Sashe 150
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Kayi dacen mata, itama kuma ta yi dacen miji, congratulations Namra Allah ya baki abubuwa da dama, ciki har da wanda na fi so sama da komai, Allah ya haɗa kan ku ya baku zama lafiya”
Uffan Namra bata ce mata ba, har tayi surutunta ta gama ta koma gurin Abdool.
“Haƙiƙa kun dace da junanku, namiji irinka be dace da ko wace irin mace ba sai Namra kamar yadda ita ma bata dace da ko wane miJi ba sai kai, na yarda da ƙaddara haka Allah ya so ta kasance a gareni...”
“Amir...”
Ta ɗaga mishi hannu.
“Na fahimta, na gane ƙaddaratace a haka”
Bata jira abunda zai faɗa ba ta juya ta koma cikin gidansu, hawaye na mata zuba kamar ruwa. Buɗe motar Abdool yayi ya koma ciki ya zauna yana kallon fuskar Namra.
“Itace yarinyar da ta cutar da ke ko?”
“Abunda ta yi min tsakanina da ita ne, kai kuma sadaukarwar da ta maka tsakanin ka da ita ne, ka maida ni gidanmu ban yi tunanin ka ɗauko ni dan ka ɓata min rai ba, na tsani yarinyar nan na tsane ta, idan ma kana son ta ni ina ruwana karka sake kawo ni gurin, idan ma zaka so ka kaje can ka so ta ni karka sake sako ni a matsalar ku”
Shiru yayi yana saurarenta har ta yi masa faɗan ta gama sannan ya tashi motar yana murmushi ya suka nufi hanyar gida. Sarai kalamata suka wanke masa zuciya ɗan ya fahimci inda ta dosa. Yana yin fakin ya buɗe motar ta fita a hasale ta shiga cikin gida.
Wayarsa ya ɗauka ya kira Abbah suka yi magana sannan ya faka motarsa ya fita ya shiga part ɗinsa.
Yayi awa ɗaya a part ɗin Abbah sannan ya fito tare da Abbah ya shiga motarsa ya kama hanya.
KALSOOM POV.
FIVE MONTHS LATER...
Daga ita har su Izza basa da wata matsala a yanzu, tana zaune da yaran lafiya ƙalau ga Hajiya sai nuna musu kulawa take. duk wani rashin kunya na Izza ta watsar, ulfah kan ba a magana daman tun da warke daga jinyar ruwana zafi sai ta ƙara ladabi, dan sosai yanzu suka gane muhimmanci Kalsoom, gashi lokaci-zuwa lokaci takan kira musu mahaifiyarsu su gaisa, ranar weekend kuma Hilal ya kaisu gidan Hajiya. Idan zai dawo Hajiya ta bashi rubutu ya kawo mata na neman ta sauka lafiya. Babu yadda Teema ba tayi ba akan ta dawo gidan amman Hilal da Hajiya suka ƙi, su Izzah kan ko zancenta basa so.
***
Bayan ta ƙare waya da Salma ne ta kalli Hilal dake kwance gefenta yana wasa da wayarsa tace.
“Salma na gaishe ka”
“Ina amsawa, bari naje na ɗauko su izza scul”
Ya faɗa yana unƙurin tashi, kai kawai ta ɗaga masa dan maganar ma wahala take mata ko wayar da take da Salma na ƙarfin hali ne, tun jiya take jin abu amman ta kasa faɗa, duk da ta kan ji irin haka lokaci lokaci amman wannan ya tsananta mata da yawa. Aiko kamar karya tashi daga gurim ta soma jin ana tsikararta, har zaman ya gagareta sai da ta kwanta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Shi take ta maimaitawa tana rumtse rumtsen ido. waƴarta na kusa da ita amman ta kasa miƙa hannu ta ɗauka, wani irin juyi take jin duniya na mata, tun tana faɗar Innalillahi a hankali har ta fara yi da ƙarfi tana ta rumtsar ido da buɗewa kamar wacce ta ci bashi. Ko da Hilal ya ɗauko su Ulfah daga makaranta Kalsoom ta jigata, jini har ya fara mata zuba, daman tun safe ya kula da yadda cikin yayi mata ƙasa sosai. Ɗakinsa ya shiga ya ɗauko kayan karɓar haihuwa ya dawo ɗakinta ya shiga ya rufe ƙofar ya shiga bata taimako, because ya san it too late yace zai ɗauke ta suke asibiti a yanzu bayan ga har kan yaro ya fara fitowa😷
ASIM POV.
