Sashe 43
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘i just can't believe that, taya wannan cutar zata kusance mu? Allah kar ka jarabe mu da abunda zai sa rayuwar mu data ƴaƴansu cikin damuwa’
A can cikin duniyar tunaninsa, kunnuwansa suka cinto masa wasu kalamai da Rashida take ta maimata masa.
“Ni kar ta sake fitar min da yara, kar taje ta lalata min su, kaji”
“Ba zata lalata su sai dai ta gyara tarbiyarsu, bakin ki ya daina furta mummun kalamai a kan Kalsoom, zamana take ba zaman ki, dan haka babu ruwanki da ita”
Da gautsi ya ƙarasa mata kalam, wanda har zuciyarsa haka take, dan kawai yana son ta ba zai yarda ta da aybanta masa amarya ba, dan shi ya san darajarta, kuma yasan gidan data fito.
“Ƙara ma ku haɗa kan ku dan ni ba zan ɗauki irin wannan abun ba, mu taru mu gode Allah akam kyautar da yayi mana, kuma ku yi fatar Allah ya sauke ku lafiya”
Kalamansa basa buƙatar fassara, kai tsaye ta san inda suka dosa, daman ita ta san ciki ne da ita, to Kalsoom fa ita ma cikin ne.
A take yawun bakinta suka tsinke, cikinta ya ɗauki kuka, ba ƙaranin ƙoƙari rayi ba wajen ƙawata fuskarta da murmushi, dan ta nunawa Hilal ta jidaɗin.
“Mashallah Kalsoom ita ma tana da ciki? What a blessed”
“Tana ma har ya riga na ki, bata da matsala sosai ne shiyasa ba za a gane tana da cikin ba”
Amsarsa ta tabbatar mata da zarginta, daman dalilin tambayar kenan. Wata duniyar take ƙoƙarin kai shi dan ta nuna masa farincikinta, ta kuma ɓoye masa baƙincikin da ke son bayyana a fuskarta.
Zuwana Kalsoom yasa ya daina takura akansa a kanta, duk magiyar da yake mata yake nuna mata maitarsa yanzu ya daina tun da ya samu wani halalin nasa, sai dai daren yau da raya masa shi fiye da yadda yake zato, a yau tayi masa abunda ta shekara goma bata masa ba, ta sakar masa jikinta sosai, har sai da shi kansa ya gaji dan kansa ya bar.
Tare suka yi wanka, suka ci abinci da kuma dan abun taɓawa daya siyo musu ɗazu, a lokacin ƙarfe biyun dare yayi. Suna gamawa ta kwanta dan ba gado haƙƙinsa, shi kam be kwanta ba sai yayi nafisa raka'ah biyu, raka'ar farko ya karanta fatiha da ayatul kursiyu sai ya dora kulhuwallahu sama, a raka a ta biyu kuma ya karanta fatiha da amanar rasulu ya ɗora kulhuwallahu sama, sannan ya zauna yayi zaman tahiya kamin ya sallame a cikin tahiyar ya faɗawa Allah buƙatarsa, sannan ya sallame.
Sai da yayi salatin annabi da godiya ga Allah da istigifari ƙafa ɗari ɗari sannan ya sake ɗaga hannu yayi kirari ga ubangijinsa ya nemi yafiyarsa, sannan ya sake koro da buƙatarsa.
A cikin ɗauko abun ɗibar jini ya ɗibi jininta dan yasan da safe ba zai samu damar ɗiba zata ce masa aiki.
Washe garin da zai kai yaransa makaranta suma ya ɗibi nasu, Kalsoom kam sai daf da zai fita sannan ya ɗibi nata sai raki take masa tana masa shagwaɓa, wai da zafi ita zai ƙarar mata da jini, haka ta riƙa narke masa a jiki har yayi lattin zuwa aiki.
NAMRA POV.
