Sashe 94
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka ta taso ta fito daga falon da ƙahon baƙinciki daya tsaya mata a zuciya. Part ɗinta ta shigo tana shiga ta shige ɗakinta ta zauna, babu abunda take tunanu sai duniyar da Abbah xai kashe masu gurin auren, kamar ita ba a ma ƴaƴanta.
Ummi ce ta shigo ƴar gurin Hajiya Barau mai sunan mahaifiyarta hakan yasa take kiranta da Ummi.
Duk cikin ƴaƴanta mata ita kaɗaice tazo tarbon lefen. Kusa da mahaifiyarta ta xauna tana kallon yanayinta kallonta Hajiya Barau tayi
“Kin gani ke kina son kashe na ki aure su kuma suna yi, idan so kike ki dawo gida mu zauna sai ki dawo”
“Haba Hajiya wallahi ni na gaji da irin wannan rayuwar da yake nuna min, kwata kwata bana gabansa, baya da aiki sai neman mata, tun abu na ɓoye har magana ta fara fita, ko fita nayi sai ya kawo wata a gida”
“Ina ruwanki da neman matansa? Ai kedai yana baki ci da sha ko yana baki na kashewa ina ruwan ki da lamarin, yanzu neman maza ma ake balle mata, abun ai yyi ne wanda be yi ba to bashi da kuɗin yin ne, ko ni ya nema kya ce ki kashe auren ki ki dawo gida balle kuma wata can daban”
Miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai ta fice, dan tasan duk yadda take son mahaifiyarta ta fahimci matsalarta ba fahimta zata yi ba.
Ƙwafa Hajiya Barau tayi taja wayarta tana soma labartawa abokin gulmarta rashin zuwan Namra tarbar lefen ƙannenta.
Duk hirar da suke be nuna mata jindaɗin hakan ko rashin jindaɗin saboda yana gaban Yasmin ne, yawancin maganar bata wuce uhn a'a ato, Har suka gama wayar.
Ƙaton cikin Yasmin ya kalla yana murmushi.
“Allah yasa karki haifa minɓɗa mai kahuwa”
Ta tsuke baki
“Mai hali dai baya fasa halinsa, ni wallahi haushi kake bani sosai”
“Daman duk kina da ciki ai baki ƙaunata kamar na kashe miki wani”
Ya faɗa yana jawo wayarsa da tayi ringing, number abokinsa Tahir ya gani.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Shine abunda ya furta bayan ƴan daƙiƙu da karɓa wayar.
“Okay gani nan zuwa”
Ya tashi tsaye da sauri, har Yasmin ta kalleshi
“Lafiya?”
“Wai Najeeb yayi hatsari, nan cikin gari”
“Subhanallahi, ina fatar be ji ciwo ba”
“Ban sani ba, sai naje tukunan”
Da sauri ya ɗauke Adnan da ke saman jikinsa ya ɗauki wayoyinsa ya zuba aljihu tare da keys ya fice hankali tashe.
*HILAL POV*
Lallaɓata yayi har sai da tayi shiru sannan yaja ta zuwa saman gadonsa ya zaunar da ita ya kama hannayenta ya riƙa.
“Na yarda ba ki aikata ba shikenan?”
“Har zuciyarka ka yarda da ni?”
“Na yarda da ke?”
“Zaka daina fushi da ni?”
“Zan daina”
“Zaka dawo da su Ezzah”
“Idan Hajiya ta yarda”
Haka yake ta amsa mata kamar tambayar babba da yaro, sai ya hau saman gadon yaja ta ƙirjinsa ya rumgume.
“I Love You”
Ƙamkamshi tayi
“I love you too”
Sun daɗe a haka kamin ya sake ta ya shiga yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sai ta ɗauko masa abinci. Ba dan yana so ba ya zauna yayi ƴan lomomi kaɗan ya tashi ya nufi gidan Hajiyarsa.
