Sashe 134
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Allah ya taimaki Mai Martaba ya ƙara maka lafiya”
Zaunawa yyi da murmushi a fuskarsa.
“Yarima Abdallah, kuma sarkin mu na gobe”
Yayi dariya.
“A dai bar ni a Yariman, har yanzu bana mafarkin zama Sarki”
“Aiko ƙara ja shirya, damin very soon zaka zama Sarki, kasan har yanzu ban faɗa maka albishir ɗin ka ba ko?”
“Shiyasa ma ka ga na zo yanzu”
Mai Martab ya ɗora ƙafa saman ɗaya yana kallon Abdool cike da natsuwa.
“Wato Albishir ɗin ka guda biyu ne, kuma dukaninsu suna da muhimmanci, kuma ina fatar zaka karɓa ka yi na'am da dukansu. Na farƙo dai ina maka albishir da cewar Hajiya Shafa ta baka Zalihatu kyauta, abu na biyu kuma mun yanke shawarar naɗa ka sabon Sarkin Katsina...”
Wani irin kallo yayi ma Mai Martaba kamar Ummi bata faɗa masa komai ba, sai ya sauka ƙasa yana nuna kansa.
“Mai Martaba ni?”
“Kai fa”
Ya faɗa da murmushi a fuskarsa.
“Ka fi kowa karantar waye ni Mai Martaba, ka fi kowa sanin abunda ya dace da ni, ba zaka taɓa zaɓa min sheri ba, kuma na san kafi kowa son farinciki da walwala. Sai dai akwai abun dubawa a maganganun ka Mai Martaba, kamin ni kana da ƴaƴa biyu, waɗanda ko baka raye su suka fi cancanta a ɗora a sarautar nan, bayan kuma Sarkin gari, da Baba Macido ƙanenka ne da ke tunanin idan a yau baka raye, za a iya basu sarautar Katsina, babu wanda zai jidaɗi a cikinsu, idan a ɗauki Sarautar nan aka bani ko da baka raye ballantana kana da ranka kuma kai da hannunka zaka ɗauki Sarautar nan ka ba ni, a iya sanin da na yi ma Sarautar nan, zaɓe ake idan za'ayi sabon sarki, nasan mutane da yawa za su ce ka shigo da sabon tsari ka nuna son kai. Na sani idan cancanta ake dubawa, na cancanta, amman ana barin Halak dan kunya, ni Wallahi ina son aikina kuma ina ƙaunar na mutu ina yinsa”
Mai Martaba yaja wani dogon numfashi ya sauke yana gyara zama. Tabbas Abdool yayi magana mai kyau da kama hankali, hakan kuma ba ƙaramin ƙara burge Mai Martaba ya yi ba, a ƙara karantar irin basira da fikrah da ɗansa yake da ita.
“Haƙiƙa kafi kowa dacewa da Sarautar Katsina, ana son Sarki mai fikra da Nagarta, kuma an fi son Sarki da baya son Sarautar kwata-kwata a ransa. Sai dai hakan be isa yasa na cilasta maka ba, wata ƙila gaba zaka iya neman Sarautar da kan ka”
Hannayensa biyu yasa ya riƙe ƙafar Mai Martaba ɗaya da ke ƙasa.
“Na gode sosai da ka fahimce kuma ka min Uzuri, Allah ya ƙara mana lafiya da nisan kwana. Abu na biyu kuma Mai Martaba na samu matar da na ke so...”
“Namra?”
Yayi ƙasa da kansa yana jin kunya.
“Zamu aura maka duk mace da kake so Babana, ba zamu maka cilas ba, abun da kawai yake da muhimmanci kana son ta”
“Ina fatar hakan ba zai ɓata maka rai ba, kuma ina son na ji ra'ayinka akan auren bazarawa”
“Baka san Annabi S.A.W ya auri Bazawara ba, Nana Khadija ta haifi ƴaƴa ma a wani gidan sannan ta auri Annabi yana yaronsa, balle wannan da ɓata ma haihu ba, indai yarinyar ƴar kirkici mun yarda ka aureta ɗari-ɗari”
Miƙewa yayi tsaye yayi wani tsalle ya dire kamar ƙaramin yaro
“I knew it, daman na faɗawa Ummi tace wai ba zaka yarda ba, har musu take min wai she know you better than i”
Mai martaba yayi murmushi.
