Sashe 15
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ba dole sai ita ba, amman ita ce tafi ko wace sauƙi”
Tahir ya kalli Uzair
“Toh kai kana da mak maka wannan aikin ne?”
“Akwai wata ƙawarta ina jin kamar zata iya, amman what if ba ayi nasara ba?”
Tahir ya dafa shi.
“Ka yarda kawai za'ayi nasara, karka sawa kanka wannan”
Kai ya girgiza
“Ni dai ko na haƙura kawai na ƙyaleta”
Ganin yadda Uzair ya tsorata yasa Malamin shiga kwantar masa da hankalin
“Za'ayi nasara, karka damu, ka haɗani da wadda zata kai mata rigar na san yadda zan tsara mata komai”
Shiru Uzair be ce komai ba, shi dai sai tunani yake. Ganin hakan yasa Najeeb yace da Malamin
“Shikenan a fara aikin kawai, zan turo maka dubu ɗari a account ina tunanin zasu isa? Idan ma da wani abu sai ka kira a waya”
“Zasu isa inshallah, amman za a kawo rigar da taɓa sawa, dan da ita zamuyi aiki, kuma ina son ganin yarinyar”
“Ba matsala zuwa gobe duk yadda muka yi zaka ji ni”
Daga haka suka yi sallama, Najeeb yasa direba ya maida malamin. Sannan suka ya dawo falo suka shiga tattauna maganar.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 12*
HILAL POV.
Wanka yayi ya shirya cikin wata gizna, maroon color, sannan ya ɗauki hulla mai kyau ya saka, ya ɗauki agogon hannu ya saka ya feshe jikinshi da turare, sannan ya buɗe wardrobe ya ɗauko sababin kuɗi ya saka a aljihu, sannan ya dawo gaban madubi ya sake kallon kansa, ya tabbatar da kwaliyarsa ta fito, sannan ya ɗauki keys ɗinsa ya saka baƙaƙen takalmi, ya fice.
Ko da ya fito falo, Rashida na gaban dinning tana shirya musu dinner, su Ulfah zagayeta suna nuna mata assignment ɗinsu.
Kusa da ita ya ƙarasa yana leƙon abincin da take zubawa.
“Pyar a zubawa yara nasu nawa sai na dawo mu ci”
“Ina zaka je?”
“Ango zamu je rakawa ba zan daɗe ba”
Juyowa tayi ta kalleshi daga sama har ƙasa, yadda kyau nan nasa ya fito ya bata tsoro. Shi kuma sai yayi kamar be ga kallon da take masa ba sai ya kalli agogon hannunsa.
“Bari naje kar nayi latti, ni kawai suke jira”
Hannu yasa ya rufe idon Ulfah sannan yayi mata kiss a baki, sannan ya nufi ƙofa sai ƙanshi turare yake.
“Allah ya tsare min kai ni dai”
Ta faɗa lokacin da zai fice. Murmushi kawai yayi ya saka kai ya fice.
Motarsa ya shiga yayi horn mai gadi ya buɗe masa, ya hau ti-ti zuciyarsa cike da nishaɗi.
Cikin ƴan mintuna ya isa estate ɗin su Kalsoom. Numbers ɗin gidaje ya riƙa dubawa har ya kai ga number.
Dai-dai gate ɗin ya tsaya yayi horn yayi mai gadin gidan ya leƙo sannan ya buɗe masa, sannan ya shiga harabar gidan yayi parking. Sai ya fito ya nufo mai gadi ya bashi hannu suka gaisa sannan yace
“Dan Allah ko nan ne gidan Alhaji Faruk Kafinta?”
“Eh nan ne”
“Dan Allah mai gidan yana ciki?”
“Eh yana ciki”
“Dan Allah kayi min sallama da shi”
“To wa za'ace masa?”
“Ce masa Doctor Hilal ne”
Da sauri mai gadin ya nufi cikin gidan. Doctor Hilal kuma ya dawo gurin motarsa ya tsaya yana ƙarema gidan kallo.
