Sashe 63
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani ɓangare na asibitin ya nufa, inda sauran sojojin suke. Yayi magana da su akan a canja ma Amira asibiti zuwa asibitin sojoji da ke Abuja. Cikin sirri suka kawo wata mota ya shiga yaje gida ya tsimtsa ya canja tufafin jikinsa dan duk sun ɓace da jini.
Army uniform ya saka ya shiga wata motar ya koma asibitin. Ko da ya isa har an canjawa Amira asibiti zuwa asibitin daya buƙata, wajen asibitin ya fito yayi magana da ƴan jarida ya tabbatar musu da abunda ya faru, sannan ya juya ya koma cikin asibiti shima aka soma duba lafiyarsa duk da sun san albarushin be same shi ba.
“Sir Hajiya ta matsa sai ta yi magana da kai, Mai Martaba ma ya kira tun ɗazu kusan sau biyar”
Ya faɗa bayan ya tsare masa ya maƙe guri ɗaya kamar irin ya sha jinin jikinsa ɗin nan.
Sai da aka cire masa abun awan jini sannan ya karɓi wayar. Number Mai maitaba ce wannan karon hakan yasa shi murmushi.
“My Royal Highness”
“Babana kana lafiya?”
“Ina nan ƙalau Mai martaba”
“Babana karka ɓoye min komai”
“Wallahi Babu abunda ya same ni, sai dai yarinya ita sun same ta”
“Ga mu nan gida duk sun rikice sai koke-koke suke, Ummin ka ma ta kirani wai nayi waya da kai? Ta kira ba kai ka ɗauka ba, tana jin dai ko sun same ka bata san halin da kake ciki ba”
“i'm fyn Mai martaba, yanzu nan ma nayi magana da ƴan jarida, da kun kalli news za ku gani ai”
“Wai ya abun ya faru? Kuma su wanene?”
“Wallahi ban san su ba, amman dukan an kashe su, ni ina fito daga restaurant ne kawai sai naga yarinya tana gudu ta doso inda nake, shine sai kawai naga wani ya fito a wata mota dake can nesa da mu, amman haka be hana bingdigar samunta da yake Allah ya rubuto, sai duk muka faɗi, sai na kira boys ɗin mu dake nan gida na faɗa musu sannan na kira head quarter na faɗa musu, kamin su bar gurin sai da suka harbi mutum biyu, kuma duk sun mutu. Sai dai dikansu basu tsira ba sai akayi musu ƙofar rago suna ganin haka sai suka fara buɗawa boys ɗin mu wuta, suma sai suka buɗa musu. Anyi nasara akan su dan an kashe su duka, sai dai suma sun kashe mana soldiers biyu”
“Subhanallah Allah ya tsare gaba, amman ita yarinya ba tare take da su ba?”
“Bana jin haka da ba zasu harbe ta ba, kuma ta zo da wata takardar hannunta an rubuta, wai nayi taka tsan-tsan akwai masu son kashe ni suna bibiyar sawuna, ba zasu min komai a garin Abuja ba har sai na isa katsina saboda sasu akayi”
“Amman ya akayi ita yarinyar ta san da wannan? Anya ba haɗin kai ba ne?”
“Tunanin hakan yasa aka bincika bullet ɗin dan a tabbatar na ƙwarai ne ko roba, an bincika bullet ɗin na ƙwarai ne irin wannan ne da ake shigo da shi ta waje, ta ɓarauniyar hanya, yanzu dai duk wasu tambayoyi sai idan ta farka zamu mata”
“Allah ya tsare gaba, a riƙa taka tsantsan Babana kana wasa da rayuwarka fa”
“Kar hakan ya dame ka Mai martaba, ɗan Adam baya wuce ƙaddararsa, kuma abunda Allah ya kawo babu mahani”
“Haka ne, amman gobe zaka dawo ko?”
Yayi dariya yana mai miƙewa tsaye ya nufi window gurin.
“Gobe kuma? Ai bamu gama meeting ba, akwai wanda za muyi gobe da jibi kamin na dawo”
“Kai ni wannan aiki naka Babana yana tsorata ni”
“To ya muka iya? Dole ne mu saiyardar rayuwarmu dan wasu su rayu”
“Toh Allah ya kyauta. Ga Mamanka zaku gaisa”
Haka Abdool ya bisu ɗaya bayan ɗaya yana gaisawa da matan uban masa da ƙannensa da ƴan'uwansa da suke gidan.
Yana katse kiran Mai martaba ya kira Ummi, ringing ɗaya ta ɗauka tana kuka.
“Son...”
“Ummi I'm fine Wallahi babu abunda ya same ni”
“Ban yarda da kai ba, ai ba zaka faɗa min gaskiya ba, naso na biyo mota saboda babu jirgi yanzu amman gobe da safe zan zo”
“Ummi you don't have to, Wallahi babu abunda ya same ni, yarinyar data tare min bullet ɗin ita aka samu, kuma an yi nasarar kashe su duka”
“I don't trust you”
“If you don't trust me, you should trust yourself, believe yourself remember how you treated your Son he will never ever lied to you”
“You started it”
“No I'm just show it”
“Whatever ni dai gobe zan zo”
“To Allah ya kai mu”
“Amin. Ga sisters naka za ku gaisa sun ta kiran wayarka sai wani ya ɗauka”
Ɗaya bayan ɗaya ya gaisa da su sannan Ummi ta karɓa.
