Sashe 19
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Toh na gode sai na jiki”
Daga haka ta kashe wayar.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata Hilal be yi zuwa huɗu ba Daddy yace ya turo iyayensa. Shi kuma daman haka yake son yaji, satin daya zagawo iyayen Hilal suka neman auren Kalsoom, farin ciki gurin mahaifiyar Hilal kamar ta zuba ruwa ƙasa ta sha.
Iyayen basu bar gurin ba har sai da Daddy da ƴan'uwansa suka yanka musu sadakinta dubu saba'in suka biya sai Daddy yasa musu rana dan ba so yake aja abun da nisa ba, shirin da biyar ga watan huɗu. Cikin farinciki da jindaɗi suka bar gidan.
A ranar Rashida bata yi bachi ba saboda baƙinciki, kwana tayi kuka Hilal na rarrashinta. Washen garin ranar da akayi abun Kalsoom taje aiki sai suka riƙa taya ta murna suna ce mata amarya. Tayi mamakin inda suka samu labarin tun dai ita ban da ƙawarta Salma bata san ta faɗawa kowa ba, da Momy tace mata ƙara kawai mutane suji za'a ɗaura mata aure.
Sai daga baya suka faɗa mata ai Asma'u ce ta faɗa musu. Kalsoom ta kalli Asma'u tana dariya
“Asmee ina kika ji?”
“Abun sheri ma be ɓoyu ba balle na alheri”
“Ni ina mamakin ta ina kika ji”
“Ai tuni ni na sani dan har a wayar mijin naga hoton ki, ido na sa miki dan naga indan zaki faɗa”
Sai duk suka sa dariya. Suka mata barka da Allah yasa alheri.
Bayan ta wuce office ɗin ta Asmee ta bita tana zolayarta
“Amaryar mu amarya mu”
Kalsoom ta ɗora jakarta saman tebur tana dariya.
“Wai daman Hilal ɗan'uwan ku ne?”
“A'a unkuwar mu ɗaya dai da shi, kuma mijina abokin shi ne”
“Allah sarki ke haka unguwarku daya ba”
“Amman Wallahi kin yi dacen miji, gaskiya Hilal yana da mutunci sosai, gashi bawon mata sai yadda kika yi dashi, matarsa ma ba daɗinta yake ji ba amman sai juya shi take”
“Kin san matarsa kenan?”
“Sosai ma, amman wallahi ƴar banza ce sai kin shirya zama da ita hmmm amman aje aikinki zakiyi ko?”
“Haka yace wai baya son aiki”
“Ai saboda aikin matarsa zai ƙara aure dan ya son ya hanata aiki amman ba dama”
“Saboda me?”
“Ai ma'aikaciyar banki ce ƴar gidan su Dr. Ayuba matsayi, kin san ai ƴaƴan gidan ba daga baya ba, haka ake cewa wai aba a musu kishiya, uwarsu ma duk masifar Uban sai tun da ya aure mui”
Ta ƙarasa tana shafa baki. Ganin yadda Kalsoom ke kallonta yasa ta tsargu sai ta tashi daga saman kujerar da take zaune tana dariya tace
“Bari na koma gurin zamana kar MD ya tararda ni a nan ina tsiyaya”
Nan ma Kalsoom murmushi kawai tayi. Sai ta nufi ƙofa tana faɗin
“Mu dai ayi auren nan da wuri aje ayi mana rainon ƴan ɗiyan mu, Allah ya sanya alheri”
Da Amin Kalsoom ta amsa ta bita da kallo tana nazarin maganganunta.
NAMRA POV.
Wuni Namra tayi addu'ah tana ba Allah cigiyar inda Amira take. Duk hankalinta ya tashi ji take kamar ita ce ta ɓata, abu ɗaya zuciyarta ke ayyana mata wato Uzair, sai dai ta kan tambayi kanta da kanta ma zai haɗa alaƙa tsakanin Uzair da Amira.
Kiran da taji Maryam tana mata yasa ta tashi daga saman sallayar da take ta nufi falo.