Kwata-kwata bachi ƙaura yayi mata daga ido, bata ma jin alamunsa balle har tasa rai zai so mata, abu ɗaya zuwa biyu yayi mata tsaye a rai, maganganun da Asim yayi shi da mahaifiyarsa, wata zuciyar na shawarta akan ta bayayyana masa ta kuma tambaye shi abunda yake ƙoƙarin ɓoye mata, yayinda ɗayar kuma take ce mata ta haƙura taga iya gudun zuwansa dan tabbatar da zarginta.
Babu amfani da raya dare da tunani bayan Ubangijinta yana kallonta, kuma yana shirye ya amsa buƙatunta, tayi haramar ƙorar sheiɗan sannan ta samu kuzarin fita tayi alwalah, sannan ta dawo ɗakin tayi nafila ta ɗora sa salatin Annabi.
Firgigit Mardiya ta farka daga dogon bachin da take a farkigice har tana ihu. Namra ma dake kusa da ita sai da ta ji tsoro kowa dake cikin ɗakin ya matsa, Mahaifiyarta ta tashi tana kallonta.
Gabanta ta fara kallo kamin ta kalli bayanta, sai kuma ta bi ko'ina na ɗakin da kallo, ajiyar zuciya ta sauke yafi ashirin, sannan ta haɗe yawun bachin da suka cika mata baki, ba dan tasan tayi ba.
“Ke lafiyarki?”
Ashe dai duniya take, jin muryar mahaifiyarta ya ƙara tabbatar mata da a farke take.
“Wallahi wani mumunan mafarki na yi, wai wuta tana bina”
“Subhanallahi, ke kuwa ai addu'ah zaki yi”
Namra ta faɗa, tana rufe ƙur'anen dake hannunta, sannan ta nufi gurin bachinta tayi addu'ah bachi ta kwanta ba dan tana jin bachin ba, sai dan tana buƙatar jinginar da jikinta da tabar suka saba mata shimfiɗa da ita.
Washe gari...
Da sassafe ta siye tea da buroɗi ta nufi asibiti, dan bata son su Mama su kama hanya bata isa ba, tun da babu wanda zai kula da Asim sai ita. Duk yadda take ganin ta doka sammako sai taga har sun fi ta, dan tana shiga ɗakin taga alamar sun kama hanya.
Bata yarda ta nunawa Asim komai ba, ta gaisheshi sannan ta masa ya jiki ta soma zuba masa tea ɗin.
“Jiya kika tafi baki faɗa ba”
“Eh pad ɗina ne ya lalace shine naje gida na canja, su Mama sun kama hanya ko?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yanzu kam hankalinsa ya kwanta, daman can yana tunanin ko ta ji maganar sune yasa taje ba tare data faɗa musu ba, ashe shi da Mama ba su canka dai-dai.
“Eh tace da wuri zata je yadda zata tararda matar da za a ranto kuɗin gareta”
“Allah yasa a dace”
Ta faɗa tana miƙa masa tea, kallon da tayi masa da kuma maganarsa sun zari zuciyarta, miyasa Asim yake ɓoye mata? Wani tunanin ne ya zo mata sai ta kawar da fuskarta gefe.
_______________________________
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 33*
NOT EDITED ⚠️
Washe garin ranar da Mama ta tafi ta dawo, guraren uku da rabi na rana. Ita kaɗai ta dawo ba tare da Hajara ba, Namra bata nuna mata komai ba ta tarbeta da far'ah tana mata sannu da zuwa.
Tana son tayi labari Namra ta tsare su taƙi ta tashi, shi kansa Asim yana son magana da ita amman ba dama, tun da Namra tana gurin.
Kamar ta san Namra bata tanadar mata komai, tun a hanya ta tayi gurin biredin ta da lemu, sai ta ta ci ta ƙoshi, sannan ta tashi ta fita.
Da kanta taje ta biya kuɗin maganin dan kar taba Namra.
