Sashe 107
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru ya ɗan yi yana tunanin faɗawa abokinsa nasa, sai dai baya jin zai iya ɓoyewa mustafa komai, kamar yadda mustafan baya ɓoye masa, kuma yasan idan ma be faɗa masa yanzu ba zai faɗa masa gaba, ko kuma ƴan gulma su tsegunta masa.
Hakan yasa be ɓoye masa komai daga haɗuwarsa da Namra da kuma labarin da Namra ta ba su nata.
Shi kansa Mustafa ya girgiza kuma ya tausayawa Namra matuƙa. Babu ma abunda yafi taɓa shi kamar rabuwa da tayi da iyayinta.
“Ai kaji matsalar mata suna da ƙaramar ƙwaƙwalwa, dan me zaka rabu da uwayen ka kan saurayi?”
Lamido ya numfasa.
“Ai mutum baya iya tsallake ƙaddararsa, sannan mu kan mu maza muna da matsala, da yawa sai ki ga dan kuɗin gidansu yarinya ake son ta, ni ina mamakin irin mazan nan wallahi, haka kawai abun wani ya tsune maka ido, ni dai Allah be sa min irin wannan rayuwar ba wallahi”
“Ai irin ka irin ka kaɗan ne Lamido, ni ma nan idan na ga arziki ba zan ƙi bi ba, masu arzikin nan suke kawai suke watayawa, ka duba kaga tun yaushe ka gama digiri ka yo bautar ƙasa, amman aiki ya gagareka, yanzu da kai ɗan wani mai kuɗi ne, da yanzu kana can Abuja kana hanawa kana aiki a wani babban kamfani”
Ajiyar zuciyar Lamido ya sauke.
“Muma Allah be manta da mu ba, kuma kaga wannan sana'ar Napep ɗin da nake? Ni ta wadarta da ni kamin Allah ya buɗo min wata hanyar kuma”
“Allah ya tabbatar mana da alheri, amman babu wanda ya ƙi kuɗi”
“Ita yanzu kallo ɗaya zata yi ma duka mazan takalawa alhalin ba haka muke ba, dan bamu taru muka zama ɗaya ba”
“Uhm, rayuwar ce sai a hankali, Allah ya bata wani na gari, ya shirya tsakaninta da iyayenta”
“Amin Amin”
*ABDOOL POV*
```Yana tsaye jikin wani upstairs, ya hango ta tana wani irin gudu kamar zata faɗi, kare na biye da ita a baya yana mata haushi, da alama karen take ma gudun, bata ankara da ƙaton ramen dake gabanta sai kawai ta faɗa cikin kamar an jefata. Daga can cikin ramen ta ɗagowa Abdool hannu tana son ya taimake ta sai kuma take, shi kuma ya yi tsaye yana kallonta kamar zai je, kamar ba zai je ba.```
Firgigit ya farka daga ɗan kajeren bachin daya kwashe shi yanzu-yanzu.
Haƙi yake sosai yana maida numfashi, jin yake kamar a zahiri ne abun ya faru. kyakkyawan askin kansa ya shafa, ya lumshe ido ya buɗe yana kallon agogon ɗakin.
“Mtsssss mi zai sa ba zan yi mafarkinta ba? Bayan na kwanta da ita a raina? Why this? Miyasa na zurfafa akan yarinyar nan ne? I'm totally mad”
Ya unƙura ya tashi ya nufi bathroom, zuciyarsa na raya masa ba zai yi mafarkinta haka nan kawai ba, shi kumasai yaƙar zuciyar tasa yake yana ƙaryata ta, dan ganin yake idan har ya yarda da ita to zata kai shi ga hallaka ne kawai.