“No my son know me better than her”
Rumgume Mai Martaba Abdool yai cike da jin daɗi yana jin kamar ya haɗe shi.
NAMRA POV.
Daga gurin passport tace direba ya wuce da ita gidan su Lamido. Idonta tab da hawaye ta shiga cikin gidan, muryarta kamar wacce zata fasa kuka ta yi sallama. Lamido ne mutumen da ta fara ido huɗu da shi a gidan, kuma ya ƙi ya amsa mata sallamarta balle kauda idonsa daga kallon tarayyar da idanuwansu suka yi.
“Kin zo ban kwanar ne? Ai dama baki dawo ba saboda zaki ƙara saka zuciyana cikin ƙuna ne kawai”
“Don't you happy na shirya da iyayena”
“I won't lie Namra, yes i'm not happy because you are going to leave,kuma ba nine silar wannan farinciki na ki ba bayan wannan shi ne mafarki na a kullum, ina kishin mutumen da ya shirya ki da iyayenki sosai, kamar mutumen da cire min duka tufafi ya bar ni tsirara, kin san ya tozarta ni ko? Ko ba komai idan kika tuna shi zaki yi murmushi ni fa?”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Namra bata zo gidanku dan ka so ta ba, saboda Namra ta gama so a rayuwarta, na yi rilaya, ɗakin so kuma sai dai wata mai sunana ta shiga amman ba ni ba, ka daina yaudarar kan ka dan Allah”
“Daman na tsammaci haka, saboda ni ba Yarima ba ne, kuma ba wan....”
Hannu ta ɗaga mishi ta tsaka mishi tsawar da tasa su Neina fito daga cikin ɗaki da gudu.
“Shi haka yayi ya yaudare ni, wani namiji ba zai ƙara burgeni ba, put this in your mind i will never ever ever ever love someone again”
Murmushi yayi yasa kai ya fice. Neina ta nufo tana tambayar abunda ya faru.
“Babu komai kawai na zo na yi muku bankwana ne anjima kaɗan zamu wuce”
“Ƙaraso ki zauna mana”
“Ba sai na ƙaraso ba, direba yana jirana a waje”
Sai kawai ta rumgume Neina ta fashe da kuka.
“Zan dawo Neina, rabuwa ba mutuwa ba ce kun min halaccin da ba zan iya mantawa ba”
Nan Neina da Uwani suka saka kuka, dan Maryam bata nan a lokacin. Kamar ba zasu rabu ba haka suka riƙa riƙe juna suna kuka kamar an yi mutuwa, har maƙota suka leƙo suna kallon ikon Allah.
Namra na komawa aka aiko musu da abincin rana, lokaci na yi direba ya zo ɗaukarsu zuwa airport, kamar su ake jira suna isa jirgi ya kama hanyar sokoto. Suna sauka Abbah yayi ma direbansa waya ya zo ya ɗauke su, kuka sosai Namra ta riƙa yi cikin motar ta daman tun a jirgi ta fara abunta, sam bata ji daɗin kalaman da ta faɗawa Lamido ba, sai dai bata da wani zaɓi sai wannan, ga kuma kukan rabuwa da Neina, da kuma kuka dawowa sokoto birnin shehu birni mai albakar da karamci tare da iyayenta komai ya zame mata kamar sabo, bama kamar ta motarsa ta nutsa kai cikin gidan duk an fence shi an sabunta komai saboda bikin Maryam da za'ayi.
Suna jin mota duk suka fito waje har Hajiya Barau da Zinatu da zo jiya suna jiran Abbah da Anty su fito. Abbah ne ya fara fita daga cikin motar sannan Namra ta fito fuskarta da hawaye. Wani irin ihu Maryam ta saka taje a guje ta rumgume Namra suka fashe da kuka, sannan Hindatu da Aisha suka je suka rumgume ta, suma suka saka kuka, Hajiya Barau ce Mamaki ya hanata komai har Abbah da wuce da Anty Amarya sannan ta nufi Namra kunya kunya.