Ta dawo daga biyan maganin ne, Namra ta tashi tayi musu sallama ta baro asibitin.
Har ta iso gida kuka take, tana tunanin yadda Asim yake ɓoye mata lamarin, dan ta lura da yadda suke kallon kallo da Mama, hakan ya soma tabbatar mata da abunda Anty Amarya ke faɗa mata.
“Idan har ta tabbata Asim na son yaudarata....”
Sai kuma tayi shiru ta share hawayenta, ta miƙawa mai Napep kuɗinsa ta shige gida.
*** ***
“Thank you”
Ta faɗa tana murmushi tare da kallon mutumen daya tashi daga saman kujerar ta ya nufi ƙofar fita. Sai da ya fice sannan ta kalli wayarta dake ringing, sannan ta kai hannu ta ɗauka zuciyarta na raya mata irin labarin da Asmee zata bata.
“Ƴar gari kamar kin san yanzu nake tunanin ki nace ko kin samu zuwan kuwa?”
Kuka ta fara ji kamin Asmee ta ɗora mata da zancen dalilin kiran nata.
“Rashida ina ciki matsala”
“Lafiya miya faru?”
“Wani malami ne da muke zuwa gurinsa, yana ba mu taimako, shine yanzu ake ce mana malamin yana da ciwon nan na zamani, shine tun ranar na kasa sukuni ban ma sama naje gurin matsalar ki ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Asmee garin yaya? Ya taɓa sex dake ne? Ko me?”
Kuka tayi sosai har ka kasa magana.
“Ki faɗa min mana ki daina kuka”
“Ya taɓa lokacin da je neman wani taimako sai yace min sai na kawo sperm ɗin wani wanda ba mijina ba, da jinin al'ada da shi za a haɗa, ni kuma na ce masa ban san inda zan samo ba, shine....”
Ta ƙarasa da kuka
“Ke yanzu kin je an gwada jinin ki ance kina ɗauke da ciwon ne? Stop crying and tell me Asmee”
“Ban je ba, tsoro nake ji ban san wanda zan faɗawa ba sai, dan bani da ƙawa irin ki, na rasa yadda zan yi tsoron gwajin na ke, aiki ma na daina zuwa yanzu”
“Innalillahi Ya salam Ya salam”
Ta soma zagaye office ɗin tana dafe kai, da wayar a kunnenta.
“Ki kwantar da hankalin ki kinji karki faɗawa kowa, kuma karki yi abunda zai sa mijin ki ko wani ya zargi wani abu, i will call you back”
Tayi saurin kashe wayar tana tuna jininta da Hilal ya ɗiba, idai har Asmee ta kamu da cutar to itama zata iya kamuwa da ita tun da har suna using mutum ɗaya.
Faɗuwa tayi zaune zumi na keto mata ta ko'ina, hannu ta kai tana shafa kanta, tana girgiza shi kamar wani ne a gabanta.
“Ko shiyasa ya sake ɗibar jinina? Amman kuma ai da ba zai kusance ni ba, amman yanzu idan ya auna dole ya gano idan akwai shi”
A fili take furucin zuciyarta a karaye, jikinta har tsimi yake, yanzu kam hannaye biyu tasa ta dafe kanta tana tunanoma kanta mafita.
“Dole ne na dakatar dashi daga yin gwajin, kuma dole ne nima naje na bincika kai na, indai har da gaske ne Asmee kin cuce ni”
Da sauri ta tashi ta kaɗe jikinta ta fiddo hoda a jakarta ta gyara fuskarta sannan ta ɗauki jakar ta fita. Sai da ta biya ta faɗa musu fitar gaggauwa ta kamata, sannan ta fito harabar bankin ta shiga motar, ta ɗauki hanyar Asibiti.
Akwai ƴar tazara tsakaninta da asibitin, amman yadda ta sakarwa motar wuta yasa ta isa cikin ƙanƙanen lokaci. A harabar asibitin tayi parking, ta fito ta duba gurin da aka tanadarwa manyan likitoci dan faka motocinsu.
