Sashe 20
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbah be kula jikokinta da suke falon ba ya hauta da faɗa, daman haka yake idan ya tashi matsifa babu ruwanshi da wanda yake zaune. Ta inda Hajiya barau take shiga bata nan take fita ba, tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta kai ga fasa kuka tana faɗin
“Ni Wallahi ba da wata niya nayi ba, kuma tun da daɗewa mukayi wannan maganar fa”
“Ni dai na faɗa miki, ki iya bakin ki ko kuma duk abunda ya same ki ke kika ja, Namra dai kin kusa jikanya da ita, dan haka ba dai-dai bane ki zauna kina faɗan mugaye kalamai akan ƴarki”
Kuka take sosai tana faɗar wai ƙazafi aka mata, har jikokinta suka dafata suna bata haƙuri. Sannan Abbah ya tashi ya nufi part ɗinsa.
Namra na kwance jikin Anty Amarya tana sauke ajiyar zuciya Maryam tace
“Wallahi Allah sai ya saka miki daga Ammy har tsohuwar makirar can Hajiya”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ke matar uwanki zaki cewa makira ko dan darajar tsufanta kya ce mata haka, balle tana auren uban? Kin gani ina ja miki kunne akan rashin kunyar nan kina ƙarawa ko? Wallahi kika kai ni ƙul sai na ɓata miki rai”
Miƙewa tayi tsaye cikin fushi ta miƙawa Namra takardar dake hannunta.
“Ke ni dai karɓi, Asim ya zo baki nan yace a baki”
Da sauri Namra ta ɗago ta kai hannu ta karɓi takardar, sai ta share hawayenta ta tashi ta nufi ɗakinta, zuciyarta cike da zazzanar son sanin abunda takardar ta ƙumsa.
__________________________
Wannan shafi na ƴan TASKAR KHADEEJA CANDY ne, da CLASSIC LADIES, tare da NAMRA FANS GROUP. I really appreciate your comments 💖💖💖
https://chat.whatsapp.com/LHd6gwdQQWZKNeHU9z4qf0
Masu tambayan grp ga link nan. Amman ban da maza ❌
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 16*
Natsuwa tayi sosai ta tattara dukan hankalinta ta mai da gurin takardar, sannan ta buɗe ta soma karantawa.
_SALAM_
MY DEAR NAMRA.
Na zo gidan ku ance min baki nan, na kira wayarki ban samu ba, mahaifiyata kuma ta shaida min kina nema ma, ban san ta yadda zan iya ganin ki ba amman ga sabon number waya na ki kira ni dan Allah.
Urs ASIM.
Wani dogon ajiyar zuciya ta sauke, ta rumgume takardar a ƙirjinta ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta ɗauki daƙiƙa goma zuwa shabiyar kamin ta buɗe idon, ta tashi ta nufi ɗakin Maryam.
Dariya ta tararda Maryam na ƙyalƙyala kamar wata sabuwar mahaukaciya, har ta zauna kusa da ita bata san ta zauna ba, tana taɓa ta ta zabura.
“Wayyo Allah na”
“Ke lafiyan ki?”
“Wallahi wani littafi ne nake karantawa mai shegen dariya”
“Littafi kuma ai ke Allah be raba ki da karatun littafai ba”
“Wallahi Anty Namra yayi daɗi kamar me, da zaki karanta kema da kin sha dariya”
“Idan na samu time zan karanta, meye sunan littafin?”
“Noor na Khadeeja Candy”
“Okay ni dai ara min wayarki wani abu”
“Ke dai ce zaki kira Asim ba wai kiyi wani abu ba”
“Naji ni dai bani”
Sai da tayi saving ɗin page ɗin, sannan ta miƙa mata wayar tana zolayarta. Namra dai bata ce mata komai ba ta tashi ta fice tana faɗin.
“Ina fatar da Akwai kuɗi a ciki”
“Kai kaji ki da wata magana, manyan Babe's irin zasu zauna waya ba kati, taf mune tare da manyan samarin garin nan fa, kin san ko dan karya dole a saka mana manyan kati ”
Da dariya Namra ta fice, ta koma ɗakinta. Takardar ta ɗauko ta saka Number ta danna kira. Ringing biyu zuwa uku yayi picking da sallama.