Tsatsaye ta tararda su Anty Amarya da wasu police biyu mata tsaye a falo. Gaban Namra ya faɗi, da sauri ta ƙaraso kusa da su.
“Lafiya?”
Sai ɗaya daga cikin ƴan sandar ta nuna mata id cart ɗinta.
“From Marna Police station, Muna zargin da a hannu gurin kidnapping ɗin Amira, abokan aikin mu suna waje, zamu je da ke a station”
Ba shiri Namra ta daki ƙirgi tana nuna kanta.
“Ni....?”
Da sauri Maryam ta nufi part ɗin Abbah tana kuka. Anty Amarya ma kuka take ita da Aisha. Kamar an jefo Hajiya Barau sai gata cikin ɗakin tana salati da sallami.
____________________________________
THERE WORDS FOR THIS CHAPTER...!
WHAT DO YOU EXPECT NEXT?
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 😘💖🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa12.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 15*
Suna fitowa waje Abbah na kawowa. Sai ya tsayar da ƴan sanda yana tambayarsu.
“Miya faru haka?”
“Sir muna tuhumar Namra ne da sa hannu a gurin sace Amira”
Abbah yayi ma Namra wani kallo. Sannan ya kalli ƴan sanda yace
“Ɗaya daga cikin ku zata biyo ni muje cikin motana”
Ba su musa masa ba, ɗaya daga cikin police ɗin ta bi Abbah suka shiga mota ita da Namra baya, Anty Amarya a front seat.
In banda kuka babu abunda Namra take har aka isa station ɗin. Sannan Abbah ya fita suka shiga cikin station ɗin. Ammy da ƙanwarta na tsaye a gurin idonta A kumbure.
A take wani police ya karanto masa abunda ake zargin Namra da shi, sannan yayi musu jaga zuwa office ɗin dpo. Sai da ya gama da wasu cases sannan ya su Namra suka iso gurin ya gaisa da Abbah cikin mutumci yana girmama shi.
“Ranka ya daɗe Ashe kai ne”
“Nine Wallahi ya aiki ya kwana biyu”
Abbah ya faɗa ba dan ya waye shi, sai dai shi ɗin yasan Abbah kasancewarshi sanannen ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa.
Bayan Abbah ya zauna, Namra ta zauna a kujera dake kusa da Abbah, sai Ammy ta zauna a kujarar dake gefen Namra ita da ƙanwarta.
DPO ya kalli ya dubi takarda take gabansa ya kalli Namra yace
“Amm Namra Usman ana zargin ki dasa hannu gurin ɓatan ƙawarki Amira...”
Kasa magana Namra tayi sai kuka take. Abbah ya katsa mata tsawa.
“Ki buɗe baki kiyi magana mana”
Sai kawai ta ƙara rushewa da kuka kamar zata tsuƙe. Anty Amarya tace
“Taya zata iya magana? Bayan irin ƙazafin da aka mata, a rasa wanda za'a zarga sai ita, lokacin da Namra ta ɓata miyasa bamu zargi Amira ba, ko ita Namra ba ƴa bace? Ko kuma ni ban san zafin ta ba? Faɗa min ɗa ya fi ɗa ne? Wallahi Allah sai ya saka mata shikenan dan anga yarinya bata magana komai aka kwaso sai a dire a kanta, dan kin rikice akan neman ƴarki sai ki ɗauka ki ɗorawa wani, me kuke da shi da har Namra zata sa a ɗauke Amira, wallahi ke kinsan Namra ta fi ƙarfin Amira nesa ba kusa ba...”
Dpo ya miƙe tsaye yana ɗaga ma Anty Amarya hannu.
“Dan Allah Hajiya ki saurara, an zo nan dan a sasanta ba dan faɗa ba”
Bayan ya zauna ya kalli Namra yace
“Ki kwantar da hankalin ki ba wani za'a miki ba, nan guri ne na...”
Ƙwanƙwasa ƙofar da akayi ne ya hana Dpo ƙarasa maganarsa.