A can cikin duniyar tunaninsa, kunnuwansa suka cinto masa wasu kalamai da Rashida take ta maimata masa.
“Ni kar ta sake fitar min da yara, kar taje ta lalata min su, kaji”
“Ba zata lalata su sai dai ta gyara tarbiyarsu, bakin ki ya daina furta mummun kalamai a kan Kalsoom, zamana take ba zaman ki, dan haka babu ruwanki da ita”
Da gautsi ya ƙarasa mata kalam, wanda har zuciyarsa haka take, dan kawai yana son ta ba zai yarda ta da aybanta masa amarya ba, dan shi ya san darajarta, kuma yasan gidan data fito.
“Ƙara ma ku haɗa kan ku dan ni ba zan ɗauki irin wannan abun ba, mu taru mu gode Allah akam kyautar da yayi mana, kuma ku yi fatar Allah ya sauke ku lafiya”
Kalamansa basa buƙatar fassara, kai tsaye ta san inda suka dosa, daman ita ta san ciki ne da ita, to Kalsoom fa ita ma cikin ne.
A take yawun bakinta suka tsinke, cikinta ya ɗauki kuka, ba ƙaranin ƙoƙari rayi ba wajen ƙawata fuskarta da murmushi, dan ta nunawa Hilal ta jidaɗin.
“Mashallah Kalsoom ita ma tana da ciki? What a blessed”
“Tana ma har ya riga na ki, bata da matsala sosai ne shiyasa ba za a gane tana da cikin ba”
Amsarsa ta tabbatar mata da zarginta, daman dalilin tambayar kenan. Wata duniyar take ƙoƙarin kai shi dan ta nuna masa farincikinta, ta kuma ɓoye masa baƙincikin da ke son bayyana a fuskarta.
Zuwana Kalsoom yasa ya daina takura akansa a kanta, duk magiyar da yake mata yake nuna mata maitarsa yanzu ya daina tun da ya samu wani halalin nasa, sai dai daren yau da raya masa shi fiye da yadda yake zato, a yau tayi masa abunda ta shekara goma bata masa ba, ta sakar masa jikinta sosai, har sai da shi kansa ya gaji dan kansa ya bar.
Tare suka yi wanka, suka ci abinci da kuma dan abun taɓawa daya siyo musu ɗazu, a lokacin ƙarfe biyun dare yayi. Suna gamawa ta kwanta dan ba gado haƙƙinsa, shi kam be kwanta ba sai yayi nafisa raka'ah biyu, raka'ar farko ya karanta fatiha da ayatul kursiyu sai ya dora kulhuwallahu sama, a raka a ta biyu kuma ya karanta fatiha da amanar rasulu ya ɗora kulhuwallahu sama, sannan ya zauna yayi zaman tahiya kamin ya sallame a cikin tahiyar ya faɗawa Allah buƙatarsa, sannan ya sallame.
Sai da yayi salatin annabi da godiya ga Allah da istigifari ƙafa ɗari ɗari sannan ya sake ɗaga hannu yayi kirari ga ubangijinsa ya nemi yafiyarsa, sannan ya sake koro da buƙatarsa.
A cikin ɗauko abun ɗibar jini ya ɗibi jininta dan yasan da safe ba zai samu damar ɗiba zata ce masa aiki.
Washe garin da zai kai yaransa makaranta suma ya ɗibi nasu, Kalsoom kam sai daf da zai fita sannan ya ɗibi nata sai raki take masa tana masa shagwaɓa, wai da zafi ita zai ƙarar mata da jini, haka ta riƙa narke masa a jiki har yayi lattin zuwa aiki.
NAMRA POV.