Sai faman faɗa yake ma kansa kamar wani taɓaɓɓe. Har yayi wanka ya fito mafarkin be daina tsaya masa a rai ba. Haka ya shirya cikin tufafi na alfarma, wata musulmar shadda ya saka har wani maiƙo take tana shining daya ya motsa sai shadda ta amsa amo, shaddar ta karɓesa sosai, ta zauna a jikinsa kasancewarta sky blue, shi kansa da ya kalli kansa a madubi sai da yayi murmushi.
Wayarsa ya ɗauka ya ɗauki kansa hoto, sannan ya baro gaban madubin baya ya feshe jikinsa da turare mai mugun tsada da ƙamshi.
Already ya saka agogo hannunsa da zabban azurfa.
Yana doso sitting room mafarkinsa ya faɗo masa a rai. Wani irin faɗuwa gabansa ya yi har sai da ya rumtse ido ya murƙushe bakinsa.
“Wai miyasa yarinyar ta tsaya min arai ne? Ko dai akwai wani abun ne? Yeah na ga kare yana binta, ta faɗa rame? Me wannan yake nufi ne?”
“Allah ya taimaki Yarima, ba mu da masaniya akan abunda kake magana a kai, Allah yaja kwanan ka”
Kallon mamaki yayi musu yana juyar da kai, dan shi be san ya iso sitting room ba ma sai yanzu, ashe a fili yake maganar.
Iskar bakinsa ya furzar ya kalli tsadadden agogon hannunsa. Ƙarfe biyu saura minti goma ya gani, ya san ɗaurin auren ƙarfe biyu ne.
“Allah ya taimaki Yarima, tuni Mai martaba, ya kira kana bachi har ya bada umarnin tashin ka”
Hannayensa ya zuba cikin aljihu.
“Yanzu dole sai an naɗa min rawani?”
“Allah ya taimaki Yarima, haka Mai Martaba ya ce, har alkibar da zaka saka mun zo da ita”
Haka ya zauna suka naɗa masa rawani akai, ya fito fes Sarki, ba ma ɗan Sarki ba.
Miƙewa yayi tsaye suka saka masa baƙar alkyabar mai ratsin zaiba, sannan suka fiddo takalmin alkyabar suka aje masa ƙasa. A ƙoƙarinsa na saka takalmin ya kalli Sadauki ya ce.
“Idan ka yi mafarki kare yana bin ka me hakan yake nufi?”
“Allah ya taimaki Yarima, Maƙiyi ne.”
Ya ɗan yi shiru na wasu mintuna, kamin ya sake furta.
“Idan kuma ka faɗa a rame fa? Sai kuma ka miƙo min hannu kana son kamo ni?”
“Wannan Makaru ne, Allah yaja kwanan ka, idan kuma ina miƙa masa hannu to ina neman taimakon ka ne”
Sai da Sadauki ya gama amsa masa duka tambayoyinsa sannan ya saka takarmin, zai soma tafiya Sadauki ya ciro wani turare zai fasa masa.
“Allah yaja kwanan ka Mai Martaba ya ce afesa maka wannan”
“Na saka turare bana da buƙata”
“Allah ya taimaki Yarima, wannan na gidan sarautar ne, na Masarautar Katsina ne, ƙamshinsa ne zai sanar da isowar ka, kuma wannan turaren na gidane da ake haɗawa tun gadon gadon”
Ba dan yana so ba, ya tsaya suka fesa masa turaren sannan suka shiga gaba, wasu kuma a baya, shi kuma sai wata tafiya yake kaɗan-kaɗan, mai cike da tsantsar kasaita, da nuna isa, bayan kuma shi hankalinsa yana can wani gurin dabam.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *66 NOT EDITED ⚠️*
AMIRA POV.
Ta san yau zai dawo, amma hakan be hana ta kiwarsa ba, duk sai taji gidan ya mata girma kamar ita kaɗai ce a ciki. Tana son aika masa da saƙon tana tuna gargaɗin da yayi mata akan ta daina.
