← Book details Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 173

Sashe 45

Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Banki ta dawo zuciyarta cike da tunani kala-kala, masu sokanar tama ganinta da rigar likita, dariya kawai take musu ba dan ta kula da zancen su ba. Ta shiga office ɗinta sai zama ya gagareta, ga takardun data tarar an kawo ma tayi sigh ko kallonsu ba tayi ba. Ta juya ta fita, office ɗin Alhaji Bashir ta nufa. Bata nemi izinin shiga ba ta tura office ɗin ta shiga.

Hannunta ta miƙa masa kamar yadda ta saba yayi mata kiss, sannan ya zauna saman teburin ta ɗora sama ƙafarta ɗaya saman ciyarsa tana masa wani irin abu, kamar wata gwaggwazajiyar karuwa.

“Security Camera, dai a kashe take?”

“Ai nasa an cire min ita tuni saboda ke”

Ta ƙara matsarda ƙafarta, izuwa cikinsa.

“Bashir akwai wanda ka sani a Alex Hospital, ɓangaren Lab?”

Hannu ya kai ya naɗe wandon suit ɗin nata, ya fara shafa ƙafarta.

“Ba za a rasa wanda na sani ba, miya faru ne?”

Shiru ta ɗanyi tana tunani, idan har ta yarda ta faɗa masa, asirinta zai tono, tun da dole ne yayi ma matarsa magana, wata ƙila ma ya sake ta.

“Wallahi wata friend ɗita ce za'ayi ma gwajin kasan asibitin sun fi ƙwarewa, sama data su Hilal”

Ya ɗauko wayarsa yana wani lumshe ido

“Bari na kira Doc Sabo sashen jini yake aiki”

Ta sauka daga saman teburin ta dawo saman cinyoyinsa.

“Kar wani ya shigo fa”

“Babu wanda zai shigo sai ya nemi izini”

Sai da suka gaisa da likitan sannan ya haɗa shi da Rashida. Gaisawa kawai tayi da shi sannan ta sanar masa zata karɓi number sa, su yi magana.

Sai da ta saka number a wayarsa sannan ta sauka daga saman jikinsa, daman tayi samana hakan ne dan kar ya gano damuwarta tun da ta saba masa a duk lokacin data shigo office ɗin.
Duk da irin kibar da yake da ita bata hanashi saurin unƙurawa ba ya riƙo hannunta ganin zata wuce.

“Yau da wuri zamu tashi babu aiki da yawa”

“Eh amman zan je gida akwai abunda zan yi”

“Aiko dai yau na so mu haɗu”

“Gaskiya akwai abunda zan yi, yanzu fa haɗuwar mu zata riƙa wuya, ƙara kaje gurin matar kawai”

Bata tsaya jiran abunda zai ƙara cewa ba ta fice daga office ɗin.
Lokacin data dawo office ɗinta zaunawa tayi ta ƙare duka aikin dake gabanta, sannan ta ɗauki wayarta ta kira likitan. Bayan sun gaisa ta gabatar masa da kanta.

“Sunana Aisha bee Omar, akwai wani cousin ɗina dake fama da matsala sai yaje asibiti aka bashi gwajin jini, to ina son idan ya kawo ka min a yi masa a kira ni a sanar dani dan Allah”

“Amman miyasa Hajiya?”

“Idan ka kawo ka sanar min zan faɗa maka ko minene, ka turo min account number ɗin ka”

“A wannan Asibitin bama yin abunda ya tsaɓa doka, hakan kan iya ja mana ɓacin suna a asibitin nan”

“Ba taka doka zaka yi ba, ceton rai ne idan har ya kawo ka faɗa min dan Allah”

“Miye sunan shi?”

“Sunan shi Hilal”

“Okay”

“Karka Manta ka turo min account number ɗin”

“Alright”

Yana kashe wayar ya turo mata account number ɗin. Ta jidaɗin ganin number, ga dukan alama zai yi saurin bata haɗin kai, jiki na rawa ta tashi ta fita daga office ɗinta, ta je ta cikin bankin ta masa transfer 100k.

