Sashe 154
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wallahi na kai mata, sai dai ban ji wata magana daga gareta ba, Uzair ina son na.baka shawara akan rayuwa, ka yi haƙuri ka rumgumi ƙaddara, wannan abun da ka gani na ishi kowa ishara ni kaina wannan ciwon naka yasa na zubar da duk wata muguwar da nake da ita, ba kai kaɗai ba, yawancin duk mai aikata irin wannan matsalar ce take faɗa musu, ka duba lamarinka Uzair ba haɗarin mota ka yi ba, ba kuma faɗowa kayi daga wani guri ba, haka kawai rana tsaka ance ka kamu da irin wannan ciwon, ita kanta Amira yanzu ta kanta take balle ka zargeta da aikata maka wani mummunan abu”
Tun da Tahir ya fara masa maganar jikinsa yayi sanyi, be san lokacin da hawaye suka zubo masa ba, lallai maso rai wawa, haƙiƙa yanzu Tahir ya lurar da shi abunda be kasa ganewa.
“Na gode”
Shine kawai abunda ya faɗa ya katse kiran. Hawaye na cigaba da masa zuba, tabbas wannan kawai ya isheshi ishara, a yanzu idan ba Mahaifiyarsa babu kowa a tare da shi, zai barwa ɗansa mumman tahirin da ba zai taɓa goguwa ba har a bada.
Kekenshi ya tura ya koma cikin falon, ƙanensa na zaune sai sha'aninsu suke ko kula da shi basu yi haka ya tura kansa ya shiga ɗakin da aka ware masa ya zamo kamar nasa. Farar takadarda da ya gani a saman gadonshi ya kai hannu ya ɗauka.
Sammaci ne daga kotun high court, ganin sunan Yasmin yasa shi murmushin da ya fi kuka ciwo, sannan ya sake tura kekena ya fito falon yana tambayar wanda ya kai masa wasiƙar.
“Ɗazu ne kana shan magani aka kawo, na shiga ban ganka ba shine na aje saman gadonka”
Ƙaramar ƙanwarsa ta faɗa. Sai kawai ya kaɗa keken ya nufi ɗakin Umma.
***
Hankalin Mai Martaba ya kwanta yanzu, har ma da na Ummi. Ganin an tsayarda magana, ranar da Mai Martaba ya aika aka yi maganar aure har da sadaka sai da yayi. Sai dai tun daga lokacin magana ta riƙa zuwa tana dawowa akan Abdallah zai auri bazawara, abun mamaki ne mutun kamar Abdallah ace zai auri bazawara kuma ɗan Sarkin Ƙatsina, wanda hakan sam be yi ma Mai Martaba daɗi ba, sai dai ya kan zuciyarsa nesa domin kawai ya farantawa ɗansa, domin yasan Annabi ma ya auri bazawara kuma yana sauranyinsa.
Ita kanta Ummi tana shan magana akan aure wasu su ce kar ta barshi wasu kuma su ce kamata yayi ya haɗa biyu. Sai dai duk wannan maganganun da ake be taɓa zuwa kunnen Abdool ba, ko da wasa ƴan'uwa da abokai basu taɓa masa wannan maganar ba, saboda sun san waye Abdool idan yana yin abu yana yi ne no matter what, ao faɗa mishi irin wannan maganar zai sa ya ɓata da kai ne kawai, ko kuma kai ma ya faɗa maka marar daɗi, sai dai abokai sun ka zolayeshi cikin wasa. Babu abunda yayi masa daɗi kamar auren da Abbah be yarda aka saka nesa ba, shi kansa da ansaka auren nesa zai roƙa a rage ne, domin ya matsu ya ɗauke Namra daga gidan. Ta ɓamgare ɗaya me yake jin zai iya zame masa matsala karatunta da take yanzu.
NAMRA POV...
Babu inda zance baikon Namra be kai ba cikin garin Sokoto da kewaye, a social media kan ba zaka iya lissafawa ba, babu abunda zai baka mamaki kamar ace bazawara ce aka yi ma wannan kayan, kuma duk da sunan an gani ana so abunda aka san budurwa ake yiwa. Kayan ƙwalah da maƙulashe ba zaka iya ƙigarsu ba, ga akwati goma da aka sako na tufafi har da zinari duk a cikin an gani ana so, kowa abunda yake faɗa to lefen me za'ayi?