Kwata-kwata bachi ƙaura yayi mata daga ido, bata ma jin alamunsa balle har tasa rai zai so mata, abu ɗaya zuwa biyu yayi mata tsaye a rai, maganganun da Asim yayi shi da mahaifiyarsa, wata zuciyar na shawarta akan ta bayayyana masa ta kuma tambaye shi abunda yake ƙoƙarin ɓoye mata, yayinda ɗayar kuma take ce mata ta haƙura taga iya gudun zuwansa dan tabbatar da zarginta.
Babu amfani da raya dare da tunani bayan Ubangijinta yana kallonta, kuma yana shirye ya amsa buƙatunta, tayi haramar ƙorar sheiɗan sannan ta samu kuzarin fita tayi alwalah, sannan ta dawo ɗakin tayi nafila ta ɗora sa salatin Annabi.
Firgigit Mardiya ta farka daga dogon bachin da take a farkigice har tana ihu. Namra ma dake kusa da ita sai da ta ji tsoro kowa dake cikin ɗakin ya matsa, Mahaifiyarta ta tashi tana kallonta.
Gabanta ta fara kallo kamin ta kalli bayanta, sai kuma ta bi ko'ina na ɗakin da kallo, ajiyar zuciya ta sauke yafi ashirin, sannan ta haɗe yawun bachin da suka cika mata baki, ba dan tasan tayi ba.
“Ke lafiyarki?”
Ashe dai duniya take, jin muryar mahaifiyarta ya ƙara tabbatar mata da a farke take.
“Wallahi wani mumunan mafarki na yi, wai wuta tana bina”
“Subhanallahi, ke kuwa ai addu'ah zaki yi”
Namra ta faɗa, tana rufe ƙur'anen dake hannunta, sannan ta nufi gurin bachinta tayi addu'ah bachi ta kwanta ba dan tana jin bachin ba, sai dan tana buƙatar jinginar da jikinta da tabar suka saba mata shimfiɗa da ita.
Washe gari...
Da sassafe ta siye tea da buroɗi ta nufi asibiti, dan bata son su Mama su kama hanya bata isa ba, tun da babu wanda zai kula da Asim sai ita. Duk yadda take ganin ta doka sammako sai taga har sun fi ta, dan tana shiga ɗakin taga alamar sun kama hanya.
Bata yarda ta nunawa Asim komai ba, ta gaisheshi sannan ta masa ya jiki ta soma zuba masa tea ɗin.
“Jiya kika tafi baki faɗa ba”
“Eh pad ɗina ne ya lalace shine naje gida na canja, su Mama sun kama hanya ko?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yanzu kam hankalinsa ya kwanta, daman can yana tunanin ko ta ji maganar sune yasa taje ba tare data faɗa musu ba, ashe shi da Mama ba su canka dai-dai.
“Eh tace da wuri zata je yadda zata tararda matar da za a ranto kuɗin gareta”
“Allah yasa a dace”
Ta faɗa tana miƙa masa tea, kallon da tayi masa da kuma maganarsa sun zari zuciyarta, miyasa Asim yake ɓoye mata? Wani tunanin ne ya zo mata sai ta kawar da fuskarta gefe.
_______________________________
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 33*
NOT EDITED ⚠️
Washe garin ranar da Mama ta tafi ta dawo, guraren uku da rabi na rana. Ita kaɗai ta dawo ba tare da Hajara ba, Namra bata nuna mata komai ba ta tarbeta da far'ah tana mata sannu da zuwa.
Tana son tayi labari Namra ta tsare su taƙi ta tashi, shi kansa Asim yana son magana da ita amman ba dama, tun da Namra tana gurin.
Kamar ta san Namra bata tanadar mata komai, tun a hanya ta tayi gurin biredin ta da lemu, sai ta ta ci ta ƙoshi, sannan ta tashi ta fita.
Da kanta taje ta biya kuɗin maganin dan kar taba Namra.
Ta dawo daga biyan maganin ne, Namra ta tashi tayi musu sallama ta baro asibitin.