Tun bayan rasuwar Mama ya daina ganin kam kowa da gashi, gani yake tun da yayi losing mahaifiyarsa a yanzu baya gudun komai, haka zai shigo cikin sokoto ya kwana gurin ogansa, ba zai leƙa ƙanensa ba sai zai tafi sannan ya basu kuɗi mai yawa, babban gida ya siya musu, dan yana ganin kamar su ne family da suka rage masa yanzu. Sai duk lokacin da ya shiga sokoto sai ya binka labarin Namra ace masa tana nan lafiya, har wani ya ɗauka mai aikin bincika masa labarinta, dan a tunaninsa tana nan ɗauke da cikinsa, burinsa kawai ta haifa masa ɗan ko ya ya ɗauke ta dan kawai ya ɗasa mata baƙin ciki. Sati ɗaya da rasuwar Mama aka saka ranar aurensa da Mardiya, yadda yake kashe mata kuɗi sai ka rantse da Allah shi ne yake buga kuɗi, dan yana samun kuɗi sosai a yanzu manyan mutane yake tare da su. Ya faɗa musu baya buƙatar komai dan tun kamin a kai lefe ya saka komai a gidan da zata zauna, kama daga kayan kitchen har zuwa na kwalliya da sutura kai kace ma be mata lefen gaba ɗaya ba sai taje can, har kayan abinci babu abunda be zuba ba, freezer goma ya saka a gidan jo wace cike take da kayan daɗi.
Ranar talata aka fara event an zubar da naira a kamu sosai kasancewar Asim ya bawa kawaye amarya kuɗi sosai, gashi shi ma yaje shi da abokaninsa dan yanzu yayi sabin abokai yayan manya sai kuma masu irin aikinsa, duk wani gaye mai kuɗi da kasani a cikin garin katsina mai ji da kansa sai Asim yayi abota da shi, dan gani yake sune sa'o'insa.
Friday aka yi walima, a instagram Namra take ganin bikin kamun su, tayi mamakin da ya auri Mardiya dan bata manta lokacin da yake yawan maimaita mata cewar shi sai ƴar da ubanta ya fi nata kuɗi zai aure, wata ƙila farin jikinta ne ya jashi hankalinsa ko kuma bayan ya aureta zai ƙara wata.
Tun ranar da aka gyara ɗakin aka saka komai Asim yake kwana a gidan. Wasu abokansa da suka zo daga sokoto da Abuja sai ya kama musu hotel wasu kuma ya sauke su a ɗayan gidansa dake GRA, shi kuma ya koma Light up road inda gidan amaryarsa yake dan kwana. Light up unguwace ta masu kuɗi ko wanne gida ka gani sai ya burge ka, amman duk da haka a layin da Asim yake gidansa ya fi ko wanne gida kyau da tsari, kana ganinsa kasan ba ƙananan kuɗi aka kashe ba gurin gina shi.
Ƙarfe ɗaya da rabi na dare ya shigo gidan, cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, yana jinsa a wani matsayi na daban kwatankwacin matsayin da ya riƙa jin kamsa a lokacin da zai auri Namra, freezer da ke kitchen ya nufa ya buɗe ya ɗauko power horse ya fito falo yana sha. Kansa ya ɗaga sama yana kallon pop zuwa labulayen da aka saka falon, hantin kawai idan ka kalla sai ya burge ka, balle kuma kujera da plasma da flowers, daga kujera har center carpet da labulayen da da fantin ɗakin milk and red ne, dinning area kuma aka ƙawata gurin da red color. Relaxing yayi sama cushion yana furta sunan Namra, a zuciyarsa, haka kawai ta faɗo masa a rai, duk wacan dukiyar da aka narka masa a wacan gidan da Namra ta kama musu haya ubanta ne ya narka masa ita yayinda wannan kuma shi ne ya narka ma Mardiya. Haƙiƙa Namra ta yi masa hallacin da ba duk mace ce take yi ma namiji irin wannan hallacin ba.
“Dole wata rana zaki dawo gare ni Namra, dole idan kika haifa min ɗa ki dawo kina so na idan na karɓe abu na, zaki dawo ki ga yadda Asim yake amsa sunansa a cikin garin Katsina, daga lokacin zan nunawa Ubanki iko na da kuma karfin kuɗi na”
Ya furta yana jefar da kwankwanin power horse ɗin sannan ya ciro wayarsa daga aljihu ya nemo number Sufiyan ya aika masa kira, be damu da ganin dare yayi ba ganin yake tun da yana biyansa kuɗi dole ne ko a wane lokaci ya yi masa abunda yake so.
