zaunawa ta yi tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta kafe wayar da ido kamar mai shakkun kunnawa.
Can dai ta kunna wayar zuciyarta cike da fargaba, da tunani kala-kala. Gabanta ya soma faɗuwa lokacin da saƙwanni suka riƙa shigo mata bayan ta kunna wayar. Sai dai mafi yawanci su duka na Mtn ne, sai saƙo ɗaya mai ɗauke da number Yasmeen. Saƙon ta fara buɗewa, tana tunanin wane irin saƙo ne Yasmin ta aiko nata.
_Salam Namra na haihu na samu baby girl, na kira wayarki ban samu ba_
Murmushi ta yi tare da hawaye a lokaci ɗaya.
“Allah ya raya miki babyn ki, ya baki lafiyar shayarwa”
Shine furucin da tayi a fili, ta rumgume wayar ta lumshe ido.
‘Ya kamata na koma gida, ko me me zai faru ya faru a can, na yi kuskure tun farko da ban sauka gidan mu’
Tunanin da take a ranta kenan, kamin ta buɗe ido, ta fara kallon ɗakin.
“Gobe... Gobe ya kamata na je gida, an cire duk wani fargaba da yake rai na, zan cire tsoro zan gwada ƙarɓar sunana ko Alƙah zai za na dace, ba zaka taɓa winning ko losing ba matuƙar baka taɓa gwadawa ba, i hate to try”
A fili ta yi furucin zuciyarta cike da yaƙinin lallai zata iya, kuma ta shirya fuskantar ko wane irin hukunci na Abbah.
“Taya zai yafe min idan ban je ba? Taya zan shirya da Anty idan ban je ba? I have to do this, Allah ka taimake ni”
Komawa ta yi ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala.
ABDOOL POV.
“Lafiya ƙalau aka ɗaura aure”
“Mashallah Allah ya nuna mana na ka, ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba”
“Ka yi kyau sosai, ka fito kamar wani babban sarki”
Kallon Mamaki Abdool yayi kamar ance masa Mai Martaba yana tsaye gabansa.
“Waya faɗa maka?”
“Babu ruwanka, ai har hoton ka an turo min alkyabar ta karɓe ka sosai”
Dariya yayi cike da mamaki, dan shi dai be san ya ɗora hoton daya saka alkyaba ba a media balle yace ko wani ne ya tura masa.
“Mai martaba kasan ance informer hukunsu ɗaya da da mai fashi da makami ko”
“To ayi haƙuri Major ayi haƙuri muma muna kan aikin mu ne”
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya daga shi har Mai Martaba, daga bisani Mai martaba ya ɗora da.
“Ƙarfe nawa zaka ta so?”
Shiru yayi kamar mai tunani, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin tafiyar.
“Zan turo maka dogarawan ka sai a bar min Sadauki, zamu kwana biyu kamin mu dawo”
“Why?”
“Just kawai ina son ganin kaduna ne, kasan rabo na sa kaduna since... I can't even remember”
Ya ɗan sosa kansa yana kallon titi da mutake ta kai kawo suna sha'aninsu.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *67*
Rasa ya yi inda zai sa kansa, gaba ɗaya ganin yake gabas da yamma sun haɗe masa, musamman ma daya dawo gida.
Sai tunani ya taru ya yi masa yawa, wanka daya saba yi kamin ya kwanta yau kam be yi ba, ko kayan jikinsa ma be damu ya canja ba haka ya hau gado ya kwanta, bachi ya ƙwauracewa idonsa gaba ɗaya, har safe be rumtsa ba, sai juyi yake kan gado.
Biyar da rabi na safe ya yi sallah asuba, bayan ya gama tasbihinsa ya ɗauko alƙu'ane ya buɗe ya fara karatu.
Ƴar ƙara wayarsa ta yi alamar saƙo ya shigo, sai dai be duba wayar ba, har sai ya gama karatun nasa yayi addu'ah sannan ya maida ƙur'ane mazauninsa ya aje. Kayan dake jikinsa ya cire ya ɗaura tawul ya shiga wanka, ya daɗe zaune a bathroom ɗin sai tunane yake kamin ya samu kuzarin watsa ruwa ya fito. Cikin rashin daɗin rai ya shirya, Farar shadda ya saka, be damu da duba kansa ba a madubi ba, ya saka agogon hannunsa tare da hulla, sannan ya ɗauki wayarsa yana duba ya nufi ƙofa,
Tunawa yayi da be saka turare ba hakan yasa shi ya dawo ya saka turaren sannan ya fice.
_Ka yi blocking ɗin number na, ka raba ni da ƴaƴana, Hilal ka ci amana ta, ina roƙon ka alfarma, dan Allah dan Manzon Allah ka bar ƴaƴa su dawo a gare ni su ne kawai gata na_
Yana karanta saƙon yasan daga inda ya fito duk da ba number ba ta bace. Wani godon tsaki yaja.