Da shigarsa Ezzah da Ulfah da sauran yaran gidan suka rugo da gudu suka tarbeshi. Ulfah ce kawai ta tambayi Kalsoom Ezzah kan ko a jikinta. Bayan ya gama ganinsu ya miƙa musu chocolates ɗin ya shigo da shi sannan ya wuce gurin Hajiyarsa.
Tun daga yanayin yadda ta amsa masa sallamarsa yasan akwai abunda ya faru. Guri ya samu ya zauna yana kallon tv dake ɗakinta, kamin daga bisani ya gaishe ta. A maimakon ta amsa sai kawai ta hau shi da faɗa
“Yanzu fisabilliahi abunda kake ƙoƙarin yi kyautawa ne? Kace xaka kare ta idan kun je kutu bayan ga abunda tayi ma ɗan ka, irin waɗannan matan fa zama da du matsala ne dan kai ma xata iya maka haka”
Daga yanayin maganar ta ya gane Amina ce ta kawo mata zancen, dan ita kaɗai yasan yayi zancen a gabanta sai kuma Alh Bashir.
“Amman Amina munafukace wallahi, zuwa tayi ta faɗa miki ko?”
“Ai dole ta faɗa min mana tun da abun yayi mata zafi, ni kama rabu da wannan matar ka nemi wata ka aura”
“Gaskiya ba zan iya rabuwa da ita ba”
“To ko zaka auro wacce zata riƙa maka ƴaƴanka, dole ne ka ƙara aure ko kuma ka rabu da ita idan baka shirya zama da mata biyu ba”
“Haba Hajiya, kuskure ne nima a yanzu na gane ba ita ce ta aikata ba”
“To waya aikata? Ga abu ƙiri da muzu ka nemi takewa dan kana son ta, ah lallai ba banza ta barka ba, Ezzah ma tana ta faɗar irin abunda take musu a gidan, cin amana zalla”
Dariya abun ya bashi yau kuma Hajiya da kanta take irin wannan furucin.
“Babu maganin komai Hajiya, amman wannan matsalar nima ban san kan ta ba”
“To ni dai na faɗa maka ko ka ƙara aure ko ka rabu da ita, tashi ka bani guri”
Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya
“Hajiya ki fahimta...”
“Ba zan fahimta ba, ka tafiyarka kawai”
Yasan duk yadda zai yi ba zata fahimta sai kawai ya tashi ya fice da jimmar idan ta huce zai dawo ya fahimtar da ita.
-----------------------------------------------------------------
*Jiya naje biki ban samu na yi typing ba, so wannan zai zama na jiya, na yau kuma sai dare zan kawo. Thank you 🖤*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *60 - NOT EDITED ⚠️*
*RASHIDA POV.*
“Teema ya faɗa min abinda ya fi ƙarfin zuciyata da tunani, ya bani labarin yau da kuma gobe na, ƙoƙari raba ni yake da Ubangijina”
Ta faɗa cikin kuka, tana mai jin tsantsar ƙyama da kuma tsanar bokan a ranta, ta kuɗiri aniyar zata iya aikata komai akan duniyarta amman ba zata iya aikata abunda ya faɗa mata ta aikata ba.
Teema ta tsire baki, tana mamakin ƙawar ta'ta.
“Ai kin daɗe da rabuwa da raba hanya da Ubangijinki, tun da kika soma neman taimakon wani daga cikin bayinsa, Abunda zaki yi kawai ki aikata wannan in yaso daga baya sai ki nemi yafiyar”
“Ya ce min baƙin hudu yana bibiyata, kuma wannan baƙin duhun baƙar rana ce, what if ranar mutuwa na ne? Ba shine na farko daya faɗa min haka ba, Teema ina tsoro”
Kyalƙyalwa Teema tayi da dariya har da taɓawa tana kallon Rashida.
