Sashe 148
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Abbah why not ka ɗauke shi aiki a kamfanin ka, yayi degree fa, aikin ne be samu ba”
“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”
“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”
“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”
“Ni?”
Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.
“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”
“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”
“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”
“Ni gaskiya ba zani ba”
“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”
“Zan je kawai bisa Umarnin ka”
“To tashi ki saka Hijabin ki”
Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.
“Wai ko na taso muje har da ni ne?”
Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.
“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”
Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.
Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.
“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”
“Ina wuni”
Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka tausayi, gaba ɗaya ya tafi da imaninta, ya rame sosai, ga ledar fitsari an saka masa ta ƙasanshi, saboda rashin tashin da yake. A ɗayan ɓangaren kuma tana mamakin ganin Amira a ɗaki tare da iyayenta da kuma abokinsa Tahir.
“Ka tara mutane a nan kuma baka ce komai ba”
Umma ta faɗa cikin rashin daɗin rai, dan bata so ya kira Amira ba, duk da bata san dalilinsa na kiranta ba.
Ya ɗauki dogon lokaci kamin hawayen da suke masa zuba su tsagaita masa har yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya soma magana.
“Abbah zaka iya tuna wani lokaci a baya da aka ce Namra ta gudu taje gurin Asim? Ni na ɗana mata tarko tare da aminiyarta Amira, na bata sabon number da sunan zata zo ta ga Asim a bayan gidansu su gaisa, alhalin ni ne ba Asim ba, bayan na ɗauke ta sai abokaina suka canja min shawara da sunan kar na mata komai, na maidata a can, abokina ne ya faɗawa mai gadin gidana abunda zai faɗa akan ya tsince ta a bayan gidan ana ƙoƙarin yaga mata mutunci, kuma ana kiran sunan Asim... Kasan dalilin da yasa na yi mata wannan sheri? Saboda ta tona min asiri akan abunda na ke aikatawa, wato na neman maza ƴan'uwana, ba ƙarya ta faɗa ba, ta gan ni da gaske ina aikata wannan abun, amman na ƙaryata ta ne saboda ina ganin kamar asirina zai tonu ne, a lokacin, shine dalilin da yasa na ɓullo da maganar neman aurenta, sai ita kuma ta ƙi yarda, sanadin hakan da kuma gudun karta tona min asiri abokina Najib ya kai ni gurin wani boka muka mata asiri, yace sai an kawo rigarta da ita za ayi wannan asirin, sai na samu Amira na biyata na faɗa mata haka kuma ta yarda ita taje ta aro min rigarta da sunan ita zata saka muka kai akayi mata asiri da wannan rigar, daman can bokan ya faɗa mana duk lokacin da ta saka rigar idan har asirin be kamata ba to zai dawo kan mu ne, saboda Namra tana da ƙarfin addu'ah. Da asirin be kama Namra ba sai ya kama Amira, sanadin hakan ta gudu ta bar gida, ban sake jin ɗuriyarta ba, sai a lokacin da ta aiko min da wasiƙar cewar idan har ban je na kare wannan aikin ba zata iya aikata min komai. A lokacin ne Yasmin ta gani, kuma ta gano abunda ya shiga tsakanina da Adnan, wata rana ne da rana na shigo sai na tarar bata cikin gidan, sai kawai na afkawa ɗa na, daman can nafi son yi namiji, tun daga lokacin na keɓe Adnan ina jiyarsa bata gane ba, sai daga baya, sanadin hakan tace zata kai ni kotu, ni kuma na ƙaryata gaskiyarta, Washe garin ranar ne Hajiya barau ta kira ni ta faɗa min Namra ta dawo, daman ita take labarta min halin da Namra take ciki, da kuma duk wani abu dake gudana a gidan...”
Tun da ya fara maganar be tsaya ba sai da ya kai aya. Idon Abbah sun rine sun yi ja sosai, Abbah Amira ma kansa ya ɗaga sama ya maida hannayensa baya yana jinjina lamarin. Anty Amarya da Ammy kuma suna hawaye, Amira kan kasa kuka ta yi duk ta rikice jikinta sai rawa yake gumi na keto mata ta ko'ina.