“Duk halin dana shiga ke ce sanadi Rashida”
Sai da ya yi deleted ɗin saƙon sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Ya ɗauki hanyar da zata kai shi gidan Hajiyarsa.
Be iso mutane sosai a gidan ba, kasancesar Safiya ne, kuma mutum na ƙaramin yaro ɓe ba babba ba, ita kanta a lokacin da ya shiga cikin gidan tana can cikin ɗakinta tana shiryawa.
Guri ya samu a falonta ya zauna, yana kallon tv duk da hankalinsa baya gurin, ɗai da ɗai ƙannensa da mutanen gidan suka riƙa shigowa suna gaishe shi da yi masa ya haƙuri, shi kuma yana amsa musu kamar an cilasta masa.
Sai takwas saura Hajiyaraa ta fito daga ɗakinta. Ta yi mamakin ganinsa a falon kamar wani baƙo mutumen da ya saba shiga har ɗakinta idan ya shigo cikin gidan.
Ƙarara Hajiya ta ga damuwa da rashin bachi a idon ɗanta, ba ta yi mamaki ba, daman can ta tsammaci haka, sai dai ita aabunda yake duba mas ba shi yake hangowa ba.
“Hajiya ina kwana”
Ya gaishe ta ba tare da ya ɗaga ido ya kalleta ba.
“Lafiya ƙalau ya haƙurin mu?”
“Alhamdullah”
“Ka yi haƙuri Hilal haka rayuwa take zuwa wani lokacin, kai taka ƙaddarar ta rashin mata na gari ne, ta ɗayan ba daɗi wannan ma ba halin ƙwarai, amman inshallah zaka ji daɗi, zan nema maka mata mai hankali da ladabi, mun yi magana da mahaifin ka ma, da ba dan wannan gaisuwar ba da kaje ka ganta, dan bana son auren ku ya wuce wata biyu ko uku ba, yarinyar ƴar gidan mutunci ce”
“Duk yadda kika ce Hajiya haka za'ayi amman ina roƙon alfarmar zan je aiki idan da dama a yi addu'ah yau, tun da yaro ne kuma daman can sunna bata koyar da mu wannan zaman kwana ukun da ake ba....”
“Eh Mahaifinka ma yayi wannan maganar amman naga tun da kwana uku ne, kuma kaga yanzu kwana ɗaya ya rage ai ƙara ka yi haƙuri kawai,amman kai zaka iya juwa aikin ai”
Kamin yayi magana sai ga Ezzah da Ulfah sun fito cikin shirin makaranta, da gudu suka zo suka rumgume shi.
“Dady i miss you”
Ulfah ta faɗa. Ita Ezzah sai tasa kuka.
“Dady shikenan Rafiq ba zai dawo ba?”
Kansu ya shafa cike da ƙaunar ƴaƴan nasa, da kewarsu kamar ba jiya ya rabu da su ba.
“Kin taɓa ganin wanda ya rasu ya dawo? Sai dai ki yi masa addu'ah”
“Ni kam i hate Anty Kalsoom ita ta kashe mana Rafiq”
Ya buge mata baki kaɗan.
“Kar na sake ji, akwai mai kashe wani bayan Allah ne? Kar bakinki ya sake irin wannan furucin”
“Dady wallahi ita ce ta kashe shi”
Ulfah ma ta faɗa, ta fuskanta kamar za ta yi kuka.
“Kuje driver na jiran ku zaku je school”
Hannu yasa aljihu ya ciro dari biyu ya mika musu, suka karɓa da far'ah suna godiya.
Da kallo Hajiya ta bi su har suka fice sannan ta ce
“Ni wallahi tausayi suke ba ni, shiyasa nake son ka auri yarinyar nan dan ga alama tana da natsuwa zata kula da su”
miƙewa ya yi tsaye yana dai-daita hular kansa.
“Zan leƙa office, idan na gama abunda na ke zan dawo”
“Amman ka karya kuwa?”
“A a zan karya a can”
“Allah ya tsare amman da ka tsaya ka karya a nan dan na san a can ba komai za ka ci ba”
“Zan ci”
Daga haka yasa kai ya fice, ransa a jagule.
NAMRA POV.
A ɗakin ta wuni har yamma, tun tana kuka mai hawayen har hawayen suka daina zuba, sai dai tayi kukan kawai babu hawaye.
Gaba ɗaya yanzu hankalinta ya tattara ya koma gida, tana kewar ƴan'uwanta sosai, duk da tadan itace bata kyauta musu ba, sai dai tana jin son mahaifiyarta a ranta tana kewarta.
“Bana jin ina daga cikin masu daɗewa a duniya, ina ji kamar mutuwa ta tana kusa da ni, ina da bukatar ki Mama, Abbah ka yafe min na tuba”
Magana take da kanta kamar wata taɓɓabiya. Miƙewa ta yi tsaye ciki da ƙargin hali dan bata jin karfi sosai a jikinta, fitowa ta yi waje, tana sun sun da kai kamar mai jin kunyar kallon inda su Neina suke.