“Wai Namra ce nake gani nan ni mamaki ma ya hanani komai”
“Itace Hajiya, Abbah yaje ya taho da abar sa”
Cewar Maryam tana sharewa Namra hawaye. Sannan suka riƙa hannunta suka nufi cikin gida da ita.
YASMIN POV.
Lokacin da ta bar gidan mijita sai ta nufo gida, sai dai bata yarda ta nunawa mahaifiyarta damuwarta ba, gudun kar ta hana ta aikata abunda take da niyar yi, wuni ta yi a gidan suka sha fira kamar ba komai sai dare ta fito suka koma gida ita da yaranta da kuma mai aikinta. Bata tarar da Uzair cikin gidan ba hakan yasa ta ɗan ji sanyi dan bata ƙaunar ganinsa a yanzu. Abunda kawai take da buƙata ya za'ayi ta haɗu da Namta akwai buƙatar ta tattauna da ita kamin ta fallasa Uzair, ma'ana ta jawa Namra haƙƙinta ko zata samu sanyin zuciya akan abunda ya aikatawa ɗan sa. Haka ta kwana tana tunanin mafita washe gari ma kasa zuwa aiki ta yi duk da tana da cases a kotu, da an kira ta sai tace bata da lafiya ne. Uzair kuma be kwana a gidan ba, da alama akwai gun da ya kwana, sai dai hakan be dame ta ba ko kaɗan tun da tasan wanene shi a yanzu. Bayan ta gama waya da wani Barrister, sai ga kiran Mahaifiyarta ya shigo wayarta.
Bayan sun gaisa take labarta mata ance Namra ta dawo, kuma wai Abbah ne yaje ya taho ta ita, Yasmin ta nuna murnarta sosai daman abun nema ya samu. Dan haka tana kashe wayar ta aje little Namra ta shiga wanka, tana fitowa ta yi ma mata sannan suka shirya daman Adnan yana makaranta. Ƴar aikinta kawai ta bari a gidan ta nufi gidansu Namra.
Tana fita Uzair na shigowa, ciki wani irin yanayi ya buga ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.
“Sannu da zuwa”
Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.
TEEMA POV.
Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.
Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.
Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.
Zaunawa yyi da murmushi a fuskarsa.
“Yarima Abdallah, kuma sarkin mu na gobe”
Yayi dariya.
“A dai bar ni a Yariman, har yanzu bana mafarkin zama Sarki”
“Aiko ƙara ja shirya, damin very soon zaka zama Sarki, kasan har yanzu ban faɗa maka albishir ɗin ka ba ko?”
“Shiyasa ma ka ga na zo yanzu”
Mai Martab ya ɗora ƙafa saman ɗaya yana kallon Abdool cike da natsuwa.
“Wato Albishir ɗin ka guda biyu ne, kuma dukaninsu suna da muhimmanci, kuma ina fatar zaka karɓa ka yi na'am da dukansu. Na farƙo dai ina maka albishir da cewar Hajiya Shafa ta baka Zalihatu kyauta, abu na biyu kuma mun yanke shawarar naɗa ka sabon Sarkin Katsina...”
Wani irin kallo yayi ma Mai Martaba kamar Ummi bata faɗa masa komai ba, sai ya sauka ƙasa yana nuna kansa.
“Mai Martaba ni?”
“Kai fa”
Ya faɗa da murmushi a fuskarsa.
“Ka fi kowa karantar waye ni Mai Martaba, ka fi kowa sanin abunda ya dace da ni, ba zaka taɓa zaɓa min sheri ba, kuma na san kafi kowa son farinciki da walwala. Sai dai akwai abun dubawa a maganganun ka Mai Martaba, kamin ni kana da ƴaƴa biyu, waɗanda ko baka raye su suka fi cancanta a ɗora a sarautar nan, bayan kuma Sarkin gari, da Baba Macido ƙanenka ne da ke tunanin idan a yau baka raye, za a iya basu sarautar Katsina, babu wanda zai jidaɗi a cikinsu, idan a ɗauki Sarautar nan aka bani ko da baka raye ballantana kana da ranka kuma kai da hannunka zaka ɗauki Sarautar nan ka ba ni, a iya sanin da na yi ma Sarautar nan, zaɓe ake idan za'ayi sabon sarki, nasan mutane da yawa za su ce ka shigo da sabon tsari ka nuna son kai. Na sani idan cancanta ake dubawa, na cancanta, amman ana barin Halak dan kunya, ni Wallahi ina son aikina kuma ina ƙaunar na mutu ina yinsa”
Mai Martaba yaja wani dogon numfashi ya sauke yana gyara zama. Tabbas Abdool yayi magana mai kyau da kama hankali, hakan kuma ba ƙaramin ƙara burge Mai Martaba ya yi ba, a ƙara karantar irin basira da fikrah da ɗansa yake da ita.