Hilal ya kusan minti goma tsaye a gurin sannan Abban Kalsoom ya fito, yana ganin Doctor Hilal ya washe baki.
“Maraba da bokan turai, yau likita a gidana na”
Da sauri Hilal ya miƙa masa hannu suka gaisa, har da ɗan risina masa yana murmushi.
“Wai daman nan ne gidan ka?”
“Nan ne kasan abu ga talaka”
Ya faɗa yana dariya, yasan Doctor Hilal sosai dan shine likitan da yake dubashi a duk lokacin daya je asibiti, sai dai Doctor Hilal be waye shi sosai ba, sai yanzu.
“Shigo ciki mana”
A falonsa ya shiga da Hilal ya ɗauko masa lemu da kansa, zai zuba masa Hilal yayi saurin karɓa ya zuba da kansa.
“Ya fama da jama'ah”
Daddy ya faɗa yayin da ya zauna saman kujera.
“Al-hamdulillah da fatar dai na same ku lafiya”
“Lafiya ƙalau, yau dai sai ga likita gidana, ina ji dai hanya ce ta biyo da kai, ni dai nasan Likita be san gidan ba”
Doctor yayi dariya.
“Yanzu ma dalili ne ya kawo ni, akwai wacce na gani naga ta shigo nan gidan”
“To, kuma bata faɗa maka sunanta ba? Ta yiyu ma ƴar maƙota ce”
“A dai yadda nake tunani ƴar nan gidan ce, sunan ta Kalsoom wata doguwa haka”
Daddy yayi murmushi.
“Kalsoom ai ƙanwar ka ce Likita”
Hilal yayi ƙasa da kanshi
“Ina fatar ba'ayi mata miji ba?”
“Ba'a mata ba, amman akwai manema”
“Ina fatar shiga cikin su, amman idan kayi min izini, dan ni da gaske nake yi idan Allah ya yarda”
“Ba ni da matsala Likita, inda har kun dai-dai ta kanku, ni da Kalsoom ai duk mallakin ka ne, tun da ni Patient ɗin ka ne”
Ƙasa Hilal yayi da kansa cike da jindaɗin maganar Daddy, be ɗago ba har sai da Daddy ya tashi yana faɗin
“Bari na kira maka ita”
Daddy na ficewa ya miƙe tsaye ya ƙara karkaɗe shaddarsa, sannan ya zauna a natse yana kallon ƙofa. Sai gata ta fito cikin hijabi tana tafiya a hankali, sallama ta fara masa sannan ta nemi guri ta zauna, tana gaishe shi.
“Lafiya ƙalau, ina fatar Gimbiyar tana nan lafiya”
“Al-Hamdulillah”
“Mashallah, na zo mun gaisa da Daddy ki sai yace ze kira min ke mu gaisa, ina fatar ban takura ki ba, kuma in babu matsala zan so ki gabatar min da kan ki”
“Sunana Kalsoom ni budurwace ina aiki a MTN Service, nan ne gidan mu kuma ina ƙarƙashin kulawar iyaye na ”
Gabansa ya faɗi, jin tana aiki, shi da yake son ƙara aure saboda aikin da matarsa take sai kuma ya sake karo da wata ma'aikaciyar. Sai dai be nuna mata ba, sai kawai yayi murmushi yace
“Mashallah, ni kuma sunan Doctor Hilal Abubakar Mai-lafiya, ina aiki a American Hospital dake nan Kaduna, ina da mata ɗaya da yara uku, ina fatar zan samu karɓuwa, duk da kasancewar na san muna da yawa”
Murmushi kawai tayi masa, ta shiga murza hannunta.
“Ba zan cikaki da surutu ba, dan na fahimci kamar Gimbiyar tawa bata son yawan magana, ni kuma gani kamar wazirin aku, zan nemi alfarma ɗaya zuwa biyu”
“Allah yasa zan iya”
Ta faɗa da murmushi.
