Sashe 122
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wannan ciwon yaƙi ya warke, ko dai maci ɗan wawa ne, amman kuma shi ai ba nan yake fitowa ba”
Ta ƙara buɗe gurin da kyau tana dubawa.
“Momee da zafi, Dadee yace na daina bari a na buɗewa, kuma ya ce karna faɗawa kowa zai dake ni idan na faɗa”
“Okay sorry ina duba maka ne, ai idan ya ji nice ba zai dake ka ba”
“Ya ce har da ke, kuma ya ce idan na faɗa abunda yake min sai ya yanke kamar yadda ake yanka rago, ya cinye nama na, ya soye”
Dariya ta yi dan bata ɗauki abun gaske ba.
“Wasa yake maka, ba zai maka komai ba”
“Wallahi yayi rantsuwa, kuma ...”
Ya faɗa cikin muryarsa mai kamar kuka. Yasmee ta juyo da shi, ta zaunar.
“Kuma me Adnan..?”
Sai kawai ya soma matsa ƙwallah.
“Talk to your Mom”
“Yace zai ba ni duka da yawa idan na faɗa”
“Minene”
Ganin kamar ya tsorata yasa ta ƙyalƙyale da dariya ta soma masa cakulkuli, sai ta jashi jikinta ta rumgume.
“Zo mu yi sirri da kai, ba zan faɗawa kowa ba”
Cikin dariyar cakulkulin da take masa ya ce.
“Allah zaki faɗa”
“Ba zan faɗa ba i promise”
“To kawo kunnenki”
Ta matso da kunenta bakinsa. Kaɗan-kaɗan ya raɗa mata.
“Dadee yake sa min abun shi nan, a baya”
Ta ɗago da mamaki tana kallonsa.
“Kai Adnan mu yi gaskiya da kai”
Kamin ya ƙara cewa wani abu mai aikinta ta ƙwalo mata kira.
“Anti Ana sallama”
Sakin sa ta yi ta tashi ta nufi falon, Zuciyarta da ɗayan biyu. Mai gadinta ta samu tsaye a falon riƙe da kwali yana shirin miƙa mata.
“Ga saƙo wani ya kawo yace a ba Alhaji wai hannuna hannunsa”
Karɓa ta yi tana faɗin.
“Okay, wanene?”
“Wallahi ban san shi ba. Ya wuce dai”
Tana karɓa, ya juya ya fice. Ita kuma ta kalli yar aikinta.
“Abincin be yi ba ne?”
“Saura kaɗan”
Juyawa ta yi ta nufi ɗakinta, cike da son jin maganar da Adnan ya soma tsaƙura mata.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *75*
Ko da sha ɗaya na safe ta yi Abbah da Anty Amarya suna katsina, amman basu samu ganin Mai Martaba sai da aka sauko daga sallar azahar, duk da haka kuma be ba da izinin a shigo da su ba sai da ya kira Abdool dan ya sanar da shi. Sai dai yasa an masu masauƙi a gefen sauƙar baƙi, duk abunda ya kamata a yi musu, an musu, abinci ma kusan kala biyar aka jera musu shi drinks, ba a maganarsa.
Mai Martaba be fito ba sai da Abdool ya iso. Sannan suka fito fada tare, ɗaya daga cikin dogarai aka aika ya yi musu iso.
Daga Anty Amarya har Abbah faɗuwa gabansu yake, dukansu zuciyarsu ɗauke take da fargabar kiran da Mai Martaba yake musu. Tun daga ƙofar faɗar Abbah ya tada kai yana kallon irin dukiyar da aka narka a gurin, daman tun farkon shigowarsa gudan ya koma baƙauye, dan duk kuɗin Abbah wasu abubuwan be taɓa ganinsu ba, sai a gidan Mai Martaba, wata ƙila saboda yana sarki ne, shine abunda ya fi ayyanawa a ransa, ga uban sojojin da aka zube a gidan sun matuƙar burgesa, ko ina na gidan cctv cameras ne.