Sai da ta lumshe ido ta buɗe da murmushi sannan ta amsa masa.
“Wa'alaikassalam. Asim”
“Namra...”
Daga cikin wayar tana jin lokacin daya sauke ajiyar zuciya, sannan yace
“Namra wai Abban ki ya yarda na aure ki?”
Kai ta ɗaga masa kamar yana gabanta, hawaye suka silalo mata.
“Ya yarda Asim, shiyasa na neme ka”
“Alhamdulillah”
“Ina kaje Asim? Ashe zaka iya tafiya wani guri ka bar ni?”
“Namra idan mun haɗu zamu yi magana”
“Yaushe zaka zo?”
“Ba zan iya zuwa gidan ku da sunan hira ba, sai dai mu haɗa ta layin su Azeema”
“Okay gobe da ƙarfe tara dan Allah”
“Allah ya kai mu I Love You”
“I Love You More”
Daga haka ya kashe wayar. Sai ta rumgume phone ɗin tana murmushi tare da hawaye.
KALSOOM POV.
Kusan kullum sai Doc. Hilal ya kirata a waya sun gaisa, sai dai fira ce be cika zuwa ba sai jefi-jefi. Sau biyu ya taɓa kawo mata ƴaƴansa suka gaisheta ita kuma tayi musu goma na arziki.
Ana sauran sati biyu biki Doc. Hilal ya nemi ta bashi list ɗin abubuwan da zata yi na biki. Bata rubuta wasu abubuwa masu yawa ba, bayan abubuwan da al'ada ta tana da.
Batayi wata hidima ba duk da kasancewar ƙannenta sun so tayi, amman bata biye musu ba, wai ita ta girmi wannan yanzu.
Kala kusan arba'in da huɗu yayi mata, duk masu kyau da ɗaukar hankali, kowa ya gani sai ya yaba, wasu na faɗin haƙurin da tayi yanzu zata ci riba.
Ranar laraba aka saka amarya lalle a daren ranar akayi wankin amarya, washegari alhamis akayi ƙunshi da kitso, friday akayi walima, Assabar aka ɗaura aure Kalsoom da Doc Hilal.
Daddy yayi mata nasiha mai ratsa jiki, gwaggwanin suka mata jan kunne akan rayuwar gidan aure kamin Momy ta ɗora da nata. Kuka sosai Kalsoom tayi a lokacin da aka fito da ita za a saka ta mota zuwa gidan mijinta. Duk wanda ya gani zai yi zaton bata son auren ne.
Da ƙafar dama ta shiga gidan aurenta tana ƙorar shedan kamar yadda Momy ta faɗa mata. Sai da aka zaunar da ita a saman gadon aurenta sannan ta tsagaita kukan.
Batayi zaman minti ashirin ba abokan ango suka shigo tare da ango, sai zolayarsa suke, anyi siyen baki da wasu abubuwa da al'ada ta tanada sannan suka yi musu addu'ar zama lafiya.
Har gurin ƙofa Hilal ya raka abokansa, yayi ma ƴan'uwan amarya da wasu daga abokanta sallama sannan ya rufe ƙofar.
A maimakon ya koma ɗakin Kalsoom, sai ya nufi ɗakin Rashida dan duba halin da take ciki.
Zaune ya tararda ita ƙasan carpet tana wani irin kuka kamar ranta ze cire, wata cousin ɗinta na kusa da ita tana bata haƙuri.
“Habiba ɗan bamu waje”
Ya ƙarasa faɗar yayinda yake zaunawa kusa da ita, janta yayi izuwa ƙirjinsa ya rumgume ta sosai.
“Shiiiiiiiii. Wannan hawayen ban ga dalilin zubar da su ba Ammyn Rafiq, kin san ba ɗan bana son ki bane yasa nayi aure sai dan sauwaƙe miki wasu abubuwan, a maimakon kiyi farin ciki sai kuma kiyi kuka?”