Ba a gidan aka kawo kayan ba, daman haka Abbah yake duk lokacin da za a yanka ma ƴaƴansa sadaki ko a kai lefensu, gidan ƴaƴanshi yake turawa.
Ko da ake hidimar kai kayan Namra tana makaranta a lokacin duk da yake asabarce amman a ranar tana da darasin (lecture) da zata ɗauka a makaranta, bayan sun gama tayi sallama ta abokanta ta nufo gurin da tasan Lamido ya saba tsayawa ya jirata.
Ko da ta isa yana zaune cikin motar buɗewa kawai ta yi ta shiga ta zauna sai kawai taji ya ce
“Congratulations”
Tasan abunda yake nufi, yanayin muryarsa ya karantar da ita baya cikin daɗin rai.
“Na amince da auren Abdallah ne saboda mahaifina, kuma na san kai ma baka ƙi goya min baya ba wajen amincewa da hakan”
“Abdallah ya kasa ni, daman ya faɗa min zai kasa ni, ta tabba yanzu shi ne a zuciyarki ba kowa ba”
“Ya faɗa maka? Alfahari yayi, fariya yayi da zai kasa ka? Yaushe bakin ka ɗa nashi ya taɓa haɗuwa?”
Yayi ma motar key yana cigaba da magana a hankali.
“Bayan tafiyarki, abubuwa da tawa sun faru, ciki har da dalilin zuwa neman aurenki, da kuma neman zama direba a gidanku...”
Ta gyara zamanta a gidan bayan da take.
“Ban gane ba dan Allah ka ƙara min bayani, karka ɓoye min komai”
“Bayan kin bar Kaduna da kwana biyu, Yarima yasa aka ɗauko ni daga Kaduna aka kawo ni Katsina, mahaifata garin da ƙabarin ubana yake, kuma garin da nayi alƙawarin ba zan sake takawa ba.....”
Kamar wanda ya tuna abu sai kawai yayi shiru ya cigaba da driving ɗin da yake. Ita kuma gaba ɗaya natsuwarta ta bar jikinta hankalinta ya karkata kan labarin da Lamido ya fara bata...
IS BETTER THAN NONE... 😎 YI HAKURI DA SHORT CHAPTER 🙏
[7/23, 9:21 PM] Khadeeja Candy♥: *88*
“Ka tsayarda motar nan Lamido”
Ta faɗa a tsawace, umarninta yake bi tunda danta yake wannan aikin, a dole ya faka mota a gefen ti-ti, sai dai be juyo ya kelleta ba balle yace mata wani abu.
“Miyasa Abdallah ya sa aka kai Katsina? Miya ce maka? Miya faru bayan na baro Kaduna?”
“Faɗa miki abunda ya faru ba zai yi maganin komai ba”
“Wata ƙila zai yi wata ƙila kuma ba zai yi ba, amman faɗin shine mafi a'ala”
“Ni da Mahaifina asalin mu fulanin Katsina ne, mahaifiyata kuma ƴar asalin jihar kano ce, mahaifina ɗan kasuwa ne ya kan ɗauki kaya daga Katsina ya kai Kaduna idan ya siyar sai ya siyo na Kaduna ya kawo Katsina da hakan abun nasa ya girma, har ta kai ya kan ɗauka daga Katsina ya kai Nijar, a lokacin muna ƙanana, iya gata mahaifinmu ya nuna da kulawa mun taso cikin jindaɗi, arkizin mahaifinmu ya bunƙasa cikin ƙanƙanen lokaci, sai dai mahaifin mu be da amini irin Alhaji Mu'azu, ita kanta mahaifiya bata da ƙawa irin Hajiya Zuwaira, ba unguwar mu ɗaya ba, amman duk ranar weekend sai an kawo yaranta gidanmu su yi weekend, bana da wayo sosai a lokacin, amman ina jin yadda Mahaifina yake faɗin idan har ya haɗa wannan kuɗin ya tura aka turo masa kaya zai samu kuɗi sosai, haka ya tattara komai na shi ya haɗa kai da Aminsa ya tura kudaɗensa masu yawa sosai. Shiru-shiru babu kaya babu labarinsu, har ta kai mun fara shiga wani hali na ha'ila i, Alhaji Mu'azu ne yake aiko mana da cefane wani lokacin kuma har da ɗinkuna da wasu abubuwan na more rayuwa, ashe duk wannan yana masa ne a cikin kuɗin da yake binsa, wata ranar Assabar mahaifina yake labarta masa kayansa suna nan zuwa, har an kamo hanyar nigeria da su ta jirgin