“Yes come in”
Wani ɗan sanda ne ya shigo ya sare masa sannan yace
“Sir Alhaji Haruna is here to see you”
“Let him in”
“Yes Sir”
Ya sake sare masa sannan ya juya ya fice. Sai ga Abbah Amira ya shigo cikin ɓacin rai, idonsa be sauka ko ina ba sai akan Ammy, nunata yayi da yatsa.
“Amman Wallahi Asiya baki jin magana, yanzu duk maganar da na miki baki ji ba, sai da kika aikata? Yanzu miye amfanin haka? Ki zubar da kanki mutuncin kawai”
Ya ƙarasa yana miƙawa dpo hannu suka gaisa.
“Wannan maganar bata ma kamata ta fito bakin ki ba, dpo ban kawo maka rahoton ɓatan yarinyar nan ba? Babu inda ban kai rahoton nan ba”
Dpo ya ɗaga masa kai yana murmushi. Abban Amira ya miƙa Abbah hannu suka gaisa
“Alhaji Usman, yau dai mun yi zumunci dole, mata sun haɗa mu”
Abbah yayi dariya.
“Kasan sha'anin mata sai haƙuri, ba tunani suke ba idan zasu yi abu”
“Wallahi basa tunani yanzu miye amfanin wannan abun? Yanzu haka sai da aka kira ni daga gwuiwa station aka ce min ance anga Amira a tashar mota amman basu san motar data shiga ba”
Ammy ta fashe da kuka.
“Wallahi babu abunda ze sa Amira ta gudu tun da ba wani abu muka mata ba”
“Toh aljana ce aka gani kenan? Ko kuma ƙarya suke, tashi ki wuce gida bana son maganganun banza”
Cewar Alhaji Haruna Abban Amira. Abbah yace
“Karka ga laifin ta duk haka muke fama dasu inda mata ne sai haƙuri”
“Magana ce da bata da toshe balle makama ban san inda ma wannan maganar ta fito ba”
Cikim kuka tace Ammy tace.
“Hajiya Barau ce ta faɗa kuma ai ba zata yi ƙarya ba”
Abban Amira ya nuna ta da hannu yana kallon Abbah.
“Kaji ko? Jita-jita ne kawai”
Abbah yayi shiru yana motsa baki alamar nazari. Alhaji Haruna ya kalli Ammy da Ƙanwarta yace
“Ku tashi muke gida”
Da kuka Ammy ta tashi ta fice, sannan ya kalli dpo ya ciro wasu ƴan kudaɗe a aljihunsa ya aje gaban teburin dpo
“Dan Allah aka kashe maganar nan dpo, matsala ta cikin gida ayi haƙuri”
“Ba matsala, muma ai mun fi son haka”
Tare da Abbah suka fito. Anty Amarya na riƙe da Namra har suka fito harabar station ɗin. Sun ɗan daɗe suna fira da Alhaji Haruna sannan sukayi sallama cikin mutunci ya wuce Abbah kuma ya nufi Motarsa.
Har Abbah ya iso gida Anty Amarya masifa take, tana kiran Hajiya Barau da munafuka.
“Ai itama ta haifi ƴaƴa mata, zata jidaɗi idan aka mata haka? Me Namra ta tare mata ne? Ai Wallahi duk mace data ɗuka ta haifi mace tace wata macen ba zata jidaɗi ba sai Allah ya gwada mata akan ƴaƴanta”
Sai da Abbah yayi parking sannan ya kalli Anty Amarya yace
“Bana son ƙananan maganganu, ki wuce part ɗin ki ki bar ni da ita kawai”
Bata sake cewa komai ba, dan tasan halin Abbah zai iya juyarda faɗan akanta. Sai kawai ta buɗe ta fita ita da Namra suka nufi part ɗinta Abbah kuma ya nufi part ɗin Hajiya Barau.
Tana ganin Abbah hankalinta yayi mugun tashin, kamar tasan asirinta ya tono, ko da yake ta karanci yanayinsa shiyasa zuciyarta ta ayyana mata lallai akwai laifin da tayi masa.