“Ina son Hilal ina kishin naga wata a tare da kai, zan iya mutuwa Hilal”
Ta faɗa tana ƙara narke masa a jiki. Saman kanta ya shafa ya sumbanci shi sannan yace
“Allah ya sassauta miki wannan kishin Pyar, I Love You so much amman ina son ki so abunda nake so”
Kuka tayi sosai har sai da maƙoshinta ya bushe sannan ta sassautama kanta, har kuma lokacin Hilal na rumgume da ita yana rarrashinta.
“Pyar”
Ta ɗago kai ta kalleshi da kumburarin idanuwanta.
“Karki sa damuwa a ranki kin ji? Mijinki yana son ki matuƙa, kuma baya da niyar cutar da ke”
Ta ɗaga daga jikinsa.
“Tashi kaje kar na shiga mata haƙƙi”
“Zanje amman sai kin yi min alƙawarin zakiyi bachi!”
“Zan yi”
Babbar rigarsa ya cire, da ita ya gyara mata fuskarta, ya goge majinar data ɓata mata gaban riga sannan ya kai bakinsa cikin nata yana kiss.
Ya ɗauki lokaci mai tsawo yana kiss ɗinta da shafa wani ɓangare na jikinta, har sai da ya tabbatar ya kashe mata jiki, sannan ya ɗaga ya kalleta.
“Good night Pyar”
“Good night”
Sai ya sumbaci goshinta.
“Dream me i love you”
Ɗan murmushi ta sakar masa kaɗan. Sannan ta sake shi ya tashi, ya baro mata ɗakin zuciyarsa cike da zumuɗin zuwa gurin Amaryarshi.
Da sallama ya shiga ɗakin yana murmushi, sai ya zauna kusa da ita ya kai hannu ya yaye lulluɓin dake kanta.
“Wannan Amaryan bakinta da tsada yake, har ta kasa amsa sallamar angonta”
Hawayen daya gani a fuskarta ya tada hankalinsa. Dan be yi zaton macen data kai kamar Kalsoom idan anyi mata aure a zamanin nan zatayi kuka ba.
“Wannan hawayen na minene My Queen? Ashe yau ba ranar farincikin mu bace? Ai kamata yayi mu gode Allah ko?”
Ita kanta bata san hawayen minene take ba, na farincikin yau Allah ya gwada mata aurenta, ko kuma na yanayin da take ciki na baƙincikin rabuwa da iyayenta.
Matsawa yayi daf da ita sai ya kai tattausan hannunsa ya share mata hawayen, ya kwantar da ita jikinasa, yasa babban yatsansa da mai bi mata yana mata saƙa a jiki.
“Ranar yau ba ranar kuka bace ranar murna ne, ranace da zaki gode Allah kuma ki shirya karɓar angonki da kyakkyawar tarba”
Notse kanta tayi cikin ƙirjinsa, jikinta na amsa saƙon da ƴan yatsunsa suke kai mata. Tana jin wasan ya canja salo sai ta zame jikinta, idonta cike da nauyin kallonsa.
Murmushi yayi yana wani lumshe ido yana buɗe, sannan ya janyo ledar dake gefensu ya buɗe ya ɓalle lemun dake cikin kwali ya ɗauko cup ya zuba mata. Duk yadda taso ta ci da kanta ƙin yarda yayi a dole ta haƙura yayi feeding ɗinta, ba dan tana jindaɗin yadda yake bata ba, abun ka da wanda be saba ba.
Bayan sun gama, ya riƙa hannun tana mursa lallen dake hannu tare da yaba.
“Amman wanda tayi miki lallen nan ta iya lalle gaskiya, yayi kyau sosai”
Yadda yake taɓa hannun nata yasa tsigar jikinta tashi. Duka hannayensa yasa yana luddar hannun nata, a ɗan space ɗin dake tsakanin fingers ɗinta yasa one finger ɗinsa yana mata tafiyar tsusa, sai kallon yanayinta yake, gaba ɗaya idonsa sun koma kamar ba nashi ba.