Bata san hawaye sun zubo mata ba, har sai da ta ji ɗuminsu a kumatunta, ɗan murmushi ta yi ta kai hannu ta share hawayen tana magana da kanta.
“Idan na ce zan yaƙi zuciya akan ka, zan cuce kai na, ban cancanci komai ba sai kyakkyawan sakamako, zan iya barin komai a kan ka, zan jure haƙurin rasa komai akan ka amman ba zan iya raka ka ba, ni nafi dacewa da kai Abdool, ba zan jure ganin wata ta raɓe ka ba, ba a hallinta maka wata matar aure ba, face Amira.
Wallahi ina son ka Abdool fiye da irin son da uwa take yi ma ɗan ta, kai mafarki, kuma kai kaɗai ne cikar burina, idan har na rasa ka Abdool to sai dai ko wace mace ta rasa ka”
Cige bakinta ta yi tana karɓar kukan da ya zo mata gadan-gadan. Mulmulawa ta yi ta mulmulo saman gado tana jin abu marar daɗi yana ratsa zuciyarta. Hoton da Abdool ya yi da Amal tafi tsurawa ido, tana masa wani kallo kamar wacce bata san shi ba.
“Kin yi sa'ar ɗan'uwa ni kuma zan yi sa'ar miji, ina son ka da iyalan ka Abdool”
Bata ankaro da ɗauki lokaci tana kukan ba, har sai da ta ji abu na ƙoƙarin rufe mata ido, alamar idon ya kumbura kenan.
Muryar Ummi da ta ji ne yasa ta sauri sauka saman gadon ta shiga bathroom ta wanke fuskarta, ta fito ta nufo falo.
A tsaye ta samu Ummi tana rataye da jakarta, mayafinta a hannu, Amal ma na tsaye a bayanta sai kumburi take, ita ala dole ga auta.
Tun da Amira ta soma saukowa downstairs Ummi take kalle da yanayinta, ga kuma kumburin da idonta da ƴa yi, fuskarta har ya soma ja abun ka da farar mace.
“Ba ki da lafiya ne?”
“A'a... Eh... Kai na ne yake ɗan ciwo”
Ummi ma uwace, ta fahimci Amira tana cikin damuwa ne, ko da bata fito a fili ta faɗa mata ba. Hannu ta kai ta shafa kan Amira zuwa wuyanta.
“Ki yi haƙuri kin ji, komai mai wuce wa ne, kin ji? Rayuwa bata tabbata haka amman dai ki yi tunani kin ji? Mu zamu fita, Haleema da Meesha ma sun fita Fauza ce kawai take bachi”
“Okay to sai kun dawo, me za'a girka?”
“No no kije kawai ki kwanta Shukura za ta yi komai, kije kawai ki yi ma kan ki karatun ta natsu”
Daga haka Ummi ta fice Amal na binta a baya, tana waigo Amira da harara dan ita har yanzu haushinta take ji, wai ta maida mata ɗaki kamar nata, daman can Amal ba son mutane take ba.
Maganar Ummi ta tsaya a mata a rai, me take nufi da ta yi ma kanta karatun ta natsu? Me hakan yake nufi? Juyawa ta yi ta nufi upstairs zuciyarta da tunani kala-kala.
RASHIDA POV.
Tana kewar ɗan ta sosai, wata ƙila dan kasancewarsa shi kaɗai ne ɗa namiji a gareta, ko kuma dan ita silar mutuwarsa.
“Na rasa abubuwa da dama, na rasa mijina, ɗa na, na rasa lafiya ta, yanzu kuma ina ƙoƙarin rasa iyayena, ni ka ɗai ce mai Aure da nake aikata zina? Ba suna nan da yawa ba? Miyasa ni bana da sa'a?”
Miƙewa ta yi tsaye daga saman prayer mat da take ta cire hijabinta ta nufi window.
“Idan har na bar gidan nan kowa zai tambayi dalili, kuma dole wasu za su gane abunda yake faruwa, idan kuma na zauna zan fuskancin tsagwama da takurawa, miye mafita?”