Daga haka ta kashe wayar.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata Hilal be yi zuwa huɗu ba Daddy yace ya turo iyayensa. Shi kuma daman haka yake son yaji, satin daya zagawo iyayen Hilal suka neman auren Kalsoom, farin ciki gurin mahaifiyar Hilal kamar ta zuba ruwa ƙasa ta sha.
Iyayen basu bar gurin ba har sai da Daddy da ƴan'uwansa suka yanka musu sadakinta dubu saba'in suka biya sai Daddy yasa musu rana dan ba so yake aja abun da nisa ba, shirin da biyar ga watan huɗu. Cikin farinciki da jindaɗi suka bar gidan.
A ranar Rashida bata yi bachi ba saboda baƙinciki, kwana tayi kuka Hilal na rarrashinta. Washen garin ranar da akayi abun Kalsoom taje aiki sai suka riƙa taya ta murna suna ce mata amarya. Tayi mamakin inda suka samu labarin tun dai ita ban da ƙawarta Salma bata san ta faɗawa kowa ba, da Momy tace mata ƙara kawai mutane suji za'a ɗaura mata aure.
Sai daga baya suka faɗa mata ai Asma'u ce ta faɗa musu. Kalsoom ta kalli Asma'u tana dariya
“Asmee ina kika ji?”
“Abun sheri ma be ɓoyu ba balle na alheri”
“Ni ina mamakin ta ina kika ji”
“Ai tuni ni na sani dan har a wayar mijin naga hoton ki, ido na sa miki dan naga indan zaki faɗa”
Sai duk suka sa dariya. Suka mata barka da Allah yasa alheri.
Bayan ta wuce office ɗin ta Asmee ta bita tana zolayarta
“Amaryar mu amarya mu”
Kalsoom ta ɗora jakarta saman tebur tana dariya.
“Wai daman Hilal ɗan'uwan ku ne?”
“A'a unkuwar mu ɗaya dai da shi, kuma mijina abokin shi ne”
“Allah sarki ke haka unguwarku daya ba”
“Amman Wallahi kin yi dacen miji, gaskiya Hilal yana da mutunci sosai, gashi bawon mata sai yadda kika yi dashi, matarsa ma ba daɗinta yake ji ba amman sai juya shi take”
“Kin san matarsa kenan?”
“Sosai ma, amman wallahi ƴar banza ce sai kin shirya zama da ita hmmm amman aje aikinki zakiyi ko?”
“Haka yace wai baya son aiki”
“Ai saboda aikin matarsa zai ƙara aure dan ya son ya hanata aiki amman ba dama”
“Saboda me?”
“Ai ma'aikaciyar banki ce ƴar gidan su Dr. Ayuba matsayi, kin san ai ƴaƴan gidan ba daga baya ba, haka ake cewa wai aba a musu kishiya, uwarsu ma duk masifar Uban sai tun da ya aure mui”
Ta ƙarasa tana shafa baki. Ganin yadda Kalsoom ke kallonta yasa ta tsargu sai ta tashi daga saman kujerar da take zaune tana dariya tace
“Bari na koma gurin zamana kar MD ya tararda ni a nan ina tsiyaya”
Nan ma Kalsoom murmushi kawai tayi. Sai ta nufi ƙofa tana faɗin
“Mu dai ayi auren nan da wuri aje ayi mana rainon ƴan ɗiyan mu, Allah ya sanya alheri”
Da Amin Kalsoom ta amsa ta bita da kallo tana nazarin maganganunta.
NAMRA POV.
Wuni Namra tayi addu'ah tana ba Allah cigiyar inda Amira take. Duk hankalinta ya tashi ji take kamar ita ce ta ɓata, abu ɗaya zuciyarta ke ayyana mata wato Uzair, sai dai ta kan tambayi kanta da kanta ma zai haɗa alaƙa tsakanin Uzair da Amira.
Kiran da taji Maryam tana mata yasa ta tashi daga saman sallayar da take ta nufi falo.