Janye hannunta tayi ta miƙe tsaye.
“Bari mu tashi mu yi sallah”
“Ni Wallahi ba da wata niya nayi ba, kuma tun da daɗewa mukayi wannan maganar fa”
“Ni dai na faɗa miki, ki iya bakin ki ko kuma duk abunda ya same ki ke kika ja, Namra dai kin kusa jikanya da ita, dan haka ba dai-dai bane ki zauna kina faɗan mugaye kalamai akan ƴarki”
Kuka take sosai tana faɗar wai ƙazafi aka mata, har jikokinta suka dafata suna bata haƙuri. Sannan Abbah ya tashi ya nufi part ɗinsa.
Namra na kwance jikin Anty Amarya tana sauke ajiyar zuciya Maryam tace
“Wallahi Allah sai ya saka miki daga Ammy har tsohuwar makirar can Hajiya”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ke matar uwanki zaki cewa makira ko dan darajar tsufanta kya ce mata haka, balle tana auren uban? Kin gani ina ja miki kunne akan rashin kunyar nan kina ƙarawa ko? Wallahi kika kai ni ƙul sai na ɓata miki rai”
Miƙewa tayi tsaye cikin fushi ta miƙawa Namra takardar dake hannunta.
“Ke ni dai karɓi, Asim ya zo baki nan yace a baki”
Da sauri Namra ta ɗago ta kai hannu ta karɓi takardar, sai ta share hawayenta ta tashi ta nufi ɗakinta, zuciyarta cike da zazzanar son sanin abunda takardar ta ƙumsa.
__________________________
Wannan shafi na ƴan TASKAR KHADEEJA CANDY ne, da CLASSIC LADIES, tare da NAMRA FANS GROUP. I really appreciate your comments 💖💖💖
https://chat.whatsapp.com/LHd6gwdQQWZKNeHU9z4qf0
Masu tambayan grp ga link nan. Amman ban da maza ❌
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 16*
Natsuwa tayi sosai ta tattara dukan hankalinta ta mai da gurin takardar, sannan ta buɗe ta soma karantawa.
_SALAM_
MY DEAR NAMRA.
Na zo gidan ku ance min baki nan, na kira wayarki ban samu ba, mahaifiyata kuma ta shaida min kina nema ma, ban san ta yadda zan iya ganin ki ba amman ga sabon number waya na ki kira ni dan Allah.
Urs ASIM.
Wani dogon ajiyar zuciya ta sauke, ta rumgume takardar a ƙirjinta ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta ɗauki daƙiƙa goma zuwa shabiyar kamin ta buɗe idon, ta tashi ta nufi ɗakin Maryam.
Dariya ta tararda Maryam na ƙyalƙyala kamar wata sabuwar mahaukaciya, har ta zauna kusa da ita bata san ta zauna ba, tana taɓa ta ta zabura.
“Wayyo Allah na”
“Ke lafiyan ki?”
“Wallahi wani littafi ne nake karantawa mai shegen dariya”
“Littafi kuma ai ke Allah be raba ki da karatun littafai ba”
“Wallahi Anty Namra yayi daɗi kamar me, da zaki karanta kema da kin sha dariya”
“Idan na samu time zan karanta, meye sunan littafin?”
“Noor na Khadeeja Candy”
“Okay ni dai ara min wayarki wani abu”
“Ke dai ce zaki kira Asim ba wai kiyi wani abu ba”
“Naji ni dai bani”
Sai da tayi saving ɗin page ɗin, sannan ta miƙa mata wayar tana zolayarta. Namra dai bata ce mata komai ba ta tashi ta fice tana faɗin.
“Ina fatar da Akwai kuɗi a ciki”
“Kai kaji ki da wata magana, manyan Babe's irin zasu zauna waya ba kati, taf mune tare da manyan samarin garin nan fa, kin san ko dan karya dole a saka mana manyan kati ”
Da dariya Namra ta fice, ta koma ɗakinta. Takardar ta ɗauko ta saka Number ta danna kira. Ringing biyu zuwa uku yayi picking da sallama.