“Miye dalilinka na faɗar gaskiya Uzair miyasa ba ka yi shiru da bakin ka ba? Miyasa baka ɓoye sirrinka ba kamar yadda nima na ɓoye nawa? Ban yi niyar faɗawa kowa abunda ka aikata ba Uzair, duk da rayuwar da na shiga ta fi wacce kake ciki a yanzu, dan ni nafi ƙaunar irin ciwon nan naka na san zai sadani da lahira a nan kusa, sama da jiran gawon shanu, jiran abunda babu ranar zuwansa. Ban taɓa tunanin haka ba, na yi tunanin ka haɗa kai da Namra ne ka cutar da ni ashe ni na cutar da kai na! Yanzu na fahimci dalilin da ya sa na gudu na bar gidan mu, kuma bayan na gudu ban faɗa hannun ƙwarai ba, sai na faɗa hannun ɗan fashi, ya mayarda da ni kamar matarsa, ta sanadinsa na ceci wani mutun wanda nake wa jiran gawon shanu, a familynsu na zauna, ina ganin kamar wata sabuwar rayuwa zan shimfiɗa ashe a saman wuta na yi shinfiɗar....”
Amira ta ƙarasa tana durƙushewa a gurin cikin wani irin kuka da yake jin kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ta huta. Lokuta da dama ta kan ji hakan idan ta tuna yadda Abdool ya juya mata baya, mutumen da ta fi ƙauna fiye da komai a rayuwarta, a yanzu haka bata da buri sai na shi, shiyasa ta kasa maida jikinta duk da tana tare da iyayenta.
Gaba ɗaya Namra ta ruɗe ta kasa gane komai, daga Uzair ɗin har Amira kallonsu take tana hawaye.
“Yasmin ta kasa samun fili a zuciyarta ta yafe min, saboda na yi mata sara ne a baƙin wuya, amman ke na san zaki iya yafe min, duk da kema na miki illah, amman ki dubi girman Allah ki yafe min ko Allah zai tashi ƙafaɗuna. Idan kuma har wani aikin ne Amira ta yi min dan Allah ki je ki warware shi, saboda na tsorata da kalamin da kika rubuta min cewar zaki ɗauki mataki. Ba zan iya jure zama cikin wannan rayuwar ba, ki taimaka min ki yafe min Namra...”
“Ba zata yafe maka ba, ashe kai ne silar komai, Namra ba zata yafe maka ba...!”
Abbah ya faɗa a tsawace, har sai da Namra ta kalleshi. Ya nufi ƙofa a hasale ya buɗe.
“Mamana wuce mu je”
Abban Amira yayi saurin riƙe Abbah.
“Haba ai babba baya haka, babba baya taɓa zama ƙarami, kuma tun da har yayi nadama ya kamata ka yafe masa”
Abbah ya girgiza masa kai yana ɓanɓare hannunsa daga riƙon da yayi masa.
“Sake ni Alhaji, yaron nan be kyauta min ba, babu abunda ban masa ba a rayuwa, acw ya rasa wanda zai yi ma zagon ƙasa sai ni da iyalina, wannan wane irin abu ne? Yanzu da be shiga wannan halin ba babu wanda zai san gaskiya, sai dai ayi ta zargin Namra, babu abunda ban ma yarinyar nan ba saboda shi, ashe tana kan gaskiyarta...”
Tuni Anty Amarya ta kama hannun Namra suka bar ɗakin, sannan Abbah ya rufa musu baya. Bayan fitarsu Big Bro ya kalli Amira dake taugune a gurin tana kuka ya ce
“Kinji kunya wallahi kin ci amanar ƙawarki”
Ya ƙarasa tare da jan tsaki ya juya a fusace ya bar ɗakin. Baka jin kukan kowa a ɗakin sai na Umma da Amira, dan Ammy hawaye kawai take, kamar yadda Tahir ke yi..
***
Kuka sosai Namra ta dinga yi a a motar har suka iso gida daga Anty Amarya har Abbah babu wanda ya iya buɗe baki ya furta wata kalmar balle kuma ya bata haƙuri.
Inda suka bar Lamido a gurin suka same shi zaune, Abbah be bi ta kansa ba ya wuce Anty Amarya ma haka, Namra ce ta tsaya dai-daice tana share hawayenta da Hijab ɗinta ta nuna masa wasu ɗakuna da suke can gefen gardem.
“Kaje ka zaɓi ɗaya daga cikin ɗakunan can, zan kawo maka keys ɗin ɗakin anjima...”
Gaba ɗaya hankalinsa na kanta, ya tsorata da yanayin da ya ganta saboda ya tsani zubar hawayenta.
“Allah yasa ba nine dalilin zubar wannan hawayen ba!”