Hannu ta kai ta riƙa window, wannan karon sai ta koma zancen zuci.
Hakan yasa be ɓoye masa komai daga haɗuwarsa da Namra da kuma labarin da Namra ta ba su nata.
Shi kansa Mustafa ya girgiza kuma ya tausayawa Namra matuƙa. Babu ma abunda yafi taɓa shi kamar rabuwa da tayi da iyayinta.
“Ai kaji matsalar mata suna da ƙaramar ƙwaƙwalwa, dan me zaka rabu da uwayen ka kan saurayi?”
Lamido ya numfasa.
“Ai mutum baya iya tsallake ƙaddararsa, sannan mu kan mu maza muna da matsala, da yawa sai ki ga dan kuɗin gidansu yarinya ake son ta, ni ina mamakin irin mazan nan wallahi, haka kawai abun wani ya tsune maka ido, ni dai Allah be sa min irin wannan rayuwar ba wallahi”
“Ai irin ka irin ka kaɗan ne Lamido, ni ma nan idan na ga arziki ba zan ƙi bi ba, masu arzikin nan suke kawai suke watayawa, ka duba kaga tun yaushe ka gama digiri ka yo bautar ƙasa, amman aiki ya gagareka, yanzu da kai ɗan wani mai kuɗi ne, da yanzu kana can Abuja kana hanawa kana aiki a wani babban kamfani”
Ajiyar zuciyar Lamido ya sauke.
“Muma Allah be manta da mu ba, kuma kaga wannan sana'ar Napep ɗin da nake? Ni ta wadarta da ni kamin Allah ya buɗo min wata hanyar kuma”
“Allah ya tabbatar mana da alheri, amman babu wanda ya ƙi kuɗi”
“Ita yanzu kallo ɗaya zata yi ma duka mazan takalawa alhalin ba haka muke ba, dan bamu taru muka zama ɗaya ba”
“Uhm, rayuwar ce sai a hankali, Allah ya bata wani na gari, ya shirya tsakaninta da iyayenta”
“Amin Amin”
*ABDOOL POV*
```Yana tsaye jikin wani upstairs, ya hango ta tana wani irin gudu kamar zata faɗi, kare na biye da ita a baya yana mata haushi, da alama karen take ma gudun, bata ankara da ƙaton ramen dake gabanta sai kawai ta faɗa cikin kamar an jefata. Daga can cikin ramen ta ɗagowa Abdool hannu tana son ya taimake ta sai kuma take, shi kuma ya yi tsaye yana kallonta kamar zai je, kamar ba zai je ba.```
Firgigit ya farka daga ɗan kajeren bachin daya kwashe shi yanzu-yanzu.
Haƙi yake sosai yana maida numfashi, jin yake kamar a zahiri ne abun ya faru. kyakkyawan askin kansa ya shafa, ya lumshe ido ya buɗe yana kallon agogon ɗakin.
“Mtsssss mi zai sa ba zan yi mafarkinta ba? Bayan na kwanta da ita a raina? Why this? Miyasa na zurfafa akan yarinyar nan ne? I'm totally mad”
Ya unƙura ya tashi ya nufi bathroom, zuciyarsa na raya masa ba zai yi mafarkinta haka nan kawai ba, shi kumasai yaƙar zuciyar tasa yake yana ƙaryata ta, dan ganin yake idan har ya yarda da ita to zata kai shi ga hallaka ne kawai.
Sai faman faɗa yake ma kansa kamar wani taɓaɓɓe. Har yayi wanka ya fito mafarkin be daina tsaya masa a rai ba. Haka ya shirya cikin tufafi na alfarma, wata musulmar shadda ya saka har wani maiƙo take tana shining daya ya motsa sai shadda ta amsa amo, shaddar ta karɓesa sosai, ta zauna a jikinsa kasancewarta sky blue, shi kansa da ya kalli kansa a madubi sai da yayi murmushi.