“Ba wuta ai ƙara ki fito nan kam ki sha iska”
Neina ta faɗa tana gyara mata gurin da zata zauna. Ita kuma har ga Allah kunyar haɗa ido takw da Lamido balle kuma ta zauna inuwa ɗaya da shi.
“Zo ki zauna mana, jiri zai iya ɗaukar ki idan kina tsaye”
Ya faɗa ganin yadda ta tsaya a bakin kofar kamar ba zata zo ɗin ba, sosai gabansa yake faɗuwa, har murƴarsa na ƙoƙarin gargadar a maganar da yake mata saboda faɗuwan gabansa da ya tsananta.
Tana fara takawa gabansa ya fara fisgarsa yana wani zillo, da zaka tsaida idonka a lokacin da kyau a ƙirjinsa zaka ga yadda zuciyarsa take bugawa. Saurin ɗauke kansa ya yi daga kallo tafiyarta da yake kamin ta ƙaraso kusa da su.
Tana ƙaraso gurin sai kawai ta ɗauki filon da Neina ta aje mata, ta kalli Uwani ta ce.
“Dan Allah dan duba cikin jaka na akwai waya sai ki ɗauko min”
Ba musu Uwani ta tashi nufi ɗakin. Bata ɗauki tsawon lokaci ba ta fito da wayar a hannu ta miƙa wa Namra.
“Na gode”
Ta faɗa sai ta juya da zimmar komawa.
“Ai da kin zauna a nan”
“A.a daman wayar kawai nake son ɗauko wa”
“Zauna a ɗakin kawai, make yourself comfortable”
Kai kawai ya iya ɗaga masa, ta juya ta koma cikin ɗakin. Zaunawa ta yi tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta kafe wayar da ido kamar mai shakkun kunnawa.
Can dai ta kunna wayar zuciyarta cike da fargaba, da tunani kala-kala. Gabanta ya soma faɗuwa lokacin da saƙwanni suka riƙa shigo mata bayan ta kunna wayar. Sai dai mafi yawanci su duka na Mtn ne, sai saƙo ɗaya mai ɗauke da number Yasmeen. Saƙon ta fara buɗewa, tana tunanin wane irin saƙo ne Yasmin ta aiko nata.
_Salam Namra na haihu na samu baby girl, na kira wayarki ban samu ba_
Murmushi ta yi tare da hawaye a lokaci ɗaya.
“Allah ya raya miki babyn ki, ya baki lafiyar shayarwa”
Shine furucin da tayi a fili, ta rumgume wayar ta lumshe ido.
‘Ya kamata na koma gida, ko me me zai faru ya faru a can, na yi kuskure tun farko da ban sauka gidan mu’
Tunanin da take a ranta kenan, kamin ta buɗe ido, ta fara kallon ɗakin.
“Gobe... Gobe ya kamata na je gida, an cire duk wani fargaba da yake rai na, zan cire tsoro zan gwada ƙarɓar sunana ko Alƙah zai za na dace, ba zaka taɓa winning ko losing ba matuƙar baka taɓa gwadawa ba, i hate to try”
A fili ta yi furucin zuciyarta cike da yaƙinin lallai zata iya, kuma ta shirya fuskantar ko wane irin hukunci na Abbah.
“Taya zai yafe min idan ban je ba? Taya zan shirya da Anty idan ban je ba? I have to do this, Allah ka taimake ni”
Komawa ta yi ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala.
ABDOOL POV.
“Lafiya ƙalau aka ɗaura aure”
“Mashallah Allah ya nuna mana na ka, ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba”
“Ka yi kyau sosai, ka fito kamar wani babban sarki”
Kallon Mamaki Abdool yayi kamar ance masa Mai Martaba yana tsaye gabansa.
“Waya faɗa maka?”
“Babu ruwanka, ai har hoton ka an turo min alkyabar ta karɓe ka sosai”
Dariya yayi cike da mamaki, dan shi dai be san ya ɗora hoton daya saka alkyaba ba a media balle yace ko wani ne ya tura masa.
“Mai martaba kasan ance informer hukunsu ɗaya da da mai fashi da makami ko”
“To ayi haƙuri Major ayi haƙuri muma muna kan aikin mu ne”
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya daga shi har Mai Martaba, daga bisani Mai martaba ya ɗora da.
“Ƙarfe nawa zaka ta so?”
Shiru yayi kamar mai tunani, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin tafiyar.
“Zan turo maka dogarawan ka sai a bar min Sadauki, zamu kwana biyu kamin mu dawo”
“Why?”
“Just kawai ina son ganin kaduna ne, kasan rabo na sa kaduna since... I can't even remember”
Ya ɗan sosa kansa yana kallon titi da mutake ta kai kawo suna sha'aninsu.