ruwa, haka muka ɗauki tsawon wata ɗaya muna jiran isowar jirgin, sai kawai dirar ƴan sanda muka gani a gidanmu, wai ana zarginsa da safarar muyagun ƙwayoyi, haka suka tisa ƙeyarsa a gaba suka tafi da shi, sau ɗaya suka bar mu muka ganshi tun daga lokacin ba mu sake ganinsa ba, sai dai abokinsa ya zo ya faɗa mana cewar ana nan za a sako shi, amman shiru har Allah ya karɓi ransa. Bayan rasuwarsa Alhaji Mu'azu yake faɗa mana cewar babu dukiyar Mahaifinmu ko taro a hannunsa, sanadin haka muka bar garin Katsina ni da Mahaifiyata, sai muka koma garin Kaduna da zama wato mahaifarta, a gidan data gada gurin mahaifinta, tun daga lokacin garin Katsina ya fita daga raina duk da kasancewar a nan mahaifar ubana take, sai sai bayan rasuwar mahaifina babu wanda ya sake waiwayar mu a cikinsu”
Namra ta share hawaye idonta cike da tausayawa ta ce
“Ba shi na tambayeka, abunda Abdallah yayi maka na tambaye ka”
“Abdallah yasa an ɗauko ni daga garin Kaduna aka kawo ni Katsina saboda kawai yana ɗan sarauta kuma ɗan mai kuɗi yafi ƙarfin ya bar garinsa ya zo kaduna saboda ni”
“Har yanzu baka faɗa min dalilin ɗaukoa da yasa aka yi ba”
Shiru be sake ce mata komai ba, hara aka kira sallah la'asar, tasan ba zai faɗa mata ko minene a yanzu ba. Zata sake magana wayarta ta yi ƙara number Abbah ta gani cikin sauri ta yi picking.
“Gamu nan kan hanya”
Shine kawai abunda ta faɗa ta sauke wayar. Shi kuma ya tashi motar suka hau ti-ti. Ta madubin gaban mota take kallon yadda hawaye suke zuba daga idon Lamido.
Sai da suka kusa isa gida sannan ya ciro handkerchef ɗinsa ya share hawayensa. Yana faka motar ta buɗe ta fito sai shi ma ya buɗe ya fito ya miƙa mata keys ɗin motar.
“Aikina ya ƙare daga yau! Gobe zan kama hanyar garin mu”
“Ba a gurina ka karɓi keys ɗin motar ba, ba ni na ɗauke ka driving ba”
Tun da Tahir ya fara masa maganar jikinsa yayi sanyi, be san lokacin da hawaye suka zubo masa ba, lallai maso rai wawa, haƙiƙa yanzu Tahir ya lurar da shi abunda be kasa ganewa.
“Na gode”
Shine kawai abunda ya faɗa ya katse kiran. Hawaye na cigaba da masa zuba, tabbas wannan kawai ya isheshi ishara, a yanzu idan ba Mahaifiyarsa babu kowa a tare da shi, zai barwa ɗansa mumman tahirin da ba zai taɓa goguwa ba har a bada.
Kekenshi ya tura ya koma cikin falon, ƙanensa na zaune sai sha'aninsu suke ko kula da shi basu yi haka ya tura kansa ya shiga ɗakin da aka ware masa ya zamo kamar nasa. Farar takadarda da ya gani a saman gadonshi ya kai hannu ya ɗauka.
Sammaci ne daga kotun high court, ganin sunan Yasmin yasa shi murmushin da ya fi kuka ciwo, sannan ya sake tura kekena ya fito falon yana tambayar wanda ya kai masa wasiƙar.
“Ɗazu ne kana shan magani aka kawo, na shiga ban ganka ba shine na aje saman gadonka”
Ƙaramar ƙanwarsa ta faɗa. Sai kawai ya kaɗa keken ya nufi ɗakin Umma.
***
Hankalin Mai Martaba ya kwanta yanzu, har ma da na Ummi. Ganin an tsayarda magana, ranar da Mai Martaba ya aika aka yi maganar aure har da sadaka sai da yayi. Sai dai tun daga lokacin magana ta riƙa zuwa tana dawowa akan Abdallah zai auri bazawara, abun mamaki ne mutun kamar Abdallah ace zai auri bazawara kuma ɗan Sarkin Ƙatsina, wanda hakan sam be yi ma Mai Martaba daɗi ba, sai dai ya kan zuciyarsa nesa domin kawai ya farantawa ɗansa, domin yasan Annabi ma ya auri bazawara kuma yana sauranyinsa.