“Ina farko ina son ki bani damar zuwa muna gaisawa, bace kullum ba gudun kar na takura miki, amman zan riƙa kwatantawa, sannan ina son ki samin number wayarki”
A take ta karanto masa number, sai da yasa yayi saving sannan ya kalle ta
“Amman fa ni bana son na kira naji User busy, dan ni ina da kishi sosai, ba kamar sauran samarin ki bane”
Nan ma murmushi tayi, sai ya tashi tsaye yana faɗin
“Bari na zo na tafi, kar Daddy yace zan sace masa ƴa”
Sai a lokacin tace
“Ai Daddy ya san be kawo ɓarawo gidansa ba”
“Kar kiyi saurin yanke hukunci, Wallahi sata na zo nayi masa”
A kaikaice ta kalleshi zuciyarta na raya mata abunda ze fito bakinsa.
“Zuwa nayi na sace zuciyar ƴarsa, daga nan sai na sake sace gangar jikinta, na kaita gidana na aje”
Fuskarta da murmushi ta lumshe ido yana girgiza kai. Yau kam Allah ya haɗa ta da Mutum me son raha.
“Ba dan kar na takurawa Sarauniyar ba, dana nemi izinin a rakani ”
Lumshe ido tayi ta buɗe
“Ai duk umarnin da sarki ya bada, da shi baiwa zata yi amfani”
Hannunsa ɗaya yasa aljihu sai ya nuna mata ƙofa da ɗayan.
“Zan so Sarauniya ta wuce gaba, gudun kar bafade yayi mata ba dai-dai ba”
“Amman ai ko a fagen yaƙi, Yarima ne yake sharewa Gimbiya hanya”
Wani irin murmushi Hilal yayi murmushin daya ƙara fito da kyaunsa. Sai kawai ya shiga gaba ta rufa masa baya.
A tare suka isa gurin motar sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro sabbin kuɗi ya miƙa mata.
“Nasan wannan ba ze siye kalamai da kuma tsadadden murmushin ki ba, amman zai iya zama tukuici ga rakiyar da kika min”
Naɗe hannayenta tayi
“Ai wanda ya cika da yaƙi, ya mallake ka duka kai da iyalan ka”
Yasan me take nufi sai kawai yayi murmushi yace
“Zan yi farin ciki idan kika karɓa”
“Ni kuma zan fika farin ciki idan baka cilastani na karɓa ɗin ba, kuma nasan farincikin na naka ne”
Mayarda kuɗin yayi aljihu.
“Na gode da wannan karramawar Kalsoom, ni zan tafi ki kula min da kanki”
“Ni kuma ka kula min da Anty na da duk yarana, kuma ka miƙa min kyakkyawar gaisuwa na a gare su”
Ya buɗe baki
“Baki ce min na kula da kai na ba”
Murmushi tayi masa as respond ta juya ta shige cikin falon, tana mai jin sonsa a zuciyarta.
Shima murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
Ko da ya isa gida, Rashida na zaune falo tana jiransa, duk ta haɗe rai sai kallon agogo take, jikinta na bata ba gurin kai ango yaje ba, gurin wata yaje.
Yana yin sallama ta amsa masa
“Wa'alaikassalam, amman pyar ba gurin kai Amarya kaje ba ko? Gaskiya wannan fitar daga gani gurin wata kaje”
Kusa da ita ya zauna yana murmushi.
“Na gode Allah daya sa matana ta iya karantar mijinta har haka, inda zuciyarki ta raya miki can naje kinsan ba zan iya ɓoye miki ba, ɗa zun ma dan bani da tabbacin zan karɓu ne shiyasa ban faɗa miki inda zanje ba”
Ta masa wani kallo
“Ka karɓu kenan?”
“Sosai ma har da tukuici”
Nan da nan idonta ya cika da hawaye.
“Doctor wasa dai kake”
“Banker da gaske nake, ba tuni nake miki waƙen zan yi aure ba kika ganin kamar wasa nake ba”
“Wallahi baka isa ba, ba a gidan nan ba”
“Toh ai sai ki hana idan gidan ki ne, ni dai tashi ki zubo mana abinci yunwa nake ji”
“Ba zan zubo ba, sai ka koma can kaje ta baka abinci”
Tahir ya kalli Uzair
“Toh kai kana da mak maka wannan aikin ne?”