“Ba kai ba ne, gaskiya ce ta yi halinta...”
“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”
“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”
“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”
“Ni?”
Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.
“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”
“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”
“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”
“Ni gaskiya ba zani ba”
“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”
“Zan je kawai bisa Umarnin ka”
“To tashi ki saka Hijabin ki”
Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.
“Wai ko na taso muje har da ni ne?”
Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.
“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”
Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.
Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.
“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”
“Ina wuni”
Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka tausayi, gaba ɗaya ya tafi da imaninta, ya rame sosai, ga ledar fitsari an saka masa ta ƙasanshi, saboda rashin tashin da yake. A ɗayan ɓangaren kuma tana mamakin ganin Amira a ɗaki tare da iyayenta da kuma abokinsa Tahir.
“Ka tara mutane a nan kuma baka ce komai ba”
Umma ta faɗa cikin rashin daɗin rai, dan bata so ya kira Amira ba, duk da bata san dalilinsa na kiranta ba.
Ya ɗauki dogon lokaci kamin hawayen da suke masa zuba su tsagaita masa har yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya soma magana.
“Abbah zaka iya tuna wani lokaci a baya da aka ce Namra ta gudu taje gurin Asim? Ni na ɗana mata tarko tare da aminiyarta Amira, na bata sabon number da sunan zata zo ta ga Asim a bayan gidansu su gaisa, alhalin ni ne ba Asim ba, bayan na ɗauke ta sai abokaina suka canja min shawara da sunan kar na mata komai, na maidata a can, abokina ne ya faɗawa mai gadin gidana abunda zai faɗa akan ya tsince ta a bayan gidan ana ƙoƙarin yaga mata mutunci, kuma ana kiran sunan Asim... Kasan dalilin da yasa na yi mata wannan sheri? Saboda ta tona min asiri akan abunda na ke aikatawa, wato na neman maza ƴan'uwana, ba ƙarya ta faɗa ba, ta gan ni da gaske ina aikata wannan abun, amman na ƙaryata ta ne saboda ina ganin kamar asirina zai tonu ne, a lokacin, shine dalilin da yasa na ɓullo da maganar neman aurenta, sai ita kuma ta ƙi yarda, sanadin hakan da kuma gudun karta tona min asiri abokina Najib ya kai ni gurin wani boka muka mata asiri, yace sai an kawo rigarta da ita za ayi wannan asirin, sai na samu Amira na biyata na faɗa mata haka kuma ta yarda ita taje ta aro min rigarta da sunan ita zata saka muka kai akayi mata asiri da wannan rigar, daman can bokan ya faɗa mana duk lokacin da ta saka rigar idan har asirin be kamata ba to zai dawo kan mu ne, saboda Namra tana da ƙarfin addu'ah. Da asirin be kama Namra ba sai ya kama Amira, sanadin hakan ta gudu ta bar gida, ban sake jin ɗuriyarta ba, sai a lokacin da ta aiko min da wasiƙar cewar idan har ban je na kare wannan aikin ba zata iya aikata min komai. A lokacin ne Yasmin ta gani, kuma ta gano abunda ya shiga tsakanina da Adnan, wata rana ne da rana na shigo sai na tarar bata cikin gidan, sai kawai na afkawa ɗa na, daman can nafi son yi namiji, tun daga lokacin na keɓe Adnan ina jiyarsa bata gane ba, sai daga baya, sanadin hakan tace zata kai ni kotu, ni kuma na ƙaryata gaskiyarta, Washe garin ranar ne Hajiya barau ta kira ni ta faɗa min Namra ta dawo, daman ita take labarta min halin da Namra take ciki, da kuma duk wani abu dake gudana a gidan...”
Tun da ya fara maganar be tsaya ba sai da ya kai aya. Idon Abbah sun rine sun yi ja sosai, Abbah Amira ma kansa ya ɗaga sama ya maida hannayensa baya yana jinjina lamarin. Anty Amarya da Ammy kuma suna hawaye, Amira kan kasa kuka ta yi duk ta rikice jikinta sai rawa yake gumi na keto mata ta ko'ina.