Be ƙara raina kansa ba, sai da aka walgale masa ƙofar faɗa ya shiga. Komai na faɗar ruwan zinari ne, daga kan kujerun har center carpet, da fankar tsaye da ta sama hatta da maɓallin wutar faɗar golden color ne, ga bangon gurin an masa kwalli da wani abu mai kamar zinari, ga wani ƙaton agogon gmt na zinari a gefen faɗar. Alkyabar Mai Martaba ma yau golden ya saka, kamar takalminsa, sai farin rawani da ke kansa. Yarima Abdool na zaune gefensa, cikin shiga ta farar shadda, ya ɗora baƙar hula a kansa, fuskarsa sai wani sheƙi take kamar ango.
Kallo ɗaya Abbah yayi ma Mai Martaba ya yi saurin sadda kansa, saboda wani kwarjini da Mai Martaba ya yi masa, sai gashi ya zube ƙasa yana kwasar gaisuwa, kamar wani ƙaramin talaka.
Mai Martaba be amsa ba sai dai dogaransa ne suke amsa, kamin ya ɗaga musu hannu, ya muku musu izinin fita ba tare da yaƴi magana ba. Tsif ɗakin yai sai sanyi ac dake tsara jikinsu, Abbah dai be sake cewa komai ba, balle kuma Anty Amarya da ko ɗaga kai ba ta yi ba tun da suka shigo.
Tun daga shigowarsu, Abdool ya fahimci Anty Amarya ce mahaifiyar Namra, dan ga kamanin Namra nan shinfiɗe a fuskarta. Mai Martaba yai gyaran murya, wanda hakan ya tatttaro hankalin Abdool ya dawo gurinsa, dan jin shinfiɗar da Mai Martaba zai yi.
“Kai ne mahaifin Namra?”
Da sauri Abbah ya amsa gabansa na faɗuwa, tare da ɗaga hannunsa ɗaya yana bawa Mai Martaba girma.
“Allah ya taimake ka Ni ne”
Mai Martaba ya ɗauki daƙiƙu ashiri da uku kamin ya ɗora da...
“Amman kamaninka da yanayinka be nuna zaka iya aikata abunda ka aikata ba, sam ba kayi kama da mutumen da ya kori ƴarsa saboda ta zaɓi wanda take so ba”
Anty Amarya ta ɗan ɗago kaɗan ta kalli Mai Martaba da kuma Abdool, da take ganin kamar ta san shi.
“Ko kana da dalilin yanke wannan ɗanyin hukuncin?”
Abdool ya tambaya, cike da son jin labarin ta ɓangaren Abbah, wata ƙila ya sha banban da na Namra, idan kuma ya zo ɗaya, Namra ta faɗa masa gaskiya daman be zaci zata masa ƙarya ba, sai dai yana tunanin zata iya ɓoye mata wani abu daga labarinta, ko kuma laifin da ta yi ma Abbah ta.
“Ta zaɓi son ranta ne, bayan kuma na yi mata zaɓi, sannan ina ganin kamar wanda ta zaɓa be dace da ita ba, ta ɓata taraiyyata da mahaifiyar yaron, kuma ta watsa min ƙasa a ido cikin family mu shiyasa na sallama masa ita gaba ɗaya.”
Mai Martaba ya rausayar da kai, tare da kallon ɗansa kaɗan ya ɗauke kai ya mayar gurin Abbah.
“Idan ta kasance kai ne kake son mata fa? Sai kuma iyayenta suka hana ka aurenta har ya zama ka aure ta sai su yi fushi da kai, ya kake tunanin rayuwarka zata kasance?”
“Allah ya taimaki Mai Martaba, ba zan jidaɗi ba”
“Miyasa ka auna ƴarka a muhallinka ba? Kai fa uba ne, ban yi tunanin zaka iya aikata abu kamar wannan, ka kai matsayin da idan wani ya aikata ka kirashi ka yi masa faɗa. Ƴarka ba ƙarar ta kawo a nan ba, kaga yaro gashi nan shi ya ji abunda ya faru ya gurgiza da lamarin har yasa muka kira ka anan”
Mai Martaba na ajewa Abdool ya ɗora.