Wayarsa ya ɗauka ya ɗauki kansa hoto, sannan ya baro gaban madubin baya ya feshe jikinsa da turare mai mugun tsada da ƙamshi.
Already ya saka agogo hannunsa da zabban azurfa.
Yana doso sitting room mafarkinsa ya faɗo masa a rai. Wani irin faɗuwa gabansa ya yi har sai da ya rumtse ido ya murƙushe bakinsa.
“Wai miyasa yarinyar ta tsaya min arai ne? Ko dai akwai wani abun ne? Yeah na ga kare yana binta, ta faɗa rame? Me wannan yake nufi ne?”
“Allah ya taimaki Yarima, ba mu da masaniya akan abunda kake magana a kai, Allah yaja kwanan ka”
Kallon mamaki yayi musu yana juyar da kai, dan shi be san ya iso sitting room ba ma sai yanzu, ashe a fili yake maganar.
Iskar bakinsa ya furzar ya kalli tsadadden agogon hannunsa. Ƙarfe biyu saura minti goma ya gani, ya san ɗaurin auren ƙarfe biyu ne.
“Allah ya taimaki Yarima, tuni Mai martaba, ya kira kana bachi har ya bada umarnin tashin ka”
Hannayensa ya zuba cikin aljihu.
“Yanzu dole sai an naɗa min rawani?”
“Allah ya taimaki Yarima, haka Mai Martaba ya ce, har alkibar da zaka saka mun zo da ita”
Haka ya zauna suka naɗa masa rawani akai, ya fito fes Sarki, ba ma ɗan Sarki ba.
Miƙewa yayi tsaye suka saka masa baƙar alkyabar mai ratsin zaiba, sannan suka fiddo takalmin alkyabar suka aje masa ƙasa. A ƙoƙarinsa na saka takalmin ya kalli Sadauki ya ce.
“Idan ka yi mafarki kare yana bin ka me hakan yake nufi?”
“Allah ya taimaki Yarima, Maƙiyi ne.”
Ya ɗan yi shiru na wasu mintuna, kamin ya sake furta.
“Idan kuma ka faɗa a rame fa? Sai kuma ka miƙo min hannu kana son kamo ni?”
“Wannan Makaru ne, Allah yaja kwanan ka, idan kuma ina miƙa masa hannu to ina neman taimakon ka ne”
Sai da Sadauki ya gama amsa masa duka tambayoyinsa sannan ya saka takarmin, zai soma tafiya Sadauki ya ciro wani turare zai fasa masa.
“Allah yaja kwanan ka Mai Martaba ya ce afesa maka wannan”
“Na saka turare bana da buƙata”
“Allah ya taimaki Yarima, wannan na gidan sarautar ne, na Masarautar Katsina ne, ƙamshinsa ne zai sanar da isowar ka, kuma wannan turaren na gidane da ake haɗawa tun gadon gadon”
Ba dan yana so ba, ya tsaya suka fesa masa turaren sannan suka shiga gaba, wasu kuma a baya, shi kuma sai wata tafiya yake kaɗan-kaɗan, mai cike da tsantsar kasaita, da nuna isa, bayan kuma shi hankalinsa yana can wani gurin dabam.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *66 NOT EDITED ⚠️*
AMIRA POV.
Ta san yau zai dawo, amma hakan be hana ta kiwarsa ba, duk sai taji gidan ya mata girma kamar ita kaɗai ce a ciki. Tana son aika masa da saƙon tana tuna gargaɗin da yayi mata akan ta daina.
Bata san hawaye sun zubo mata ba, har sai da ta ji ɗuminsu a kumatunta, ɗan murmushi ta yi ta kai hannu ta share hawayen tana magana da kanta.