“Hello oga Allah yasa lafiya ka kira ni a wannan lokacin”
Ya faɗa cikin muryar bachi.
“Lafiya ƙalau, kana da labarin Namra? ”
“Akwai labari oga amman da ka hakƙura har da safe”
“Ba zan haƙura ba, faɗa min kawai”
“Oga wannan monday da ta wuce ta fara zuwa makaranta, na bita har makarantar na ganta Mahaifinta ya ɗaukar mata sabon direba, amman oga sam babu alamun ciki a tare da ita, dole ne idan har akwai cikin da zai tsawon wannan watannin ya nuna ko da kaɗan nan, sam ban ga alamun tana da ciki ba, kuma kaga da tana da ciki da ba zata koma karanta ba yanzu”
“Ka tabbata?”
“Na tabbata oga”
Ya katse kiran yana lasa lips ɗinsa.
“Idan ko har kika yi kuskuren zubar da cikin nan sai kin yi nadama Namra, ke da ubanki sai na kaskantaku”
Yayi ƙwafa tare da busar da iskar bakinsa. Ɗan kishingiɗawa yayi kaɗan sai bachi yayi gaba da shi daman a kwai gajiya sosai a tare da shi. Be yi bachin awa biyu ba ya soma jin hancins ana mugun yaji numfashinsa na sama-sama sai sarƙewa yake, ba shiri ya farka a firgice sai hayaki ya turniƙe masa ido, duhu ya soma gani sai tari yake kamin ya waiga ɗayan gefensa ya hango bedrooms ɗin suna ci da wuta. Wani irin tsalle ya daka ya sai gashi gaban ƙofar falo yana ƙoƙarin ɓanɓanreta amman ina hayaƙi da tsage ƙofar. Mai gadinsa ne ya farko yaga halin da ake ciki ya fita neman jama'a abunka da unguwar masu kuɗi sai kowa yayi maaa banza sai gaba ɗaya mutane suka fiffito, daker aka samu aka ɓalle ƙofar falon, suka fito da Asim, domin hayaƙi ya turniƙe shi tuni ya faɗi a gurin yana haƙi.
Kan kace kwabo sai ga ƴan fire service mota kusan uku aka shiga kashe wutar, amman kamar ana ƙarawa, haka wutar ta riƙa ci har asuba, bata mutu ba sai da ta ƙone komai na gidan.
Uffan Namra bata ce mata ba, har tayi surutunta ta gama ta koma gurin Abdool.
“Haƙiƙa kun dace da junanku, namiji irinka be dace da ko wace irin mace ba sai Namra kamar yadda ita ma bata dace da ko wane miJi ba sai kai, na yarda da ƙaddara haka Allah ya so ta kasance a gareni...”
“Amir...”
Ta ɗaga mishi hannu.
“Na fahimta, na gane ƙaddaratace a haka”
Bata jira abunda zai faɗa ba ta juya ta koma cikin gidansu, hawaye na mata zuba kamar ruwa. Buɗe motar Abdool yayi ya koma ciki ya zauna yana kallon fuskar Namra.
“Itace yarinyar da ta cutar da ke ko?”
“Abunda ta yi min tsakanina da ita ne, kai kuma sadaukarwar da ta maka tsakanin ka da ita ne, ka maida ni gidanmu ban yi tunanin ka ɗauko ni dan ka ɓata min rai ba, na tsani yarinyar nan na tsane ta, idan ma kana son ta ni ina ruwana karka sake kawo ni gurin, idan ma zaka so ka kaje can ka so ta ni karka sake sako ni a matsalar ku”
Shiru yayi yana saurarenta har ta yi masa faɗan ta gama sannan ya tashi motar yana murmushi ya suka nufi hanyar gida. Sarai kalamata suka wanke masa zuciya ɗan ya fahimci inda ta dosa. Yana yin fakin ya buɗe motar ta fita a hasale ta shiga cikin gida.
Wayarsa ya ɗauka ya kira Abbah suka yi magana sannan ya faka motarsa ya fita ya shiga part ɗinsa.
Yayi awa ɗaya a part ɗin Abbah sannan ya fito tare da Abbah ya shiga motarsa ya kama hanya.
KALSOOM POV.
FIVE MONTHS LATER...