“Mijin da take aure ya sake ta, saboda ya ce a zubar da ciki ta ƙi, yanzu haka bata cikin garin katsina tana Kaduna, gidan wasu rakuɓe, ba abincin kirki babu abun sha na ƙwarai, kuma kullum kuka take, tana tunanin yadda za tayi ta koma gida har ka karɓe”
Tun da Abdool ya soma magana Anty Amarya ta ɗago tana kallonsa, hawaye sai bin fuskarta suke, daman kullum cikin kukan rashin sanin Halin da Namra take ciki take.
Sai dai zancen sakin da Abdool ya labarta mata ya sanyaya mata rai, hankalinta ya kwanta sosai lokacin data ji dalilin kiran da Mai Martaba yake musu, daman da daɗi tana addu'ah sai yanzu Allah zai amsa mata.
“Kasan abunda nake so da kai?”
Abbah ya girgiza kai tareda ɗaga hannu sama.
“A'a Allah ya taimake ka”
“Ina son ka yafe mata abunda ta yi maka, ko da ba zaka zauna da ita ba, ni zan zauna da ita a matsayin ƴata, daman ni gida na gidan ƴaƴa ne, amman idan ka yafe mata kuma ka saka mata albarka zata ga haske a rayuwarta”
Abbah ya sauke ajiyar zuciya.
“Allah ya taimake ka, ba wai bana son Namra ba ne, kawai ta aikata min abunda ban taɓa mafarkin zata aikata min ba ne, ta zaɓi wani sama da ni, ta bar karatun ta da danginta saboda shi...”
“Wallahi ta yi nadama yanzu, abunda kawai Mai Martaba yake so ka yafe mata mu zamu zauna da ita”
Abdool ya faɗa yana mai saukowa ƙasa ya zauna kusa da Abbah. Anty Amarya ta ɗago ta kalli Abdool.
“Idan har ya yafe mata, ni na fi kowa cancantar na zauna da ƴa ta”
Abbah ya data kai ya kalli Anty Amarya sannan ya kalli Mai Martaba.
“Mamana ta shiga rigarka ta samu alfarmarka, duk da yake ina jiran zuwan wannan ranar da Mamana zata gane kuskure da kuma gangancin abunda ta aikata, na sani wata zata dawo a gareni ko da kuwa mijinta be wulaƙanta ba, nasani wata rana zata gane muhimmancin iyaye, da kuma irin gudumawar da suke badawa a rayuwa, ko da babu saki na sani akwai ciwo, ba fata nake mata ba, amman nasan wata rana zai iya kamata ba duk miji bane yake zama da mace mai wani ciwo, sam bana son na mutu na bar Mamana a cikin halin da ta zaɓi kasancewa a ciki, na sani wata rana zata ratu ba ni, sai dai bana son ta rayu a cikin halin ina fushi da ita, dan nasan ba zata ga dai-dai, ina son Mamana sosai, kuma na yafe mata duniya da lahira”
Mai Martaba yayi murmushin ƙasaita irin nasu na manya.
“Lallai kana son ƙulla abota da ni”
Abdool ma yayi dariya mai cike da farinciki da har suka bayyana haƙoransa da kuma dimples ɗinsa ya ce
“Ni da Mai Martaba muna godiya”
Anty Amarya ta share hawayen idonta tana murmushi.
“Dan Allah idan tana cikin gidan nan ku faɗa mata Mahaifinta ya yafe mata, ta fito mu ganta”
“Bata tare da mu, tana can a Kaduna a wani gida rakuɓe, bata san Mai Martaba ya aika maka ba, ni ne kawai na ga tana cikin matsala kuma na san irin matsalar da rashin zama kusa da iyaye yake haifarwa”
“Allah ya maka albarka Allah ya raya maka iyalanka, ya cika maka burinka, ya taimake ka akan dukan lamurranka, na gode sosai yadda ki yi wannan jihadin Allah ya baka abunda kake so”
Ta ƙara buɗe gurin da kyau tana dubawa.