Ita kanta Ummi tana shan magana akan aure wasu su ce kar ta barshi wasu kuma su ce kamata yayi ya haɗa biyu. Sai dai duk wannan maganganun da ake be taɓa zuwa kunnen Abdool ba, ko da wasa ƴan'uwa da abokai basu taɓa masa wannan maganar ba, saboda sun san waye Abdool idan yana yin abu yana yi ne no matter what, ao faɗa mishi irin wannan maganar zai sa ya ɓata da kai ne kawai, ko kuma kai ma ya faɗa maka marar daɗi, sai dai abokai sun ka zolayeshi cikin wasa. Babu abunda yayi masa daɗi kamar auren da Abbah be yarda aka saka nesa ba, shi kansa da ansaka auren nesa zai roƙa a rage ne, domin ya matsu ya ɗauke Namra daga gidan. Ta ɓamgare ɗaya me yake jin zai iya zame masa matsala karatunta da take yanzu.
NAMRA POV...
Babu inda zance baikon Namra be kai ba cikin garin Sokoto da kewaye, a social media kan ba zaka iya lissafawa ba, babu abunda zai baka mamaki kamar ace bazawara ce aka yi ma wannan kayan, kuma duk da sunan an gani ana so abunda aka san budurwa ake yiwa. Kayan ƙwalah da maƙulashe ba zaka iya ƙigarsu ba, ga akwati goma da aka sako na tufafi har da zinari duk a cikin an gani ana so, kowa abunda yake faɗa to lefen me za'ayi?
Ba a gidan aka kawo kayan ba, daman haka Abbah yake duk lokacin da za a yanka ma ƴaƴansa sadaki ko a kai lefensu, gidan ƴaƴanshi yake turawa.
Ko da ake hidimar kai kayan Namra tana makaranta a lokacin duk da yake asabarce amman a ranar tana da darasin (lecture) da zata ɗauka a makaranta, bayan sun gama tayi sallama ta abokanta ta nufo gurin da tasan Lamido ya saba tsayawa ya jirata.
Ko da ta isa yana zaune cikin motar buɗewa kawai ta yi ta shiga ta zauna sai kawai taji ya ce
“Congratulations”
Tasan abunda yake nufi, yanayin muryarsa ya karantar da ita baya cikin daɗin rai.
“Na amince da auren Abdallah ne saboda mahaifina, kuma na san kai ma baka ƙi goya min baya ba wajen amincewa da hakan”
“Abdallah ya kasa ni, daman ya faɗa min zai kasa ni, ta tabba yanzu shi ne a zuciyarki ba kowa ba”
“Ya faɗa maka? Alfahari yayi, fariya yayi da zai kasa ka? Yaushe bakin ka ɗa nashi ya taɓa haɗuwa?”
Yayi ma motar key yana cigaba da magana a hankali.
“Bayan tafiyarki, abubuwa da tawa sun faru, ciki har da dalilin zuwa neman aurenki, da kuma neman zama direba a gidanku...”
Ta gyara zamanta a gidan bayan da take.
“Ban gane ba dan Allah ka ƙara min bayani, karka ɓoye min komai”
“Bayan kin bar Kaduna da kwana biyu, Yarima yasa aka ɗauko ni daga Kaduna aka kawo ni Katsina, mahaifata garin da ƙabarin ubana yake, kuma garin da nayi alƙawarin ba zan sake takawa ba.....”
Kamar wanda ya tuna abu sai kawai yayi shiru ya cigaba da driving ɗin da yake. Ita kuma gaba ɗaya natsuwarta ta bar jikinta hankalinta ya karkata kan labarin da Lamido ya fara bata...
IS BETTER THAN NONE... 😎 YI HAKURI DA SHORT CHAPTER 🙏
[7/23, 9:21 PM] Khadeeja Candy♥: *88*
“Ka tsayarda motar nan Lamido”
Ta faɗa a tsawace, umarninta yake bi tunda danta yake wannan aikin, a dole ya faka mota a gefen ti-ti, sai dai be juyo ya kelleta ba balle yace mata wani abu.
“Miyasa Abdallah ya sa aka kai Katsina? Miya ce maka? Miya faru bayan na baro Kaduna?”