Sai da ta lumshe ido ta buɗe da murmushi sannan ta amsa masa.
“Wa'alaikassalam. Asim”
“Namra...”
Daga cikin wayar tana jin lokacin daya sauke ajiyar zuciya, sannan yace
“Namra wai Abban ki ya yarda na aure ki?”
Kai ta ɗaga masa kamar yana gabanta, hawaye suka silalo mata.
“Ya yarda Asim, shiyasa na neme ka”
“Alhamdulillah”
“Ina kaje Asim? Ashe zaka iya tafiya wani guri ka bar ni?”
“Namra idan mun haɗu zamu yi magana”
“Yaushe zaka zo?”
“Ba zan iya zuwa gidan ku da sunan hira ba, sai dai mu haɗa ta layin su Azeema”
“Okay gobe da ƙarfe tara dan Allah”
“Allah ya kai mu I Love You”
“I Love You More”
Daga haka ya kashe wayar. Sai ta rumgume phone ɗin tana murmushi tare da hawaye.
KALSOOM POV.
Kusan kullum sai Doc. Hilal ya kirata a waya sun gaisa, sai dai fira ce be cika zuwa ba sai jefi-jefi. Sau biyu ya taɓa kawo mata ƴaƴansa suka gaisheta ita kuma tayi musu goma na arziki.
Ana sauran sati biyu biki Doc. Hilal ya nemi ta bashi list ɗin abubuwan da zata yi na biki. Bata rubuta wasu abubuwa masu yawa ba, bayan abubuwan da al'ada ta tana da.
Batayi wata hidima ba duk da kasancewar ƙannenta sun so tayi, amman bata biye musu ba, wai ita ta girmi wannan yanzu.
Kala kusan arba'in da huɗu yayi mata, duk masu kyau da ɗaukar hankali, kowa ya gani sai ya yaba, wasu na faɗin haƙurin da tayi yanzu zata ci riba.
Ranar laraba aka saka amarya lalle a daren ranar akayi wankin amarya, washegari alhamis akayi ƙunshi da kitso, friday akayi walima, Assabar aka ɗaura aure Kalsoom da Doc Hilal.
Daddy yayi mata nasiha mai ratsa jiki, gwaggwanin suka mata jan kunne akan rayuwar gidan aure kamin Momy ta ɗora da nata. Kuka sosai Kalsoom tayi a lokacin da aka fito da ita za a saka ta mota zuwa gidan mijinta. Duk wanda ya gani zai yi zaton bata son auren ne.
Da ƙafar dama ta shiga gidan aurenta tana ƙorar shedan kamar yadda Momy ta faɗa mata. Sai da aka zaunar da ita a saman gadon aurenta sannan ta tsagaita kukan.
Batayi zaman minti ashirin ba abokan ango suka shigo tare da ango, sai zolayarsa suke, anyi siyen baki da wasu abubuwa da al'ada ta tanada sannan suka yi musu addu'ar zama lafiya.
Har gurin ƙofa Hilal ya raka abokansa, yayi ma ƴan'uwan amarya da wasu daga abokanta sallama sannan ya rufe ƙofar.
A maimakon ya koma ɗakin Kalsoom, sai ya nufi ɗakin Rashida dan duba halin da take ciki.
Zaune ya tararda ita ƙasan carpet tana wani irin kuka kamar ranta ze cire, wata cousin ɗinta na kusa da ita tana bata haƙuri.
“Habiba ɗan bamu waje”
Ya ƙarasa faɗar yayinda yake zaunawa kusa da ita, janta yayi izuwa ƙirjinsa ya rumgume ta sosai.
“Shiiiiiiiii. Wannan hawayen ban ga dalilin zubar da su ba Ammyn Rafiq, kin san ba ɗan bana son ki bane yasa nayi aure sai dan sauwaƙe miki wasu abubuwan, a maimakon kiyi farin ciki sai kuma kiyi kuka?”