“Momee da zafi, Dadee yace na daina bari a na buɗewa, kuma ya ce karna faɗawa kowa zai dake ni idan na faɗa”
“Okay sorry ina duba maka ne, ai idan ya ji nice ba zai dake ka ba”
“Ya ce har da ke, kuma ya ce idan na faɗa abunda yake min sai ya yanke kamar yadda ake yanka rago, ya cinye nama na, ya soye”
Dariya ta yi dan bata ɗauki abun gaske ba.
“Wasa yake maka, ba zai maka komai ba”
“Wallahi yayi rantsuwa, kuma ...”
Ya faɗa cikin muryarsa mai kamar kuka. Yasmee ta juyo da shi, ta zaunar.
“Kuma me Adnan..?”
Sai kawai ya soma matsa ƙwallah.
“Talk to your Mom”
“Yace zai ba ni duka da yawa idan na faɗa”
“Minene”
Ganin kamar ya tsorata yasa ta ƙyalƙyale da dariya ta soma masa cakulkuli, sai ta jashi jikinta ta rumgume.
“Zo mu yi sirri da kai, ba zan faɗawa kowa ba”
Cikin dariyar cakulkulin da take masa ya ce.
“Allah zaki faɗa”
“Ba zan faɗa ba i promise”
“To kawo kunnenki”
Ta matso da kunenta bakinsa. Kaɗan-kaɗan ya raɗa mata.
“Dadee yake sa min abun shi nan, a baya”
Ta ɗago da mamaki tana kallonsa.
“Kai Adnan mu yi gaskiya da kai”
Kamin ya ƙara cewa wani abu mai aikinta ta ƙwalo mata kira.
“Anti Ana sallama”
Sakin sa ta yi ta tashi ta nufi falon, Zuciyarta da ɗayan biyu. Mai gadinta ta samu tsaye a falon riƙe da kwali yana shirin miƙa mata.
“Ga saƙo wani ya kawo yace a ba Alhaji wai hannuna hannunsa”
Karɓa ta yi tana faɗin.
“Okay, wanene?”
“Wallahi ban san shi ba. Ya wuce dai”
Tana karɓa, ya juya ya fice. Ita kuma ta kalli yar aikinta.
“Abincin be yi ba ne?”
“Saura kaɗan”
Juyawa ta yi ta nufi ɗakinta, cike da son jin maganar da Adnan ya soma tsaƙura mata.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *75*
Ko da sha ɗaya na safe ta yi Abbah da Anty Amarya suna katsina, amman basu samu ganin Mai Martaba sai da aka sauko daga sallar azahar, duk da haka kuma be ba da izinin a shigo da su ba sai da ya kira Abdool dan ya sanar da shi. Sai dai yasa an masu masauƙi a gefen sauƙar baƙi, duk abunda ya kamata a yi musu, an musu, abinci ma kusan kala biyar aka jera musu shi drinks, ba a maganarsa.
Mai Martaba be fito ba sai da Abdool ya iso. Sannan suka fito fada tare, ɗaya daga cikin dogarai aka aika ya yi musu iso.
Daga Anty Amarya har Abbah faɗuwa gabansu yake, dukansu zuciyarsu ɗauke take da fargabar kiran da Mai Martaba yake musu. Tun daga ƙofar faɗar Abbah ya tada kai yana kallon irin dukiyar da aka narka a gurin, daman tun farkon shigowarsa gudan ya koma baƙauye, dan duk kuɗin Abbah wasu abubuwan be taɓa ganinsu ba, sai a gidan Mai Martaba, wata ƙila saboda yana sarki ne, shine abunda ya fi ayyanawa a ransa, ga uban sojojin da aka zube a gidan sun matuƙar burgesa, ko ina na gidan cctv cameras ne.