NAMRA POV.

Yau ba laifi ta samu bachi dare, duk da ba mai nauyi bane sosai, minti goma ashirin zuwa ashirin da biyar take farkawa.
Sai dai a duk farkawar da take, a zaune take ganin Mardiya tana kallonta kamar wata mayya, tun Namra tana dauriya ta koma bachi har ta gaji ta tambaye dalilin rashin bachin nata.

“Wallahi na kasa bachin ne mafarkin tsoro nake, kusan kwana biyu yanzu haka na ke”

“Kiyi addu'ah kawai ki kwanta, babu abunda zai same ki, ki karanta Ayatul kursiyu ƙafa uku ko wace da bismillah wallahi har garin Allah ya waye babu abunda zai same ki”

“Toh na gode zan gwada”

Ta faɗa da damuwar a muryarta. Komawa Namra tayi ta kwanta ba ita ta fake farkawa ba sai asuba.
A kulolin gidan ta ɗauka ta zuba musu ɗumamen tuwo da Maman Mardiya tayi, sannan tayi wanka ta ɗauka ta nufi asibitin.

Ko da ta isa ta tarar har sun siye tea a bakin asibitin sun karya. Mama bata wani sake da Namra sun gaisa ba, ciki-ciki ta amsa masa gaisuwarta, ta fice tama watsa mata wani kallo a kaikaice kamar wata kishiryarta.
Hakan be dame Namra ba, dan ita ta san muhalin data aje ta a yanzu, tun da ta fara fahimtar tafiyarsu.
Bayan kamar minti talatin da fitar Mama Asim ya ɗauko dubu goma sha biyar ya miƙa ma Namra.

“Ga wannan ki siye wasu abubuwan na gida, Mama zata siyo katifa da wasu kayan”

Namra ta jidaɗi sosai, daman zama gidan su Mardiya ya fara isarta, duk da tasan kuɗin ba zasu isheta hakan be hanata nuna farincikinta ba.

“An biya kuɗin maganin ne har wasu sun rage?”

“Eh ɗari biyu matar ta ara mana, Allah dai ya ba ni ikon biya”

“Amin, amman Asim shabiyar zasu isa siyayya kuwa? Ba mu da komai fa kasan komai ya ƙone”

“Haka nan za a matsa ayi Namra, bafa irin siyayar gidan ku zaki yi ba, ta talakawa zaki yi, kamin mu ga abunda Allah zai yi kuma”

“Toh Allah ya taimaka”

“Amin, likitan yayi min allurar ɗaya ɗazu, kuma yace ya kamata na ɗan fara taka ƙafar, koda ina riƙa wani abun ne”

“Aiko ya kamata ka fara tun yanzu”

“A'a sai nan gaba, gaskiya ni tsoro nake ji”

Ta ɗanyi dariya, tana mamakin irin rakin da Asim yake da shi. Asibitin ta wuni sai da yamma ta koma da zimmar taje Mardiya ta raka ta kasuwa suyi siyayya. Bayan tafiyarta Mama ta siyo abinci a bakin asibiti ta ci, ta kawo mo Asim, dan kwata-kwata ƙwara tayi daga ɗakin har sai da Namra ta tafiyarta, sannan ta dawo, Mama irin mutanen nan ne da basu iya samun arziki ba, waɗanda idan abu ya same su a take suke canjawa mutum, ga shegen son su yi kuɗi kamar hauka, tana daga cikin mutanen da suka tsani masu arziki, suna ganin kamar Allah ya fi son su da su, ita a nata rayuwar bata ƙi Asim yayi arziki ba ta kowa ne hali, ko dan ya rama abunda iyayen Namra suka masa.

ABDOOL POV.

A hankali yake tsotsa bakinsa kamar mai shan minti, sai wasa yake da drink ɗin dake gabansa ya kasa sha.

“Saboda Mai Martaba yace yana son ganin ka shiyasa ka wani damu ko?”