“Idan na ce zan yaƙi zuciya akan ka, zan cuce kai na, ban cancanci komai ba sai kyakkyawan sakamako, zan iya barin komai a kan ka, zan jure haƙurin rasa komai akan ka amman ba zan iya raka ka ba, ni nafi dacewa da kai Abdool, ba zan jure ganin wata ta raɓe ka ba, ba a hallinta maka wata matar aure ba, face Amira.
Wallahi ina son ka Abdool fiye da irin son da uwa take yi ma ɗan ta, kai mafarki, kuma kai kaɗai ne cikar burina, idan har na rasa ka Abdool to sai dai ko wace mace ta rasa ka”
Cige bakinta ta yi tana karɓar kukan da ya zo mata gadan-gadan. Mulmulawa ta yi ta mulmulo saman gado tana jin abu marar daɗi yana ratsa zuciyarta. Hoton da Abdool ya yi da Amal tafi tsurawa ido, tana masa wani kallo kamar wacce bata san shi ba.
“Kin yi sa'ar ɗan'uwa ni kuma zan yi sa'ar miji, ina son ka da iyalan ka Abdool”
Bata ankaro da ɗauki lokaci tana kukan ba, har sai da ta ji abu na ƙoƙarin rufe mata ido, alamar idon ya kumbura kenan.
Muryar Ummi da ta ji ne yasa ta sauri sauka saman gadon ta shiga bathroom ta wanke fuskarta, ta fito ta nufo falo.
A tsaye ta samu Ummi tana rataye da jakarta, mayafinta a hannu, Amal ma na tsaye a bayanta sai kumburi take, ita ala dole ga auta.
Tun da Amira ta soma saukowa downstairs Ummi take kalle da yanayinta, ga kuma kumburin da idonta da ƴa yi, fuskarta har ya soma ja abun ka da farar mace.
“Ba ki da lafiya ne?”
“A'a... Eh... Kai na ne yake ɗan ciwo”
Ummi ma uwace, ta fahimci Amira tana cikin damuwa ne, ko da bata fito a fili ta faɗa mata ba. Hannu ta kai ta shafa kan Amira zuwa wuyanta.
“Ki yi haƙuri kin ji, komai mai wuce wa ne, kin ji? Rayuwa bata tabbata haka amman dai ki yi tunani kin ji? Mu zamu fita, Haleema da Meesha ma sun fita Fauza ce kawai take bachi”
“Okay to sai kun dawo, me za'a girka?”
“No no kije kawai ki kwanta Shukura za ta yi komai, kije kawai ki yi ma kan ki karatun ta natsu”
Daga haka Ummi ta fice Amal na binta a baya, tana waigo Amira da harara dan ita har yanzu haushinta take ji, wai ta maida mata ɗaki kamar nata, daman can Amal ba son mutane take ba.
Maganar Ummi ta tsaya a mata a rai, me take nufi da ta yi ma kanta karatun ta natsu? Me hakan yake nufi? Juyawa ta yi ta nufi upstairs zuciyarta da tunani kala-kala.
RASHIDA POV.
Tana kewar ɗan ta sosai, wata ƙila dan kasancewarsa shi kaɗai ne ɗa namiji a gareta, ko kuma dan ita silar mutuwarsa.
“Na rasa abubuwa da dama, na rasa mijina, ɗa na, na rasa lafiya ta, yanzu kuma ina ƙoƙarin rasa iyayena, ni ka ɗai ce mai Aure da nake aikata zina? Ba suna nan da yawa ba? Miyasa ni bana da sa'a?”
Miƙewa ta yi tsaye daga saman prayer mat da take ta cire hijabinta ta nufi window.
“Idan har na bar gidan nan kowa zai tambayi dalili, kuma dole wasu za su gane abunda yake faruwa, idan kuma na zauna zan fuskancin tsagwama da takurawa, miye mafita?”
Hannu ta kai ta riƙa window, wannan karon sai ta koma zancen zuci.