“Akwai wata ƙawarta ina jin kamar zata iya, amman what if ba ayi nasara ba?”
Tahir ya dafa shi.
“Ka yarda kawai za'ayi nasara, karka sawa kanka wannan”
Kai ya girgiza
“Ni dai ko na haƙura kawai na ƙyaleta”
Ganin yadda Uzair ya tsorata yasa Malamin shiga kwantar masa da hankalin
“Za'ayi nasara, karka damu, ka haɗani da wadda zata kai mata rigar na san yadda zan tsara mata komai”
Shiru Uzair be ce komai ba, shi dai sai tunani yake. Ganin hakan yasa Najeeb yace da Malamin
“Shikenan a fara aikin kawai, zan turo maka dubu ɗari a account ina tunanin zasu isa? Idan ma da wani abu sai ka kira a waya”
“Zasu isa inshallah, amman za a kawo rigar da taɓa sawa, dan da ita zamuyi aiki, kuma ina son ganin yarinyar”
“Ba matsala zuwa gobe duk yadda muka yi zaka ji ni”
Daga haka suka yi sallama, Najeeb yasa direba ya maida malamin. Sannan suka ya dawo falo suka shiga tattauna maganar.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 12*
HILAL POV.
Wanka yayi ya shirya cikin wata gizna, maroon color, sannan ya ɗauki hulla mai kyau ya saka, ya ɗauki agogon hannu ya saka ya feshe jikinshi da turare, sannan ya buɗe wardrobe ya ɗauko sababin kuɗi ya saka a aljihu, sannan ya dawo gaban madubi ya sake kallon kansa, ya tabbatar da kwaliyarsa ta fito, sannan ya ɗauki keys ɗinsa ya saka baƙaƙen takalmi, ya fice.
Ko da ya fito falo, Rashida na gaban dinning tana shirya musu dinner, su Ulfah zagayeta suna nuna mata assignment ɗinsu.
Kusa da ita ya ƙarasa yana leƙon abincin da take zubawa.
“Pyar a zubawa yara nasu nawa sai na dawo mu ci”
“Ina zaka je?”
“Ango zamu je rakawa ba zan daɗe ba”
Juyowa tayi ta kalleshi daga sama har ƙasa, yadda kyau nan nasa ya fito ya bata tsoro. Shi kuma sai yayi kamar be ga kallon da take masa ba sai ya kalli agogon hannunsa.
“Bari naje kar nayi latti, ni kawai suke jira”
Hannu yasa ya rufe idon Ulfah sannan yayi mata kiss a baki, sannan ya nufi ƙofa sai ƙanshi turare yake.
“Allah ya tsare min kai ni dai”
Ta faɗa lokacin da zai fice. Murmushi kawai yayi ya saka kai ya fice.
Motarsa ya shiga yayi horn mai gadi ya buɗe masa, ya hau ti-ti zuciyarsa cike da nishaɗi.
Cikin ƴan mintuna ya isa estate ɗin su Kalsoom. Numbers ɗin gidaje ya riƙa dubawa har ya kai ga number.
Dai-dai gate ɗin ya tsaya yayi horn yayi mai gadin gidan ya leƙo sannan ya buɗe masa, sannan ya shiga harabar gidan yayi parking. Sai ya fito ya nufo mai gadi ya bashi hannu suka gaisa sannan yace
“Dan Allah ko nan ne gidan Alhaji Faruk Kafinta?”
“Eh nan ne”
“Dan Allah mai gidan yana ciki?”
“Eh yana ciki”
“Dan Allah kayi min sallama da shi”
“To wa za'ace masa?”
“Ce masa Doctor Hilal ne”
Da sauri mai gadin ya nufi cikin gidan. Doctor Hilal kuma ya dawo gurin motarsa ya tsaya yana ƙarema gidan kallo.
Hilal ya kusan minti goma tsaye a gurin sannan Abban Kalsoom ya fito, yana ganin Doctor Hilal ya washe baki.
