Sashe 130
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Duk yarda da Amincin dake tsanina da ke, ace kin rumtse ido ta auren ki kin yi zaman banza da mijina? Ina tunanin nayi abunda zan iya na hanasa aure, ashe na kashe macijina ban tsare kan ba, wallahi ko a mafarki ban za ci zaki min haka ba, ƴar iska macuciya, ai wallahi sai kin ga abun ki, dan Teema sai ta salwantar da rayuwar ƴaƴanki... Kuma Allah ya isa tsakanina da ke!”
Ta fisgi gyalenta ta fice a fusace. Rashida kan kuka kawai take, tana mai jin tsantsar damuwa da nadama a zuciyarta. Kuka tayi sosai, daman kullum cikin yinsa take, sannan ta koma ɗakinta ta ɗauki kkaton hijab ta saka ta saka niƙab ta ɗauki makullun motar ta ta fice.
ABDOOL POV.
Tun da ya baro ƙofar gidansu Lamido cikin farinciki yake, dan yasan sahibarsa ma tana can tana farinciki, kuma yasan zai samu ladar sulhunta uwa da ƴarta, horn ɗaya yayi aka buɗe masa gate, cikin nishaɗi yayi fakin motarsa ya fito da murmushi kamar wanda aka yi ma albishir.
What he saw a bakin ƙofar shiga part ɗinsa was surprise him, kurciyar daya gani a abuja itace a nan? Haske ne ta ko ina a gidan kamar rana, hakan ya bashi damar ganin layan dake wuyanta.
“Umar...”
Ya ƙwalawa Mai kula.da gidan kira, sai ga shi da gudu yana amsa kiran da yake masa. Keys ɗinsa ya miƙa masa.
“Zagaya ta baya ka buɗe ƙofar nan a hankali, kurciyarta nake son ta shiga ciki mu kamata”
“Ranka ya daɗe ai za'a iya halbeta da danƙo”
“Kana da danƙon ne? Kasan yadda zaka halbeta bata tashi ba?”
“Eh za a iya saitawa, amman ranka ya daɗe kurciya da dare baka san me take nufi ba, balle kuma ga laya a wuyanta”
“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”
“Toh”
Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.
“Namra”
Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.
“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”
Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.
“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”
Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.
KALSOOM POV.
Hannu ya kai ya shafa fuskarta.
“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”
Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.
“Zan shiga wanka”
Hannunta ya riƙe.
“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”
Ta saka mashi kuka.
“Baka min komai ba, kawai dai...”
miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.
“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”
Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.
“Ina son zogale”
“Okay”
Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.
ASIM POV.
Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.
“Hajiya na saka kuɗin”
“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”
“Okay na zo kenan?”
“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”
“Toh ya za'ayi kenan”
“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”
“Okay what time zan zo?”
“An jima da yamma”
“Okay Allah ya kai mu”
Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.
“Ta tabbata Nably ƴarki ce”
Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.
Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.
“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”
Ya ɗan sosa kansa.
“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”
“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”
“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”
Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.
“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”
Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.
________________________________
BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️
*77*
Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.
“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”
“Akan mi, mi zan miki?”
“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”
“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”
“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”
Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.
“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”
Hawaye ya cika idon Rashida.
“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”
“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”
Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.
“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”
Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.
*** *** ***
Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.
Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.
“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”
“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”
Ta fisgi gyalenta ta fice a fusace. Rashida kan kuka kawai take, tana mai jin tsantsar damuwa da nadama a zuciyarta. Kuka tayi sosai, daman kullum cikin yinsa take, sannan ta koma ɗakinta ta ɗauki kkaton hijab ta saka ta saka niƙab ta ɗauki makullun motar ta ta fice.
ABDOOL POV.
Tun da ya baro ƙofar gidansu Lamido cikin farinciki yake, dan yasan sahibarsa ma tana can tana farinciki, kuma yasan zai samu ladar sulhunta uwa da ƴarta, horn ɗaya yayi aka buɗe masa gate, cikin nishaɗi yayi fakin motarsa ya fito da murmushi kamar wanda aka yi ma albishir.
What he saw a bakin ƙofar shiga part ɗinsa was surprise him, kurciyar daya gani a abuja itace a nan? Haske ne ta ko ina a gidan kamar rana, hakan ya bashi damar ganin layan dake wuyanta.
“Umar...”
Ya ƙwalawa Mai kula.da gidan kira, sai ga shi da gudu yana amsa kiran da yake masa. Keys ɗinsa ya miƙa masa.
“Zagaya ta baya ka buɗe ƙofar nan a hankali, kurciyarta nake son ta shiga ciki mu kamata”
“Ranka ya daɗe ai za'a iya halbeta da danƙo”
“Kana da danƙon ne? Kasan yadda zaka halbeta bata tashi ba?”
“Eh za a iya saitawa, amman ranka ya daɗe kurciya da dare baka san me take nufi ba, balle kuma ga laya a wuyanta”
“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”
“Toh”
Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.
“Namra”
Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.
“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”
Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.
“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”
Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.
KALSOOM POV.
Hannu ya kai ya shafa fuskarta.
“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”
Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.
“Zan shiga wanka”
Hannunta ya riƙe.
“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”
Ta saka mashi kuka.
“Baka min komai ba, kawai dai...”
miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.
“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”
Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.
“Ina son zogale”
“Okay”
Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.
ASIM POV.
Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.
“Hajiya na saka kuɗin”
“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”
“Okay na zo kenan?”
“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”
“Toh ya za'ayi kenan”
“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”
“Okay what time zan zo?”
“An jima da yamma”
“Okay Allah ya kai mu”
Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.
“Ta tabbata Nably ƴarki ce”
Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.
Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.
“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”
Ya ɗan sosa kansa.
“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”
“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”
“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”
Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.
“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”
Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.
________________________________
BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️
*77*
Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.
“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”
“Akan mi, mi zan miki?”
“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”
“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”
“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”
Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.
“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”
Hawaye ya cika idon Rashida.
“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”
“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”
Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.
“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”
Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.
*** *** ***
Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.
Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.
“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”
“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”