“Haƙiƙa kafi kowa dacewa da Sarautar Katsina, ana son Sarki mai fikra da Nagarta, kuma an fi son Sarki da baya son Sarautar kwata-kwata a ransa. Sai dai hakan be isa yasa na cilasta maka ba, wata ƙila gaba zaka iya neman Sarautar da kan ka”
Hannayensa biyu yasa ya riƙe ƙafar Mai Martaba ɗaya da ke ƙasa.
“Na gode sosai da ka fahimce kuma ka min Uzuri, Allah ya ƙara mana lafiya da nisan kwana. Abu na biyu kuma Mai Martaba na samu matar da na ke so...”
“Namra?”
Yayi ƙasa da kansa yana jin kunya.
“Zamu aura maka duk mace da kake so Babana, ba zamu maka cilas ba, abun da kawai yake da muhimmanci kana son ta”
“Ina fatar hakan ba zai ɓata maka rai ba, kuma ina son na ji ra'ayinka akan auren bazarawa”
“Baka san Annabi S.A.W ya auri Bazawara ba, Nana Khadija ta haifi ƴaƴa ma a wani gidan sannan ta auri Annabi yana yaronsa, balle wannan da ɓata ma haihu ba, indai yarinyar ƴar kirkici mun yarda ka aureta ɗari-ɗari”
Miƙewa yayi tsaye yayi wani tsalle ya dire kamar ƙaramin yaro
“I knew it, daman na faɗawa Ummi tace wai ba zaka yarda ba, har musu take min wai she know you better than i”
Mai martaba yayi murmushi.
“No my son know me better than her”
Rumgume Mai Martaba Abdool yai cike da jin daɗi yana jin kamar ya haɗe shi.
NAMRA POV.
Daga gurin passport tace direba ya wuce da ita gidan su Lamido. Idonta tab da hawaye ta shiga cikin gidan, muryarta kamar wacce zata fasa kuka ta yi sallama. Lamido ne mutumen da ta fara ido huɗu da shi a gidan, kuma ya ƙi ya amsa mata sallamarta balle kauda idonsa daga kallon tarayyar da idanuwansu suka yi.
“Kin zo ban kwanar ne? Ai dama baki dawo ba saboda zaki ƙara saka zuciyana cikin ƙuna ne kawai”
“Don't you happy na shirya da iyayena”
“I won't lie Namra, yes i'm not happy because you are going to leave,kuma ba nine silar wannan farinciki na ki ba bayan wannan shi ne mafarki na a kullum, ina kishin mutumen da ya shirya ki da iyayenki sosai, kamar mutumen da cire min duka tufafi ya bar ni tsirara, kin san ya tozarta ni ko? Ko ba komai idan kika tuna shi zaki yi murmushi ni fa?”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Namra bata zo gidanku dan ka so ta ba, saboda Namra ta gama so a rayuwarta, na yi rilaya, ɗakin so kuma sai dai wata mai sunana ta shiga amman ba ni ba, ka daina yaudarar kan ka dan Allah”
“Daman na tsammaci haka, saboda ni ba Yarima ba ne, kuma ba wan....”
Hannu ta ɗaga mishi ta tsaka mishi tsawar da tasa su Neina fito daga cikin ɗaki da gudu.
“Shi haka yayi ya yaudare ni, wani namiji ba zai ƙara burgeni ba, put this in your mind i will never ever ever ever love someone again”
Murmushi yayi yasa kai ya fice. Neina ta nufo tana tambayar abunda ya faru.