Tsatsaye ta tararda su Anty Amarya da wasu police biyu mata tsaye a falo. Gaban Namra ya faɗi, da sauri ta ƙaraso kusa da su.
“Lafiya?”
Sai ɗaya daga cikin ƴan sandar ta nuna mata id cart ɗinta.
“From Marna Police station, Muna zargin da a hannu gurin kidnapping ɗin Amira, abokan aikin mu suna waje, zamu je da ke a station”
Ba shiri Namra ta daki ƙirgi tana nuna kanta.
“Ni....?”
Da sauri Maryam ta nufi part ɗin Abbah tana kuka. Anty Amarya ma kuka take ita da Aisha. Kamar an jefo Hajiya Barau sai gata cikin ɗakin tana salati da sallami.
____________________________________
THERE WORDS FOR THIS CHAPTER...!
WHAT DO YOU EXPECT NEXT?
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 😘💖🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa12.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 15*
Suna fitowa waje Abbah na kawowa. Sai ya tsayar da ƴan sanda yana tambayarsu.
“Miya faru haka?”
“Sir muna tuhumar Namra ne da sa hannu a gurin sace Amira”
Abbah yayi ma Namra wani kallo. Sannan ya kalli ƴan sanda yace
“Ɗaya daga cikin ku zata biyo ni muje cikin motana”
Ba su musa masa ba, ɗaya daga cikin police ɗin ta bi Abbah suka shiga mota ita da Namra baya, Anty Amarya a front seat.
In banda kuka babu abunda Namra take har aka isa station ɗin. Sannan Abbah ya fita suka shiga cikin station ɗin. Ammy da ƙanwarta na tsaye a gurin idonta A kumbure.
A take wani police ya karanto masa abunda ake zargin Namra da shi, sannan yayi musu jaga zuwa office ɗin dpo. Sai da ya gama da wasu cases sannan ya su Namra suka iso gurin ya gaisa da Abbah cikin mutumci yana girmama shi.
“Ranka ya daɗe Ashe kai ne”
“Nine Wallahi ya aiki ya kwana biyu”
Abbah ya faɗa ba dan ya waye shi, sai dai shi ɗin yasan Abbah kasancewarshi sanannen ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa.
Bayan Abbah ya zauna, Namra ta zauna a kujera dake kusa da Abbah, sai Ammy ta zauna a kujarar dake gefen Namra ita da ƙanwarta.
DPO ya kalli ya dubi takarda take gabansa ya kalli Namra yace
“Amm Namra Usman ana zargin ki dasa hannu gurin ɓatan ƙawarki Amira...”
Kasa magana Namra tayi sai kuka take. Abbah ya katsa mata tsawa.
“Ki buɗe baki kiyi magana mana”
Sai kawai ta ƙara rushewa da kuka kamar zata tsuƙe. Anty Amarya tace
“Taya zata iya magana? Bayan irin ƙazafin da aka mata, a rasa wanda za'a zarga sai ita, lokacin da Namra ta ɓata miyasa bamu zargi Amira ba, ko ita Namra ba ƴa bace? Ko kuma ni ban san zafin ta ba? Faɗa min ɗa ya fi ɗa ne? Wallahi Allah sai ya saka mata shikenan dan anga yarinya bata magana komai aka kwaso sai a dire a kanta, dan kin rikice akan neman ƴarki sai ki ɗauka ki ɗorawa wani, me kuke da shi da har Namra zata sa a ɗauke Amira, wallahi ke kinsan Namra ta fi ƙarfin Amira nesa ba kusa ba...”
Dpo ya miƙe tsaye yana ɗaga ma Anty Amarya hannu.
“Dan Allah Hajiya ki saurara, an zo nan dan a sasanta ba dan faɗa ba”
Bayan ya zauna ya kalli Namra yace
“Ki kwantar da hankalin ki ba wani za'a miki ba, nan guri ne na...”
Ƙwanƙwasa ƙofar da akayi ne ya hana Dpo ƙarasa maganarsa.