“Amman Wallahi kina da abun dariya, miye abun tsoro kuma? Ashe ke sabowar shiga ce wannan harka, ba lallai baƙar rana ta zama ranar mutuwa ba, yana nufin akwai abunda zai same ki marar daɗi wanda ke da kan ki zaki kira abun da baƙar rana”
Ta ɗan ji sassauci a zuciyarta, har ta samu damar haɗe yawun da ya tsaya mata a maƙoshi.
“Ni dai ina ganin haƙura zan yi, kar naje na sake mata kuma ya dawo kaina dan yace zan yi nasara amman akwai yiyuwar ya dawo kai na”
“Amman wallahi Rash kin ban mamaki, ke da na ke ganin, kamar zaki iya aikata komai akan Hilal, ashe son da kike masa na ƙarya ne, tun da har zaki iya bar wa wata shi, yanzu duk soyayyar da kuka yi ta tashi a banza kenan? Ƴaƴanki sun zama nata mijinki ya zama nata? Ko akwai wani wanda kike so bayan Hilal?”
“Babu shi, Hilal ne kawai, wallahi ina sonsa sosai”
“Kuma kin yarda ki barwa wata shi ko?”
“Na samu matsala akan jifar da nayi mata Teema, na jefeta ya faɗa kan ɗa na, kin ji ai yanzu yana faɗa min, yanzu haka Rafiq yana can kwance asibiti babu lafiya, ya damu matsalar ƙwaƙwalwa”
“Lallai wannan mata ita bata tsaya akan ta, irin wannan matar maganinta ki samu fitsari ki zuba mata a ruwa ya jiƙa ta sha, wallahi duk wani magani na tsari jikin data sha sai ya karye, amman kin ce tana shiga malamai ita ma?”
“Haka nake gani, saboda gaba ɗaya Hilal ya haukace ba shi da magana ta kowa sai na ta, baya kula ni a yanzu, kuma kin ga da dane ba zai iya sakina ba amman yanzu duba ki ga ya sake ni”
“To ina ganin ba tsari bane itama ta iya shige-shigen ne, sai aka bata aljana ta tsare ta, kin san wasu suna haka fa dan akwai su cimma burin su”
“Da gaske? Ballatana ta daɗe ba tayi aure ba zata iya haka”
“Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki share hawayen ki matuƙar ina raye sai kin koma cikin ƴaƴanki, yanzu kin ga mun fito cikin tashin hankali baki masa sallama ba, amman yanzu idan hankalinki ya kwanta natsuwarki ta dawo jikin ki, sai mu koma yayi mana aikin kawai”
“Amman ya ce sai nayi fashin salla fa?”
“To miye a ciki? Wasu ma baki ga rai suke kashewa ba? Ai daga baya sai ki ranka ki nemi yafiyar ubangijinki Allah fa gafurun rahimun ne, kin ga sai ma ki daina kwata kwata”
Shiru tayi tana nazari, tasan idan har ta aikata wannan abun ta yi, babban saɓo, ta yi fashin salla saboda biyan buƙatar da bata da tabbacin zata biya? Ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da tuƙin.
“Zan yi tunani akai Teema, amman ina jin tsoro sosai”
“Ai da tsoro zaki cuci kan ki, kawai ki cire wannan tsoron ki yaƙi zuciyarki”
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan”
Daga nan Teema ta ɗauko mata firar ƙawarsu, ita mai bin bokaye marar tsoro, wance ta mallake miji da uwarsa.
Duk tana yi ne dan kawai ta ƙara tunzira Rashida ta aikata, so that ita ma ta samu abokin shiga wuta, dan mugu be son ace shi kaɗai yake aikata abu.
Sai da ta fara biyawa ta sauke Teema a gidansu, sannan ta wuce na su gidan dan ta yi shirin zuwa gurin aiki, ganin karfe ɗaya ma bata yi ba.
Tun da tayi parking a harabar gidansu ta fara saƙe-saƙen abunda zata faɗa gurin aikin, dan gaba ɗaya kashe wayarta tayi. Tana shiga falo sai ga Momy ta fito daga ɗakinta jiki na rawa, Rashida na ganinta ta gane hankalinta a tashe yake.