Har ta iso gida kuka take, tana tunanin yadda Asim yake ɓoye mata lamarin, dan ta lura da yadda suke kallon kallo da Mama, hakan ya soma tabbatar mata da abunda Anty Amarya ke faɗa mata.
“Idan har ta tabbata Asim na son yaudarata....”
Sai kuma tayi shiru ta share hawayenta, ta miƙawa mai Napep kuɗinsa ta shige gida.
*** ***
“Thank you”
Ta faɗa tana murmushi tare da kallon mutumen daya tashi daga saman kujerar ta ya nufi ƙofar fita. Sai da ya fice sannan ta kalli wayarta dake ringing, sannan ta kai hannu ta ɗauka zuciyarta na raya mata irin labarin da Asmee zata bata.
“Ƴar gari kamar kin san yanzu nake tunanin ki nace ko kin samu zuwan kuwa?”
Kuka ta fara ji kamin Asmee ta ɗora mata da zancen dalilin kiran nata.
“Rashida ina ciki matsala”
“Lafiya miya faru?”
“Wani malami ne da muke zuwa gurinsa, yana ba mu taimako, shine yanzu ake ce mana malamin yana da ciwon nan na zamani, shine tun ranar na kasa sukuni ban ma sama naje gurin matsalar ki ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Asmee garin yaya? Ya taɓa sex dake ne? Ko me?”
Kuka tayi sosai har ka kasa magana.
“Ki faɗa min mana ki daina kuka”
“Ya taɓa lokacin da je neman wani taimako sai yace min sai na kawo sperm ɗin wani wanda ba mijina ba, da jinin al'ada da shi za a haɗa, ni kuma na ce masa ban san inda zan samo ba, shine....”
Ta ƙarasa da kuka
“Ke yanzu kin je an gwada jinin ki ance kina ɗauke da ciwon ne? Stop crying and tell me Asmee”
“Ban je ba, tsoro nake ji ban san wanda zan faɗawa ba sai, dan bani da ƙawa irin ki, na rasa yadda zan yi tsoron gwajin na ke, aiki ma na daina zuwa yanzu”
“Innalillahi Ya salam Ya salam”
Ta soma zagaye office ɗin tana dafe kai, da wayar a kunnenta.
“Ki kwantar da hankalin ki kinji karki faɗawa kowa, kuma karki yi abunda zai sa mijin ki ko wani ya zargi wani abu, i will call you back”
Tayi saurin kashe wayar tana tuna jininta da Hilal ya ɗiba, idai har Asmee ta kamu da cutar to itama zata iya kamuwa da ita tun da har suna using mutum ɗaya.
Faɗuwa tayi zaune zumi na keto mata ta ko'ina, hannu ta kai tana shafa kanta, tana girgiza shi kamar wani ne a gabanta.
“Ko shiyasa ya sake ɗibar jinina? Amman kuma ai da ba zai kusance ni ba, amman yanzu idan ya auna dole ya gano idan akwai shi”
A fili take furucin zuciyarta a karaye, jikinta har tsimi yake, yanzu kam hannaye biyu tasa ta dafe kanta tana tunanoma kanta mafita.
“Dole ne na dakatar dashi daga yin gwajin, kuma dole ne nima naje na bincika kai na, indai har da gaske ne Asmee kin cuce ni”
Da sauri ta tashi ta kaɗe jikinta ta fiddo hoda a jakarta ta gyara fuskarta sannan ta ɗauki jakar ta fita. Sai da ta biya ta faɗa musu fitar gaggauwa ta kamata, sannan ta fito harabar bankin ta shiga motar, ta ɗauki hanyar Asibiti.
Akwai ƴar tazara tsakaninta da asibitin, amman yadda ta sakarwa motar wuta yasa ta isa cikin ƙanƙanen lokaci. A harabar asibitin tayi parking, ta fito ta duba gurin da aka tanadarwa manyan likitoci dan faka motocinsu.