“Faɗa miki abunda ya faru ba zai yi maganin komai ba”
“Wata ƙila zai yi wata ƙila kuma ba zai yi ba, amman faɗin shine mafi a'ala”
“Ni da Mahaifina asalin mu fulanin Katsina ne, mahaifiyata kuma ƴar asalin jihar kano ce, mahaifina ɗan kasuwa ne ya kan ɗauki kaya daga Katsina ya kai Kaduna idan ya siyar sai ya siyo na Kaduna ya kawo Katsina da hakan abun nasa ya girma, har ta kai ya kan ɗauka daga Katsina ya kai Nijar, a lokacin muna ƙanana, iya gata mahaifinmu ya nuna da kulawa mun taso cikin jindaɗi, arkizin mahaifinmu ya bunƙasa cikin ƙanƙanen lokaci, sai dai mahaifin mu be da amini irin Alhaji Mu'azu, ita kanta mahaifiya bata da ƙawa irin Hajiya Zuwaira, ba unguwar mu ɗaya ba, amman duk ranar weekend sai an kawo yaranta gidanmu su yi weekend, bana da wayo sosai a lokacin, amman ina jin yadda Mahaifina yake faɗin idan har ya haɗa wannan kuɗin ya tura aka turo masa kaya zai samu kuɗi sosai, haka ya tattara komai na shi ya haɗa kai da Aminsa ya tura kudaɗensa masu yawa sosai. Shiru-shiru babu kaya babu labarinsu, har ta kai mun fara shiga wani hali na ha'ila i, Alhaji Mu'azu ne yake aiko mana da cefane wani lokacin kuma har da ɗinkuna da wasu abubuwan na more rayuwa, ashe duk wannan yana masa ne a cikin kuɗin da yake binsa, wata ranar Assabar mahaifina yake labarta masa kayansa suna nan zuwa, har an kamo hanyar nigeria da su ta jirgin ruwa, haka muka ɗauki tsawon wata ɗaya muna jiran isowar jirgin, sai kawai dirar ƴan sanda muka gani a gidanmu, wai ana zarginsa da safarar muyagun ƙwayoyi, haka suka tisa ƙeyarsa a gaba suka tafi da shi, sau ɗaya suka bar mu muka ganshi tun daga lokacin ba mu sake ganinsa ba, sai dai abokinsa ya zo ya faɗa mana cewar ana nan za a sako shi, amman shiru har Allah ya karɓi ransa. Bayan rasuwarsa Alhaji Mu'azu yake faɗa mana cewar babu dukiyar Mahaifinmu ko taro a hannunsa, sanadin haka muka bar garin Katsina ni da Mahaifiyata, sai muka koma garin Kaduna da zama wato mahaifarta, a gidan data gada gurin mahaifinta, tun daga lokacin garin Katsina ya fita daga raina duk da kasancewar a nan mahaifar ubana take, sai sai bayan rasuwar mahaifina babu wanda ya sake waiwayar mu a cikinsu”
Namra ta share hawaye idonta cike da tausayawa ta ce
“Ba shi na tambayeka, abunda Abdallah yayi maka na tambaye ka”
“Abdallah yasa an ɗauko ni daga garin Kaduna aka kawo ni Katsina saboda kawai yana ɗan sarauta kuma ɗan mai kuɗi yafi ƙarfin ya bar garinsa ya zo kaduna saboda ni”
“Har yanzu baka faɗa min dalilin ɗaukoa da yasa aka yi ba”
Shiru be sake ce mata komai ba, hara aka kira sallah la'asar, tasan ba zai faɗa mata ko minene a yanzu ba. Zata sake magana wayarta ta yi ƙara number Abbah ta gani cikin sauri ta yi picking.
“Gamu nan kan hanya”
Shine kawai abunda ta faɗa ta sauke wayar. Shi kuma ya tashi motar suka hau ti-ti. Ta madubin gaban mota take kallon yadda hawaye suke zuba daga idon Lamido.
Sai da suka kusa isa gida sannan ya ciro handkerchef ɗinsa ya share hawayensa. Yana faka motar ta buɗe ta fito sai shi ma ya buɗe ya fito ya miƙa mata keys ɗin motar.
“Aikina ya ƙare daga yau! Gobe zan kama hanyar garin mu”
“Ba a gurina ka karɓi keys ɗin motar ba, ba ni na ɗauke ka driving ba”