“Yes come in”
Wani ɗan sanda ne ya shigo ya sare masa sannan yace
“Sir Alhaji Haruna is here to see you”
“Let him in”
“Yes Sir”
Ya sake sare masa sannan ya juya ya fice. Sai ga Abbah Amira ya shigo cikin ɓacin rai, idonsa be sauka ko ina ba sai akan Ammy, nunata yayi da yatsa.
“Amman Wallahi Asiya baki jin magana, yanzu duk maganar da na miki baki ji ba, sai da kika aikata? Yanzu miye amfanin haka? Ki zubar da kanki mutuncin kawai”
Ya ƙarasa yana miƙawa dpo hannu suka gaisa.
“Wannan maganar bata ma kamata ta fito bakin ki ba, dpo ban kawo maka rahoton ɓatan yarinyar nan ba? Babu inda ban kai rahoton nan ba”
Dpo ya ɗaga masa kai yana murmushi. Abban Amira ya miƙa Abbah hannu suka gaisa
“Alhaji Usman, yau dai mun yi zumunci dole, mata sun haɗa mu”
Abbah yayi dariya.
“Kasan sha'anin mata sai haƙuri, ba tunani suke ba idan zasu yi abu”
“Wallahi basa tunani yanzu miye amfanin wannan abun? Yanzu haka sai da aka kira ni daga gwuiwa station aka ce min ance anga Amira a tashar mota amman basu san motar data shiga ba”
Ammy ta fashe da kuka.
“Wallahi babu abunda ze sa Amira ta gudu tun da ba wani abu muka mata ba”
“Toh aljana ce aka gani kenan? Ko kuma ƙarya suke, tashi ki wuce gida bana son maganganun banza”
Cewar Alhaji Haruna Abban Amira. Abbah yace
“Karka ga laifin ta duk haka muke fama dasu inda mata ne sai haƙuri”
“Magana ce da bata da toshe balle makama ban san inda ma wannan maganar ta fito ba”
Cikim kuka tace Ammy tace.
“Hajiya Barau ce ta faɗa kuma ai ba zata yi ƙarya ba”
Abban Amira ya nuna ta da hannu yana kallon Abbah.
“Kaji ko? Jita-jita ne kawai”
Abbah yayi shiru yana motsa baki alamar nazari. Alhaji Haruna ya kalli Ammy da Ƙanwarta yace
“Ku tashi muke gida”
Da kuka Ammy ta tashi ta fice, sannan ya kalli dpo ya ciro wasu ƴan kudaɗe a aljihunsa ya aje gaban teburin dpo
“Dan Allah aka kashe maganar nan dpo, matsala ta cikin gida ayi haƙuri”
“Ba matsala, muma ai mun fi son haka”
Tare da Abbah suka fito. Anty Amarya na riƙe da Namra har suka fito harabar station ɗin. Sun ɗan daɗe suna fira da Alhaji Haruna sannan sukayi sallama cikin mutunci ya wuce Abbah kuma ya nufi Motarsa.
Har Abbah ya iso gida Anty Amarya masifa take, tana kiran Hajiya Barau da munafuka.
“Ai itama ta haifi ƴaƴa mata, zata jidaɗi idan aka mata haka? Me Namra ta tare mata ne? Ai Wallahi duk mace data ɗuka ta haifi mace tace wata macen ba zata jidaɗi ba sai Allah ya gwada mata akan ƴaƴanta”
Sai da Abbah yayi parking sannan ya kalli Anty Amarya yace
“Bana son ƙananan maganganu, ki wuce part ɗin ki ki bar ni da ita kawai”
Bata sake cewa komai ba, dan tasan halin Abbah zai iya juyarda faɗan akanta. Sai kawai ta buɗe ta fita ita da Namra suka nufi part ɗinta Abbah kuma ya nufi part ɗin Hajiya Barau.
Tana ganin Abbah hankalinta yayi mugun tashin, kamar tasan asirinta ya tono, ko da yake ta karanci yanayinsa shiyasa zuciyarta ta ayyana mata lallai akwai laifin da tayi masa.