“Maraba da bokan turai, yau likita a gidana na”
Da sauri Hilal ya miƙa masa hannu suka gaisa, har da ɗan risina masa yana murmushi.
“Wai daman nan ne gidan ka?”
“Nan ne kasan abu ga talaka”
Ya faɗa yana dariya, yasan Doctor Hilal sosai dan shine likitan da yake dubashi a duk lokacin daya je asibiti, sai dai Doctor Hilal be waye shi sosai ba, sai yanzu.
“Shigo ciki mana”
A falonsa ya shiga da Hilal ya ɗauko masa lemu da kansa, zai zuba masa Hilal yayi saurin karɓa ya zuba da kansa.
“Ya fama da jama'ah”
Daddy ya faɗa yayin da ya zauna saman kujera.
“Al-hamdulillah da fatar dai na same ku lafiya”
“Lafiya ƙalau, yau dai sai ga likita gidana, ina ji dai hanya ce ta biyo da kai, ni dai nasan Likita be san gidan ba”
Doctor yayi dariya.
“Yanzu ma dalili ne ya kawo ni, akwai wacce na gani naga ta shigo nan gidan”
“To, kuma bata faɗa maka sunanta ba? Ta yiyu ma ƴar maƙota ce”
“A dai yadda nake tunani ƴar nan gidan ce, sunan ta Kalsoom wata doguwa haka”
Daddy yayi murmushi.
“Kalsoom ai ƙanwar ka ce Likita”
Hilal yayi ƙasa da kanshi
“Ina fatar ba'ayi mata miji ba?”
“Ba'a mata ba, amman akwai manema”
“Ina fatar shiga cikin su, amman idan kayi min izini, dan ni da gaske nake yi idan Allah ya yarda”
“Ba ni da matsala Likita, inda har kun dai-dai ta kanku, ni da Kalsoom ai duk mallakin ka ne, tun da ni Patient ɗin ka ne”
Ƙasa Hilal yayi da kansa cike da jindaɗin maganar Daddy, be ɗago ba har sai da Daddy ya tashi yana faɗin
“Bari na kira maka ita”
Daddy na ficewa ya miƙe tsaye ya ƙara karkaɗe shaddarsa, sannan ya zauna a natse yana kallon ƙofa. Sai gata ta fito cikin hijabi tana tafiya a hankali, sallama ta fara masa sannan ta nemi guri ta zauna, tana gaishe shi.
“Lafiya ƙalau, ina fatar Gimbiyar tana nan lafiya”
“Al-Hamdulillah”
“Mashallah, na zo mun gaisa da Daddy ki sai yace ze kira min ke mu gaisa, ina fatar ban takura ki ba, kuma in babu matsala zan so ki gabatar min da kan ki”
“Sunana Kalsoom ni budurwace ina aiki a MTN Service, nan ne gidan mu kuma ina ƙarƙashin kulawar iyaye na ”
Gabansa ya faɗi, jin tana aiki, shi da yake son ƙara aure saboda aikin da matarsa take sai kuma ya sake karo da wata ma'aikaciyar. Sai dai be nuna mata ba, sai kawai yayi murmushi yace
“Mashallah, ni kuma sunan Doctor Hilal Abubakar Mai-lafiya, ina aiki a American Hospital dake nan Kaduna, ina da mata ɗaya da yara uku, ina fatar zan samu karɓuwa, duk da kasancewar na san muna da yawa”
Murmushi kawai tayi masa, ta shiga murza hannunta.
“Ba zan cikaki da surutu ba, dan na fahimci kamar Gimbiyar tawa bata son yawan magana, ni kuma gani kamar wazirin aku, zan nemi alfarma ɗaya zuwa biyu”
“Allah yasa zan iya”
Ta faɗa da murmushi.