“Momy lafiya?”
“Lafiya ba lau ba, tun ɗazu nake cikin zullumi Rashida”
“Me ya faru?”
Ummi ce ta shigo ƴar gurin Hajiya Barau mai sunan mahaifiyarta hakan yasa take kiranta da Ummi.
Duk cikin ƴaƴanta mata ita kaɗaice tazo tarbon lefen. Kusa da mahaifiyarta ta xauna tana kallon yanayinta kallonta Hajiya Barau tayi
“Kin gani ke kina son kashe na ki aure su kuma suna yi, idan so kike ki dawo gida mu zauna sai ki dawo”
“Haba Hajiya wallahi ni na gaji da irin wannan rayuwar da yake nuna min, kwata kwata bana gabansa, baya da aiki sai neman mata, tun abu na ɓoye har magana ta fara fita, ko fita nayi sai ya kawo wata a gida”
“Ina ruwanki da neman matansa? Ai kedai yana baki ci da sha ko yana baki na kashewa ina ruwan ki da lamarin, yanzu neman maza ma ake balle mata, abun ai yyi ne wanda be yi ba to bashi da kuɗin yin ne, ko ni ya nema kya ce ki kashe auren ki ki dawo gida balle kuma wata can daban”
Miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai ta fice, dan tasan duk yadda take son mahaifiyarta ta fahimci matsalarta ba fahimta zata yi ba.
Ƙwafa Hajiya Barau tayi taja wayarta tana soma labartawa abokin gulmarta rashin zuwan Namra tarbar lefen ƙannenta.
Duk hirar da suke be nuna mata jindaɗin hakan ko rashin jindaɗin saboda yana gaban Yasmin ne, yawancin maganar bata wuce uhn a'a ato, Har suka gama wayar.
Ƙaton cikin Yasmin ya kalla yana murmushi.
“Allah yasa karki haifa minɓɗa mai kahuwa”
Ta tsuke baki
“Mai hali dai baya fasa halinsa, ni wallahi haushi kake bani sosai”
“Daman duk kina da ciki ai baki ƙaunata kamar na kashe miki wani”
Ya faɗa yana jawo wayarsa da tayi ringing, number abokinsa Tahir ya gani.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Shine abunda ya furta bayan ƴan daƙiƙu da karɓa wayar.
“Okay gani nan zuwa”
Ya tashi tsaye da sauri, har Yasmin ta kalleshi
“Lafiya?”
“Wai Najeeb yayi hatsari, nan cikin gari”
“Subhanallahi, ina fatar be ji ciwo ba”
“Ban sani ba, sai naje tukunan”
Da sauri ya ɗauke Adnan da ke saman jikinsa ya ɗauki wayoyinsa ya zuba aljihu tare da keys ya fice hankali tashe.
*HILAL POV*
Lallaɓata yayi har sai da tayi shiru sannan yaja ta zuwa saman gadonsa ya zaunar da ita ya kama hannayenta ya riƙa.
“Na yarda ba ki aikata ba shikenan?”
“Har zuciyarka ka yarda da ni?”
“Na yarda da ke?”
“Zaka daina fushi da ni?”
“Zan daina”
“Zaka dawo da su Ezzah”
“Idan Hajiya ta yarda”
Haka yake ta amsa mata kamar tambayar babba da yaro, sai ya hau saman gadon yaja ta ƙirjinsa ya rumgume.
“I Love You”
Ƙamkamshi tayi
“I love you too”
Sun daɗe a haka kamin ya sake ta ya shiga yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sai ta ɗauko masa abinci. Ba dan yana so ba ya zauna yayi ƴan lomomi kaɗan ya tashi ya nufi gidan Hajiyarsa.
Da shigarsa Ezzah da Ulfah da sauran yaran gidan suka rugo da gudu suka tarbeshi. Ulfah ce kawai ta tambayi Kalsoom Ezzah kan ko a jikinta. Bayan ya gama ganinsu ya miƙa musu chocolates ɗin ya shigo da shi sannan ya wuce gurin Hajiyarsa.