Ya ɗan ɗaga kai kaɗan ya kalli Ummi da idonsa na marar gaskiya.

“Eh mana, na san ba zai wuce yayi min maganar aure ba”

“Ai dole yayi maka maganar aure, tun da kai baka san ka girma ba, ace ko wace mace baka so, kwana ki har ƙaryar ciwo kayi min sai gashi likitan ya ƙarya ta ka, wai anya ba aljana take auren ka ba?”

Yayi dariya yana kallon ƙannensa mata su huɗu da suke zaune a ɗayan ɓangaren na falo suna sha'aninsu.

“Abdool ya kamata ace kana yi ma kan ka faɗa, mahaifin ka yana son ka, kar kayi abunda zai sa kyaunka ya ɓace a gare shi, kasan ƴan da matan uban nan naka suke, basun ka suke su kuma zuga shi zasu yi ta yi har sai sun ga taren ku ya ɓace, duk kuma wanda bashi da uwa a cikin gida yana cikin matsala dole ne yayi taka tsantsan”

Ya shafa kansa, yana jingina da kujerar dinning ɗin.

“Ummi Mai Martaba na da wani buri akai na, shiyasa ya natsa nayi aure, ni kuma bana son sarautar nan, ni kwata-kwata ma ba dan shi ba Wallahi da ba zan zauna ƙasar nan ba”

“Amman ai ba kai kaɗai ya haifa Namiji ba, amman kai ne mafi soyuwa a ransa, to dan me ba zakayi masa abunda zai sa ya ƙara son ka ba? Indai baka fitar da wanda kake so ba sai ya kai ga ɗaukar wata a cikin gidan nan ya haɗa ku, idan kuma ka ƙi yarda kasan abunda zai biyo baya”

“Ummi wanda nake so ban san inda zan ganta ba, ban san yadda za'ayi na haɗu da ita ba”

“Kamar ya?”

Ta tambaya tana kai ƙwallon anabi a bakinta.

“A Funtua na ganta bakin wani pharmacy, na fita nayi mata magana, tace min matar aure ce ita”

“Ta faɗa maka ita matar aure ce kuma zaka so ta?”

“Sam bata min kama da matar aure ba mai igiya uku, sai da matar aure kalar aure, ina ganin wannan take nufi, irin ƴan matan nan ne masu aji sosai, har marina tayi fa”

Ummi ta gyara zamanta, irin na mutanen nan da naira ta zauna a jikinsu har ta nuna kanta, ga kuma milkin dake cikin jininta, na ƴaƴan sarakai.

“Wayw Uban ta a garin nan?”

“Wallahi nima ban sani ba, irin yaran nan masu mugun ji da kan su, kuma na rasa yadda zan yi na same ta, duk wata hanya da zata sadani da sake ganin ta nabi amman ba nasara, har abinci naje na raba a inda ake sa ran zan ganta amman ban ganta ba, kuma ni Wallahi ita nake so”

“To sai yaya kenan?”

“Sai na nemota duk inda na ganta zan gane ta, ba zata min marin banza ba sai na rama, kuma gaskiya ba zan haɗu da ita hakan nan ba ga dukan alamun ita ce, dukan matan da nake haɗuwa da su ban ji komai akan su ba sai ita”

Ya faɗa yana mai tashi tsaye.

“Anya ba aljana ka haɗu da ita ba Abdool?”

“Ba aljana bace Ummi”

A faɗa yana dariya, zuwa yayi ya mata side hug, ya ɗauki anabi ɗaya ya kai a bakinsa, na biyu kuma ya jefe ƙannensa da shi.

“Ummi ki tsara min yadda zan cewa Mai Martaba”

Be tsaya jiran abunda zata ce ba, ya fice daga falon yana murmushi. Da kallo Ummi ta bishi tana mamakin yadda ɗan nata yake ƙoƙarin zame mata aljani.

ANTY AMARYA POV.
Chapter 45 · 0% Book details