“Ina son Hilal ina kishin naga wata a tare da kai, zan iya mutuwa Hilal”
Ta faɗa tana ƙara narke masa a jiki. Saman kanta ya shafa ya sumbanci shi sannan yace
“Allah ya sassauta miki wannan kishin Pyar, I Love You so much amman ina son ki so abunda nake so”
Kuka tayi sosai har sai da maƙoshinta ya bushe sannan ta sassautama kanta, har kuma lokacin Hilal na rumgume da ita yana rarrashinta.
“Pyar”
Ta ɗago kai ta kalleshi da kumburarin idanuwanta.
“Karki sa damuwa a ranki kin ji? Mijinki yana son ki matuƙa, kuma baya da niyar cutar da ke”
Ta ɗaga daga jikinsa.
“Tashi kaje kar na shiga mata haƙƙi”
“Zanje amman sai kin yi min alƙawarin zakiyi bachi!”
“Zan yi”
Babbar rigarsa ya cire, da ita ya gyara mata fuskarta, ya goge majinar data ɓata mata gaban riga sannan ya kai bakinsa cikin nata yana kiss.
Ya ɗauki lokaci mai tsawo yana kiss ɗinta da shafa wani ɓangare na jikinta, har sai da ya tabbatar ya kashe mata jiki, sannan ya ɗaga ya kalleta.
“Good night Pyar”
“Good night”
Sai ya sumbaci goshinta.
“Dream me i love you”
Ɗan murmushi ta sakar masa kaɗan. Sannan ta sake shi ya tashi, ya baro mata ɗakin zuciyarsa cike da zumuɗin zuwa gurin Amaryarshi.
Da sallama ya shiga ɗakin yana murmushi, sai ya zauna kusa da ita ya kai hannu ya yaye lulluɓin dake kanta.
“Wannan Amaryan bakinta da tsada yake, har ta kasa amsa sallamar angonta”
Hawayen daya gani a fuskarta ya tada hankalinsa. Dan be yi zaton macen data kai kamar Kalsoom idan anyi mata aure a zamanin nan zatayi kuka ba.
“Wannan hawayen na minene My Queen? Ashe yau ba ranar farincikin mu bace? Ai kamata yayi mu gode Allah ko?”
Ita kanta bata san hawayen minene take ba, na farincikin yau Allah ya gwada mata aurenta, ko kuma na yanayin da take ciki na baƙincikin rabuwa da iyayenta.
Matsawa yayi daf da ita sai ya kai tattausan hannunsa ya share mata hawayen, ya kwantar da ita jikinasa, yasa babban yatsansa da mai bi mata yana mata saƙa a jiki.
“Ranar yau ba ranar kuka bace ranar murna ne, ranace da zaki gode Allah kuma ki shirya karɓar angonki da kyakkyawar tarba”
Notse kanta tayi cikin ƙirjinsa, jikinta na amsa saƙon da ƴan yatsunsa suke kai mata. Tana jin wasan ya canja salo sai ta zame jikinta, idonta cike da nauyin kallonsa.
Murmushi yayi yana wani lumshe ido yana buɗe, sannan ya janyo ledar dake gefensu ya buɗe ya ɓalle lemun dake cikin kwali ya ɗauko cup ya zuba mata. Duk yadda taso ta ci da kanta ƙin yarda yayi a dole ta haƙura yayi feeding ɗinta, ba dan tana jindaɗin yadda yake bata ba, abun ka da wanda be saba ba.
Bayan sun gama, ya riƙa hannun tana mursa lallen dake hannu tare da yaba.
“Amman wanda tayi miki lallen nan ta iya lalle gaskiya, yayi kyau sosai”
Yadda yake taɓa hannun nata yasa tsigar jikinta tashi. Duka hannayensa yasa yana luddar hannun nata, a ɗan space ɗin dake tsakanin fingers ɗinta yasa one finger ɗinsa yana mata tafiyar tsusa, sai kallon yanayinta yake, gaba ɗaya idonsa sun koma kamar ba nashi ba.
Janye hannunta tayi ta miƙe tsaye.
“Bari mu tashi mu yi sallah”