Daga ita har su Izza basa da wata matsala a yanzu, tana zaune da yaran lafiya ƙalau ga Hajiya sai nuna musu kulawa take. duk wani rashin kunya na Izza ta watsar, ulfah kan ba a magana daman tun da warke daga jinyar ruwana zafi sai ta ƙara ladabi, dan sosai yanzu suka gane muhimmanci Kalsoom, gashi lokaci-zuwa lokaci takan kira musu mahaifiyarsu su gaisa, ranar weekend kuma Hilal ya kaisu gidan Hajiya. Idan zai dawo Hajiya ta bashi rubutu ya kawo mata na neman ta sauka lafiya. Babu yadda Teema ba tayi ba akan ta dawo gidan amman Hilal da Hajiya suka ƙi, su Izzah kan ko zancenta basa so.
***
Bayan ta ƙare waya da Salma ne ta kalli Hilal dake kwance gefenta yana wasa da wayarsa tace.
“Salma na gaishe ka”
“Ina amsawa, bari naje na ɗauko su izza scul”
Ya faɗa yana unƙurin tashi, kai kawai ta ɗaga masa dan maganar ma wahala take mata ko wayar da take da Salma na ƙarfin hali ne, tun jiya take jin abu amman ta kasa faɗa, duk da ta kan ji irin haka lokaci lokaci amman wannan ya tsananta mata da yawa. Aiko kamar karya tashi daga gurim ta soma jin ana tsikararta, har zaman ya gagareta sai da ta kwanta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Shi take ta maimaitawa tana rumtse rumtsen ido. waƴarta na kusa da ita amman ta kasa miƙa hannu ta ɗauka, wani irin juyi take jin duniya na mata, tun tana faɗar Innalillahi a hankali har ta fara yi da ƙarfi tana ta rumtsar ido da buɗewa kamar wacce ta ci bashi. Ko da Hilal ya ɗauko su Ulfah daga makaranta Kalsoom ta jigata, jini har ya fara mata zuba, daman tun safe ya kula da yadda cikin yayi mata ƙasa sosai. Ɗakinsa ya shiga ya ɗauko kayan karɓar haihuwa ya dawo ɗakinta ya shiga ya rufe ƙofar ya shiga bata taimako, because ya san it too late yace zai ɗauke ta suke asibiti a yanzu bayan ga har kan yaro ya fara fitowa😷
ASIM POV.
Tun bayan rasuwar Mama ya daina ganin kam kowa da gashi, gani yake tun da yayi losing mahaifiyarsa a yanzu baya gudun komai, haka zai shigo cikin sokoto ya kwana gurin ogansa, ba zai leƙa ƙanensa ba sai zai tafi sannan ya basu kuɗi mai yawa, babban gida ya siya musu, dan yana ganin kamar su ne family da suka rage masa yanzu. Sai duk lokacin da ya shiga sokoto sai ya binka labarin Namra ace masa tana nan lafiya, har wani ya ɗauka mai aikin bincika masa labarinta, dan a tunaninsa tana nan ɗauke da cikinsa, burinsa kawai ta haifa masa ɗan ko ya ya ɗauke ta dan kawai ya ɗasa mata baƙin ciki. Sati ɗaya da rasuwar Mama aka saka ranar aurensa da Mardiya, yadda yake kashe mata kuɗi sai ka rantse da Allah shi ne yake buga kuɗi, dan yana samun kuɗi sosai a yanzu manyan mutane yake tare da su. Ya faɗa musu baya buƙatar komai dan tun kamin a kai lefe ya saka komai a gidan da zata zauna, kama daga kayan kitchen har zuwa na kwalliya da sutura kai kace ma be mata lefen gaba ɗaya ba sai taje can, har kayan abinci babu abunda be zuba ba, freezer goma ya saka a gidan jo wace cike take da kayan daɗi.
Ranar talata aka fara event an zubar da naira a kamu sosai kasancewar Asim ya bawa kawaye amarya kuɗi sosai, gashi shi ma yaje shi da abokaninsa dan yanzu yayi sabin abokai yayan manya sai kuma masu irin aikinsa, duk wani gaye mai kuɗi da kasani a cikin garin katsina mai ji da kansa sai Asim yayi abota da shi, dan gani yake sune sa'o'insa.
Friday aka yi walima, a instagram Namra take ganin bikin kamun su, tayi mamakin da ya auri Mardiya dan bata manta lokacin da yake yawan maimaita mata cewar shi sai ƴar da ubanta ya fi nata kuɗi zai aure, wata ƙila farin jikinta ne ya jashi hankalinsa ko kuma bayan ya aureta zai ƙara wata.