“Miye dalilinka na faɗar gaskiya Uzair miyasa ba ka yi shiru da bakin ka ba? Miyasa baka ɓoye sirrinka ba kamar yadda nima na ɓoye nawa? Ban yi niyar faɗawa kowa abunda ka aikata ba Uzair, duk da rayuwar da na shiga ta fi wacce kake ciki a yanzu, dan ni nafi ƙaunar irin ciwon nan naka na san zai sadani da lahira a nan kusa, sama da jiran gawon shanu, jiran abunda babu ranar zuwansa. Ban taɓa tunanin haka ba, na yi tunanin ka haɗa kai da Namra ne ka cutar da ni ashe ni na cutar da kai na! Yanzu na fahimci dalilin da ya sa na gudu na bar gidan mu, kuma bayan na gudu ban faɗa hannun ƙwarai ba, sai na faɗa hannun ɗan fashi, ya mayarda da ni kamar matarsa, ta sanadinsa na ceci wani mutun wanda nake wa jiran gawon shanu, a familynsu na zauna, ina ganin kamar wata sabuwar rayuwa zan shimfiɗa ashe a saman wuta na yi shinfiɗar....”
Amira ta ƙarasa tana durƙushewa a gurin cikin wani irin kuka da yake jin kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ta huta. Lokuta da dama ta kan ji hakan idan ta tuna yadda Abdool ya juya mata baya, mutumen da ta fi ƙauna fiye da komai a rayuwarta, a yanzu haka bata da buri sai na shi, shiyasa ta kasa maida jikinta duk da tana tare da iyayenta.
Gaba ɗaya Namra ta ruɗe ta kasa gane komai, daga Uzair ɗin har Amira kallonsu take tana hawaye.
“Yasmin ta kasa samun fili a zuciyarta ta yafe min, saboda na yi mata sara ne a baƙin wuya, amman ke na san zaki iya yafe min, duk da kema na miki illah, amman ki dubi girman Allah ki yafe min ko Allah zai tashi ƙafaɗuna. Idan kuma har wani aikin ne Amira ta yi min dan Allah ki je ki warware shi, saboda na tsorata da kalamin da kika rubuta min cewar zaki ɗauki mataki. Ba zan iya jure zama cikin wannan rayuwar ba, ki taimaka min ki yafe min Namra...”
“Ba zata yafe maka ba, ashe kai ne silar komai, Namra ba zata yafe maka ba...!”
Abbah ya faɗa a tsawace, har sai da Namra ta kalleshi. Ya nufi ƙofa a hasale ya buɗe.
“Mamana wuce mu je”
Abban Amira yayi saurin riƙe Abbah.
“Haba ai babba baya haka, babba baya taɓa zama ƙarami, kuma tun da har yayi nadama ya kamata ka yafe masa”
Abbah ya girgiza masa kai yana ɓanɓare hannunsa daga riƙon da yayi masa.
“Sake ni Alhaji, yaron nan be kyauta min ba, babu abunda ban masa ba a rayuwa, acw ya rasa wanda zai yi ma zagon ƙasa sai ni da iyalina, wannan wane irin abu ne? Yanzu da be shiga wannan halin ba babu wanda zai san gaskiya, sai dai ayi ta zargin Namra, babu abunda ban ma yarinyar nan ba saboda shi, ashe tana kan gaskiyarta...”
Tuni Anty Amarya ta kama hannun Namra suka bar ɗakin, sannan Abbah ya rufa musu baya. Bayan fitarsu Big Bro ya kalli Amira dake taugune a gurin tana kuka ya ce
“Kinji kunya wallahi kin ci amanar ƙawarki”
Ya ƙarasa tare da jan tsaki ya juya a fusace ya bar ɗakin. Baka jin kukan kowa a ɗakin sai na Umma da Amira, dan Ammy hawaye kawai take, kamar yadda Tahir ke yi..
***
Kuka sosai Namra ta dinga yi a a motar har suka iso gida daga Anty Amarya har Abbah babu wanda ya iya buɗe baki ya furta wata kalmar balle kuma ya bata haƙuri.
Inda suka bar Lamido a gurin suka same shi zaune, Abbah be bi ta kansa ba ya wuce Anty Amarya ma haka, Namra ce ta tsaya dai-daice tana share hawayenta da Hijab ɗinta ta nuna masa wasu ɗakuna da suke can gefen gardem.
“Kaje ka zaɓi ɗaya daga cikin ɗakunan can, zan kawo maka keys ɗin ɗakin anjima...”
Gaba ɗaya hankalinsa na kanta, ya tsorata da yanayin da ya ganta saboda ya tsani zubar hawayenta.
“Allah yasa ba nine dalilin zubar wannan hawayen ba!”
“Ba kai ba ne, gaskiya ce ta yi halinta...”