“Ina farko ina son ki bani damar zuwa muna gaisawa, bace kullum ba gudun kar na takura miki, amman zan riƙa kwatantawa, sannan ina son ki samin number wayarki”
A take ta karanto masa number, sai da yasa yayi saving sannan ya kalle ta
“Amman fa ni bana son na kira naji User busy, dan ni ina da kishi sosai, ba kamar sauran samarin ki bane”
Nan ma murmushi tayi, sai ya tashi tsaye yana faɗin
“Bari na zo na tafi, kar Daddy yace zan sace masa ƴa”
Sai a lokacin tace
“Ai Daddy ya san be kawo ɓarawo gidansa ba”
“Kar kiyi saurin yanke hukunci, Wallahi sata na zo nayi masa”
A kaikaice ta kalleshi zuciyarta na raya mata abunda ze fito bakinsa.
“Zuwa nayi na sace zuciyar ƴarsa, daga nan sai na sake sace gangar jikinta, na kaita gidana na aje”
Fuskarta da murmushi ta lumshe ido yana girgiza kai. Yau kam Allah ya haɗa ta da Mutum me son raha.
“Ba dan kar na takurawa Sarauniyar ba, dana nemi izinin a rakani ”
Lumshe ido tayi ta buɗe
“Ai duk umarnin da sarki ya bada, da shi baiwa zata yi amfani”
Hannunsa ɗaya yasa aljihu sai ya nuna mata ƙofa da ɗayan.
“Zan so Sarauniya ta wuce gaba, gudun kar bafade yayi mata ba dai-dai ba”
“Amman ai ko a fagen yaƙi, Yarima ne yake sharewa Gimbiya hanya”
Wani irin murmushi Hilal yayi murmushin daya ƙara fito da kyaunsa. Sai kawai ya shiga gaba ta rufa masa baya.
A tare suka isa gurin motar sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro sabbin kuɗi ya miƙa mata.
“Nasan wannan ba ze siye kalamai da kuma tsadadden murmushin ki ba, amman zai iya zama tukuici ga rakiyar da kika min”
Naɗe hannayenta tayi
“Ai wanda ya cika da yaƙi, ya mallake ka duka kai da iyalan ka”
Yasan me take nufi sai kawai yayi murmushi yace
“Zan yi farin ciki idan kika karɓa”
“Ni kuma zan fika farin ciki idan baka cilastani na karɓa ɗin ba, kuma nasan farincikin na naka ne”
Mayarda kuɗin yayi aljihu.
“Na gode da wannan karramawar Kalsoom, ni zan tafi ki kula min da kanki”
“Ni kuma ka kula min da Anty na da duk yarana, kuma ka miƙa min kyakkyawar gaisuwa na a gare su”
Ya buɗe baki
“Baki ce min na kula da kai na ba”
Murmushi tayi masa as respond ta juya ta shige cikin falon, tana mai jin sonsa a zuciyarta.
Shima murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
Ko da ya isa gida, Rashida na zaune falo tana jiransa, duk ta haɗe rai sai kallon agogo take, jikinta na bata ba gurin kai ango yaje ba, gurin wata yaje.
Yana yin sallama ta amsa masa
“Wa'alaikassalam, amman pyar ba gurin kai Amarya kaje ba ko? Gaskiya wannan fitar daga gani gurin wata kaje”
Kusa da ita ya zauna yana murmushi.
“Na gode Allah daya sa matana ta iya karantar mijinta har haka, inda zuciyarki ta raya miki can naje kinsan ba zan iya ɓoye miki ba, ɗa zun ma dan bani da tabbacin zan karɓu ne shiyasa ban faɗa miki inda zanje ba”
Ta masa wani kallo
“Ka karɓu kenan?”
“Sosai ma har da tukuici”
Nan da nan idonta ya cika da hawaye.
“Doctor wasa dai kake”
“Banker da gaske nake, ba tuni nake miki waƙen zan yi aure ba kika ganin kamar wasa nake ba”
“Wallahi baka isa ba, ba a gidan nan ba”
“Toh ai sai ki hana idan gidan ki ne, ni dai tashi ki zubo mana abinci yunwa nake ji”
“Ba zan zubo ba, sai ka koma can kaje ta baka abinci”