Tun ranar da aka gyara ɗakin aka saka komai Asim yake kwana a gidan. Wasu abokansa da suka zo daga sokoto da Abuja sai ya kama musu hotel wasu kuma ya sauke su a ɗayan gidansa dake GRA, shi kuma ya koma Light up road inda gidan amaryarsa yake dan kwana. Light up unguwace ta masu kuɗi ko wanne gida ka gani sai ya burge ka, amman duk da haka a layin da Asim yake gidansa ya fi ko wanne gida kyau da tsari, kana ganinsa kasan ba ƙananan kuɗi aka kashe ba gurin gina shi.
Ƙarfe ɗaya da rabi na dare ya shigo gidan, cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, yana jinsa a wani matsayi na daban kwatankwacin matsayin da ya riƙa jin kamsa a lokacin da zai auri Namra, freezer da ke kitchen ya nufa ya buɗe ya ɗauko power horse ya fito falo yana sha. Kansa ya ɗaga sama yana kallon pop zuwa labulayen da aka saka falon, hantin kawai idan ka kalla sai ya burge ka, balle kuma kujera da plasma da flowers, daga kujera har center carpet da labulayen da da fantin ɗakin milk and red ne, dinning area kuma aka ƙawata gurin da red color. Relaxing yayi sama cushion yana furta sunan Namra, a zuciyarsa, haka kawai ta faɗo masa a rai, duk wacan dukiyar da aka narka masa a wacan gidan da Namra ta kama musu haya ubanta ne ya narka masa ita yayinda wannan kuma shi ne ya narka ma Mardiya. Haƙiƙa Namra ta yi masa hallacin da ba duk mace ce take yi ma namiji irin wannan hallacin ba.
“Dole wata rana zaki dawo gare ni Namra, dole idan kika haifa min ɗa ki dawo kina so na idan na karɓe abu na, zaki dawo ki ga yadda Asim yake amsa sunansa a cikin garin Katsina, daga lokacin zan nunawa Ubanki iko na da kuma karfin kuɗi na”
Ya furta yana jefar da kwankwanin power horse ɗin sannan ya ciro wayarsa daga aljihu ya nemo number Sufiyan ya aika masa kira, be damu da ganin dare yayi ba ganin yake tun da yana biyansa kuɗi dole ne ko a wane lokaci ya yi masa abunda yake so.
“Hello oga Allah yasa lafiya ka kira ni a wannan lokacin”
Ya faɗa cikin muryar bachi.
“Lafiya ƙalau, kana da labarin Namra? ”
“Akwai labari oga amman da ka hakƙura har da safe”
“Ba zan haƙura ba, faɗa min kawai”
“Oga wannan monday da ta wuce ta fara zuwa makaranta, na bita har makarantar na ganta Mahaifinta ya ɗaukar mata sabon direba, amman oga sam babu alamun ciki a tare da ita, dole ne idan har akwai cikin da zai tsawon wannan watannin ya nuna ko da kaɗan nan, sam ban ga alamun tana da ciki ba, kuma kaga da tana da ciki da ba zata koma karanta ba yanzu”
“Ka tabbata?”
“Na tabbata oga”
Ya katse kiran yana lasa lips ɗinsa.
“Idan ko har kika yi kuskuren zubar da cikin nan sai kin yi nadama Namra, ke da ubanki sai na kaskantaku”
Yayi ƙwafa tare da busar da iskar bakinsa. Ɗan kishingiɗawa yayi kaɗan sai bachi yayi gaba da shi daman a kwai gajiya sosai a tare da shi. Be yi bachin awa biyu ba ya soma jin hancins ana mugun yaji numfashinsa na sama-sama sai sarƙewa yake, ba shiri ya farka a firgice sai hayaki ya turniƙe masa ido, duhu ya soma gani sai tari yake kamin ya waiga ɗayan gefensa ya hango bedrooms ɗin suna ci da wuta. Wani irin tsalle ya daka ya sai gashi gaban ƙofar falo yana ƙoƙarin ɓanɓanreta amman ina hayaƙi da tsage ƙofar. Mai gadinsa ne ya farko yaga halin da ake ciki ya fita neman jama'a abunka da unguwar masu kuɗi sai kowa yayi maaa banza sai gaba ɗaya mutane suka fiffito, daker aka samu aka ɓalle ƙofar falon, suka fito da Asim, domin hayaƙi ya turniƙe shi tuni ya faɗi a gurin yana haƙi.
Kan kace kwabo sai ga ƴan fire service mota kusan uku aka shiga kashe wutar, amman kamar ana ƙarawa, haka wutar ta riƙa ci har asuba, bata mutu ba sai da ta ƙone komai na gidan.