Be ƙara raina kansa ba, sai da aka walgale masa ƙofar faɗa ya shiga. Komai na faɗar ruwan zinari ne, daga kan kujerun har center carpet, da fankar tsaye da ta sama hatta da maɓallin wutar faɗar golden color ne, ga bangon gurin an masa kwalli da wani abu mai kamar zinari, ga wani ƙaton agogon gmt na zinari a gefen faɗar. Alkyabar Mai Martaba ma yau golden ya saka, kamar takalminsa, sai farin rawani da ke kansa. Yarima Abdool na zaune gefensa, cikin shiga ta farar shadda, ya ɗora baƙar hula a kansa, fuskarsa sai wani sheƙi take kamar ango.
Kallo ɗaya Abbah yayi ma Mai Martaba ya yi saurin sadda kansa, saboda wani kwarjini da Mai Martaba ya yi masa, sai gashi ya zube ƙasa yana kwasar gaisuwa, kamar wani ƙaramin talaka.
Mai Martaba be amsa ba sai dai dogaransa ne suke amsa, kamin ya ɗaga musu hannu, ya muku musu izinin fita ba tare da yaƴi magana ba. Tsif ɗakin yai sai sanyi ac dake tsara jikinsu, Abbah dai be sake cewa komai ba, balle kuma Anty Amarya da ko ɗaga kai ba ta yi ba tun da suka shigo.
Tun daga shigowarsu, Abdool ya fahimci Anty Amarya ce mahaifiyar Namra, dan ga kamanin Namra nan shinfiɗe a fuskarta. Mai Martaba yai gyaran murya, wanda hakan ya tatttaro hankalin Abdool ya dawo gurinsa, dan jin shinfiɗar da Mai Martaba zai yi.
“Kai ne mahaifin Namra?”
Da sauri Abbah ya amsa gabansa na faɗuwa, tare da ɗaga hannunsa ɗaya yana bawa Mai Martaba girma.
“Allah ya taimake ka Ni ne”
Mai Martaba ya ɗauki daƙiƙu ashiri da uku kamin ya ɗora da...
“Amman kamaninka da yanayinka be nuna zaka iya aikata abunda ka aikata ba, sam ba kayi kama da mutumen da ya kori ƴarsa saboda ta zaɓi wanda take so ba”
Anty Amarya ta ɗan ɗago kaɗan ta kalli Mai Martaba da kuma Abdool, da take ganin kamar ta san shi.
“Ko kana da dalilin yanke wannan ɗanyin hukuncin?”
Abdool ya tambaya, cike da son jin labarin ta ɓangaren Abbah, wata ƙila ya sha banban da na Namra, idan kuma ya zo ɗaya, Namra ta faɗa masa gaskiya daman be zaci zata masa ƙarya ba, sai dai yana tunanin zata iya ɓoye mata wani abu daga labarinta, ko kuma laifin da ta yi ma Abbah ta.
“Ta zaɓi son ranta ne, bayan kuma na yi mata zaɓi, sannan ina ganin kamar wanda ta zaɓa be dace da ita ba, ta ɓata taraiyyata da mahaifiyar yaron, kuma ta watsa min ƙasa a ido cikin family mu shiyasa na sallama masa ita gaba ɗaya.”
Mai Martaba ya rausayar da kai, tare da kallon ɗansa kaɗan ya ɗauke kai ya mayar gurin Abbah.
“Idan ta kasance kai ne kake son mata fa? Sai kuma iyayenta suka hana ka aurenta har ya zama ka aure ta sai su yi fushi da kai, ya kake tunanin rayuwarka zata kasance?”
“Allah ya taimaki Mai Martaba, ba zan jidaɗi ba”
“Miyasa ka auna ƴarka a muhallinka ba? Kai fa uba ne, ban yi tunanin zaka iya aikata abu kamar wannan, ka kai matsayin da idan wani ya aikata ka kirashi ka yi masa faɗa. Ƴarka ba ƙarar ta kawo a nan ba, kaga yaro gashi nan shi ya ji abunda ya faru ya gurgiza da lamarin har yasa muka kira ka anan”
Mai Martaba na ajewa Abdool ya ɗora.