Tun daga yanayin yadda ta amsa masa sallamarsa yasan akwai abunda ya faru. Guri ya samu ya zauna yana kallon tv dake ɗakinta, kamin daga bisani ya gaishe ta. A maimakon ta amsa sai kawai ta hau shi da faɗa
“Yanzu fisabilliahi abunda kake ƙoƙarin yi kyautawa ne? Kace xaka kare ta idan kun je kutu bayan ga abunda tayi ma ɗan ka, irin waɗannan matan fa zama da du matsala ne dan kai ma xata iya maka haka”
Daga yanayin maganar ta ya gane Amina ce ta kawo mata zancen, dan ita kaɗai yasan yayi zancen a gabanta sai kuma Alh Bashir.
“Amman Amina munafukace wallahi, zuwa tayi ta faɗa miki ko?”
“Ai dole ta faɗa min mana tun da abun yayi mata zafi, ni kama rabu da wannan matar ka nemi wata ka aura”
“Gaskiya ba zan iya rabuwa da ita ba”
“To ko zaka auro wacce zata riƙa maka ƴaƴanka, dole ne ka ƙara aure ko kuma ka rabu da ita idan baka shirya zama da mata biyu ba”
“Haba Hajiya, kuskure ne nima a yanzu na gane ba ita ce ta aikata ba”
“To waya aikata? Ga abu ƙiri da muzu ka nemi takewa dan kana son ta, ah lallai ba banza ta barka ba, Ezzah ma tana ta faɗar irin abunda take musu a gidan, cin amana zalla”
Dariya abun ya bashi yau kuma Hajiya da kanta take irin wannan furucin.
“Babu maganin komai Hajiya, amman wannan matsalar nima ban san kan ta ba”
“To ni dai na faɗa maka ko ka ƙara aure ko ka rabu da ita, tashi ka bani guri”
Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya
“Hajiya ki fahimta...”
“Ba zan fahimta ba, ka tafiyarka kawai”
Yasan duk yadda zai yi ba zata fahimta sai kawai ya tashi ya fice da jimmar idan ta huce zai dawo ya fahimtar da ita.
-----------------------------------------------------------------
*Jiya naje biki ban samu na yi typing ba, so wannan zai zama na jiya, na yau kuma sai dare zan kawo. Thank you 🖤*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *60 - NOT EDITED ⚠️*
*RASHIDA POV.*
“Teema ya faɗa min abinda ya fi ƙarfin zuciyata da tunani, ya bani labarin yau da kuma gobe na, ƙoƙari raba ni yake da Ubangijina”
Ta faɗa cikin kuka, tana mai jin tsantsar ƙyama da kuma tsanar bokan a ranta, ta kuɗiri aniyar zata iya aikata komai akan duniyarta amman ba zata iya aikata abunda ya faɗa mata ta aikata ba.
Teema ta tsire baki, tana mamakin ƙawar ta'ta.
“Ai kin daɗe da rabuwa da raba hanya da Ubangijinki, tun da kika soma neman taimakon wani daga cikin bayinsa, Abunda zaki yi kawai ki aikata wannan in yaso daga baya sai ki nemi yafiyar”
“Ya ce min baƙin hudu yana bibiyata, kuma wannan baƙin duhun baƙar rana ce, what if ranar mutuwa na ne? Ba shine na farko daya faɗa min haka ba, Teema ina tsoro”
Kyalƙyalwa Teema tayi da dariya har da taɓawa tana kallon Rashida.
“Amman Wallahi kina da abun dariya, miye abun tsoro kuma? Ashe ke sabowar shiga ce wannan harka, ba lallai baƙar rana ta zama ranar mutuwa ba, yana nufin akwai abunda zai same ki marar daɗi wanda ke da kan ki zaki kira abun da baƙar rana”
Ta ɗan ji sassauci a zuciyarta, har ta samu damar haɗe yawun da ya tsaya mata a maƙoshi.