“Babu komai kawai na zo na yi muku bankwana ne anjima kaɗan zamu wuce”
“Ƙaraso ki zauna mana”
“Ba sai na ƙaraso ba, direba yana jirana a waje”
Sai kawai ta rumgume Neina ta fashe da kuka.
“Zan dawo Neina, rabuwa ba mutuwa ba ce kun min halaccin da ba zan iya mantawa ba”
Nan Neina da Uwani suka saka kuka, dan Maryam bata nan a lokacin. Kamar ba zasu rabu ba haka suka riƙa riƙe juna suna kuka kamar an yi mutuwa, har maƙota suka leƙo suna kallon ikon Allah.
Namra na komawa aka aiko musu da abincin rana, lokaci na yi direba ya zo ɗaukarsu zuwa airport, kamar su ake jira suna isa jirgi ya kama hanyar sokoto. Suna sauka Abbah yayi ma direbansa waya ya zo ya ɗauke su, kuka sosai Namra ta riƙa yi cikin motar ta daman tun a jirgi ta fara abunta, sam bata ji daɗin kalaman da ta faɗawa Lamido ba, sai dai bata da wani zaɓi sai wannan, ga kuma kukan rabuwa da Neina, da kuma kuka dawowa sokoto birnin shehu birni mai albakar da karamci tare da iyayenta komai ya zame mata kamar sabo, bama kamar ta motarsa ta nutsa kai cikin gidan duk an fence shi an sabunta komai saboda bikin Maryam da za'ayi.
Suna jin mota duk suka fito waje har Hajiya Barau da Zinatu da zo jiya suna jiran Abbah da Anty su fito. Abbah ne ya fara fita daga cikin motar sannan Namra ta fito fuskarta da hawaye. Wani irin ihu Maryam ta saka taje a guje ta rumgume Namra suka fashe da kuka, sannan Hindatu da Aisha suka je suka rumgume ta, suma suka saka kuka, Hajiya Barau ce Mamaki ya hanata komai har Abbah da wuce da Anty Amarya sannan ta nufi Namra kunya kunya.
“Wai Namra ce nake gani nan ni mamaki ma ya hanani komai”
“Itace Hajiya, Abbah yaje ya taho da abar sa”
Cewar Maryam tana sharewa Namra hawaye. Sannan suka riƙa hannunta suka nufi cikin gida da ita.
YASMIN POV.
Lokacin da ta bar gidan mijita sai ta nufo gida, sai dai bata yarda ta nunawa mahaifiyarta damuwarta ba, gudun kar ta hana ta aikata abunda take da niyar yi, wuni ta yi a gidan suka sha fira kamar ba komai sai dare ta fito suka koma gida ita da yaranta da kuma mai aikinta. Bata tarar da Uzair cikin gidan ba hakan yasa ta ɗan ji sanyi dan bata ƙaunar ganinsa a yanzu. Abunda kawai take da buƙata ya za'ayi ta haɗu da Namta akwai buƙatar ta tattauna da ita kamin ta fallasa Uzair, ma'ana ta jawa Namra haƙƙinta ko zata samu sanyin zuciya akan abunda ya aikatawa ɗan sa. Haka ta kwana tana tunanin mafita washe gari ma kasa zuwa aiki ta yi duk da tana da cases a kotu, da an kira ta sai tace bata da lafiya ne. Uzair kuma be kwana a gidan ba, da alama akwai gun da ya kwana, sai dai hakan be dame ta ba ko kaɗan tun da tasan wanene shi a yanzu. Bayan ta gama waya da wani Barrister, sai ga kiran Mahaifiyarta ya shigo wayarta.
Bayan sun gaisa take labarta mata ance Namra ta dawo, kuma wai Abbah ne yaje ya taho ta ita, Yasmin ta nuna murnarta sosai daman abun nema ya samu. Dan haka tana kashe wayar ta aje little Namra ta shiga wanka, tana fitowa ta yi ma mata sannan suka shirya daman Adnan yana makaranta. Ƴar aikinta kawai ta bari a gidan ta nufi gidansu Namra.
Tana fita Uzair na shigowa, ciki wani irin yanayi ya buga ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.
“Sannu da zuwa”
Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.
TEEMA POV.
Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.
Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.
Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.