“Mijin da take aure ya sake ta, saboda ya ce a zubar da ciki ta ƙi, yanzu haka bata cikin garin katsina tana Kaduna, gidan wasu rakuɓe, ba abincin kirki babu abun sha na ƙwarai, kuma kullum kuka take, tana tunanin yadda za tayi ta koma gida har ka karɓe”
Tun da Abdool ya soma magana Anty Amarya ta ɗago tana kallonsa, hawaye sai bin fuskarta suke, daman kullum cikin kukan rashin sanin Halin da Namra take ciki take.
Sai dai zancen sakin da Abdool ya labarta mata ya sanyaya mata rai, hankalinta ya kwanta sosai lokacin data ji dalilin kiran da Mai Martaba yake musu, daman da daɗi tana addu'ah sai yanzu Allah zai amsa mata.
“Kasan abunda nake so da kai?”
Abbah ya girgiza kai tareda ɗaga hannu sama.
“A'a Allah ya taimake ka”
“Ina son ka yafe mata abunda ta yi maka, ko da ba zaka zauna da ita ba, ni zan zauna da ita a matsayin ƴata, daman ni gida na gidan ƴaƴa ne, amman idan ka yafe mata kuma ka saka mata albarka zata ga haske a rayuwarta”
Abbah ya sauke ajiyar zuciya.
“Allah ya taimake ka, ba wai bana son Namra ba ne, kawai ta aikata min abunda ban taɓa mafarkin zata aikata min ba ne, ta zaɓi wani sama da ni, ta bar karatun ta da danginta saboda shi...”
“Wallahi ta yi nadama yanzu, abunda kawai Mai Martaba yake so ka yafe mata mu zamu zauna da ita”
Abdool ya faɗa yana mai saukowa ƙasa ya zauna kusa da Abbah. Anty Amarya ta ɗago ta kalli Abdool.
“Idan har ya yafe mata, ni na fi kowa cancantar na zauna da ƴa ta”
Abbah ya data kai ya kalli Anty Amarya sannan ya kalli Mai Martaba.
“Mamana ta shiga rigarka ta samu alfarmarka, duk da yake ina jiran zuwan wannan ranar da Mamana zata gane kuskure da kuma gangancin abunda ta aikata, na sani wata zata dawo a gareni ko da kuwa mijinta be wulaƙanta ba, nasani wata rana zata gane muhimmancin iyaye, da kuma irin gudumawar da suke badawa a rayuwa, ko da babu saki na sani akwai ciwo, ba fata nake mata ba, amman nasan wata rana zai iya kamata ba duk miji bane yake zama da mace mai wani ciwo, sam bana son na mutu na bar Mamana a cikin halin da ta zaɓi kasancewa a ciki, na sani wata rana zata ratu ba ni, sai dai bana son ta rayu a cikin halin ina fushi da ita, dan nasan ba zata ga dai-dai, ina son Mamana sosai, kuma na yafe mata duniya da lahira”
Mai Martaba yayi murmushin ƙasaita irin nasu na manya.
“Lallai kana son ƙulla abota da ni”
Abdool ma yayi dariya mai cike da farinciki da har suka bayyana haƙoransa da kuma dimples ɗinsa ya ce
“Ni da Mai Martaba muna godiya”
Anty Amarya ta share hawayen idonta tana murmushi.
“Dan Allah idan tana cikin gidan nan ku faɗa mata Mahaifinta ya yafe mata, ta fito mu ganta”
“Bata tare da mu, tana can a Kaduna a wani gida rakuɓe, bata san Mai Martaba ya aika maka ba, ni ne kawai na ga tana cikin matsala kuma na san irin matsalar da rashin zama kusa da iyaye yake haifarwa”
“Allah ya maka albarka Allah ya raya maka iyalanka, ya cika maka burinka, ya taimake ka akan dukan lamurranka, na gode sosai yadda ki yi wannan jihadin Allah ya baka abunda kake so”