“Ni dai ina ganin haƙura zan yi, kar naje na sake mata kuma ya dawo kaina dan yace zan yi nasara amman akwai yiyuwar ya dawo kai na”
“Amman wallahi Rash kin ban mamaki, ke da na ke ganin, kamar zaki iya aikata komai akan Hilal, ashe son da kike masa na ƙarya ne, tun da har zaki iya bar wa wata shi, yanzu duk soyayyar da kuka yi ta tashi a banza kenan? Ƴaƴanki sun zama nata mijinki ya zama nata? Ko akwai wani wanda kike so bayan Hilal?”
“Babu shi, Hilal ne kawai, wallahi ina sonsa sosai”
“Kuma kin yarda ki barwa wata shi ko?”
“Na samu matsala akan jifar da nayi mata Teema, na jefeta ya faɗa kan ɗa na, kin ji ai yanzu yana faɗa min, yanzu haka Rafiq yana can kwance asibiti babu lafiya, ya damu matsalar ƙwaƙwalwa”
“Lallai wannan mata ita bata tsaya akan ta, irin wannan matar maganinta ki samu fitsari ki zuba mata a ruwa ya jiƙa ta sha, wallahi duk wani magani na tsari jikin data sha sai ya karye, amman kin ce tana shiga malamai ita ma?”
“Haka nake gani, saboda gaba ɗaya Hilal ya haukace ba shi da magana ta kowa sai na ta, baya kula ni a yanzu, kuma kin ga da dane ba zai iya sakina ba amman yanzu duba ki ga ya sake ni”
“To ina ganin ba tsari bane itama ta iya shige-shigen ne, sai aka bata aljana ta tsare ta, kin san wasu suna haka fa dan akwai su cimma burin su”
“Da gaske? Ballatana ta daɗe ba tayi aure ba zata iya haka”
“Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki share hawayen ki matuƙar ina raye sai kin koma cikin ƴaƴanki, yanzu kin ga mun fito cikin tashin hankali baki masa sallama ba, amman yanzu idan hankalinki ya kwanta natsuwarki ta dawo jikin ki, sai mu koma yayi mana aikin kawai”
“Amman ya ce sai nayi fashin salla fa?”
“To miye a ciki? Wasu ma baki ga rai suke kashewa ba? Ai daga baya sai ki ranka ki nemi yafiyar ubangijinki Allah fa gafurun rahimun ne, kin ga sai ma ki daina kwata kwata”
Shiru tayi tana nazari, tasan idan har ta aikata wannan abun ta yi, babban saɓo, ta yi fashin salla saboda biyan buƙatar da bata da tabbacin zata biya? Ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da tuƙin.
“Zan yi tunani akai Teema, amman ina jin tsoro sosai”
“Ai da tsoro zaki cuci kan ki, kawai ki cire wannan tsoron ki yaƙi zuciyarki”
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan”
Daga nan Teema ta ɗauko mata firar ƙawarsu, ita mai bin bokaye marar tsoro, wance ta mallake miji da uwarsa.
Duk tana yi ne dan kawai ta ƙara tunzira Rashida ta aikata, so that ita ma ta samu abokin shiga wuta, dan mugu be son ace shi kaɗai yake aikata abu.
Sai da ta fara biyawa ta sauke Teema a gidansu, sannan ta wuce na su gidan dan ta yi shirin zuwa gurin aiki, ganin karfe ɗaya ma bata yi ba.
Tun da tayi parking a harabar gidansu ta fara saƙe-saƙen abunda zata faɗa gurin aikin, dan gaba ɗaya kashe wayarta tayi. Tana shiga falo sai ga Momy ta fito daga ɗakinta jiki na rawa, Rashida na ganinta ta gane hankalinta a tashe yake.
“Momy lafiya?”
“Lafiya ba lau ba, tun ɗazu nake cikin zullumi Rashida”
“Me ya faru?”