“Ka kira Mai Martaba ɗazu na kira shi yace shi ma hankalinsa a tashe yake be same ka ba”
“Yanzu muka gama waya da shi”
“Okay, Son su waye ne suka maka haka?”
“Nima ban san su ba maƙiya ne kawai”
“Amman ita yarinya ta rayu? Ka santa ne? Ina ka haɗu da ita”
“Na fito ne kawai sai na ganta tana gudu ta doso inda na ke, shine suka buɗe mata wuta, tana da rai amman tana buƙatar addu'ah dan tana cikin mawuyacin hali”
“Allah ya tashi kafaɗunta, ko dan na mata godiya for what she did to our family”
“Ni kaina ina son ta tashi dan akwai tambayoyin da na ke son ta amsa min”
“Allah ya bata lafiya gobe zan zo”
“Ummi”
“Don't!”
Ya riƙe bakinsa kamar tana gabansa.
“To Allah kawo ki lafiya”
Daga haka ya kashe wayar ya juya ya fice daga ɗakin. Ba shi ya bar asibitin ba sai da ya karɓa waya ta fi a ƙirga ɗuk masu tambayar lafiyarsa ne ƴan'uwa da kuma abokan arziki.
NAMRA POV.
Tun da Yasmin ta bar gidan bata fito ko bakin ƙofa ba, balle har ta fito falo, Gwaggo Kulu bata takurata ba, dan tasan halin Namra daman can ba mai son surutu bace balle yanzu data fuskanci kamar tana cikin damuwa.
Duk wainar da ake toyawa a falon Namra bata sani ba, dan hankalinta ma kwata-kwata baya jikinta yana can wata duniyar tana tunanin lamarin rayuwa, yadda ta sauya mata a lokaci ɗaya. Turo ƙofar da Hindatu tayi ne yasa ta dawo hayyacinta har ta ɗan tsorota.
“Anty Namra”
Ta rumgune ta zumuɗi ita da Aisha. Ƴar far'ah tayi irin far'ar nan data zame maka dole tun da tasan ba zuwan daɗi ne ta yi ba.
Sai daga baya Maryam ta shigo dan tun shigowarta tana can gurin Gwaggo tanan mata faɗa akan rashin son zumunci, wai rabonta da gidan har ta manta.
A bakin ƙofa ta tsaya tana murmushi.
“Ta so muje ƴar Anty Abbah yace mu zo muje da ke”
“Da gaske?”
Namra ta tambaya tana zaro ido, irin mamakin ɗin nan da rashin yarda da zancen Maryam. Sai Aisha ta karɓa mata.
“Wallahi kuwa, da gaske shine ma ya kira ki a waya yace muje mu ɗauko ki”
“Ko dai wani abun ai min?”
Ta faɗa da muryar tausayi tana kallonsu, dan bata gamsu Abbah zai ce aje a zo da ita hakan nan kawai ba.
“Babu abunda zai miki baya ma gidan yanzu na fita, Anty ce ta buɗe masa wuta shiyasa ya yarda”
Shiru ta ɗan yi tana tunani, kamin ta miƙe tsaye ta ɗauki jakarta ta rayata, ta kalli Maryam.
“Dan Allah Abbah ne yace na zo?”
Maryam ta dafe kanta.
“Kai ni Allah na, Namra nawa zaki biya ni ne da zan miki ƙarya”
“Ina jin tsoro ne”
“Daman ai kullum cikin tsoro kike”
Ta juya ta fice tana mai jin haushin lamarin Namra. Cikin rashin kuzari ta fito ɗakin tana riƙe da hannun Aisha ta zo ta risina gaban Gwaggo dake zaune falon tana mata sallama kamar wanda bata son zuwa.
Gwaggo na kallon idonta ta kalli Maryam tace
“Duk aka haɗa baki da ke aka yi ma Namra wani abu ko? Heeeee Wallahi sai kin raina kan ki”
Maryam ta ɗora hannu saman kai tana dariya
“Oh Ni na shiga uku, wai fuskata tayi kama da mugaye ne hala?”
“Na dai san halin ki, shegen karanbani da iyayi, kuma na faɗa miki, wallahi ran ki sai ya fi na kowa ɓaci duk aka haɗa baki da ke”
Da dariya ta fita falon. Har gurin Mota Gwaggo ta raka su, tana yi Maryam jan kunne ta daina tuƙin dare kuma ta kula da hanya ban da gudu.
Har suka isa gida gaban Namra be daina dakan uku-uku ba, saboda tsoro da tunanin abunda Abbah zai mata. Lokacin da Namra ta fito motar sai ta ɗaga kanta sama ta kalli gid, idonta ya cika da hawaye, tuna rayuwar da tayi a ciki, da hawaye shaɓe-shaɓe Hindatu taja hannunta suka shiga falo.
Tsaye suka same Anty Amarya tana tsumayinsu, duk wani kunya da take na Namra yau cireshi tayi sai ta zo da sauri gurin ƙofa ta rumgume ƴarta idonta cike da hawaye, haƙiƙa tayi farincikin ganin Namra, sai dai kuma bata jidaɗin ganin yadda ta lalace ba, kamar wance ta shekara tana ciwo.
Maryam ne da Aisha suka ɗauko mata abinci da sha suka jera saman center table. Namra ta kallesu da murmushi.
“Thank you Sisters amman ni ba na cin komai”
“Saboda me? ”
Anty Amarya ta tambaya.
“Namra kamar akwai abunda yake damun ki?”
Shiru ta ɗan yi tana nazarin abunda zata cewa Anty Amarya, dan bata jin zata iya faɗa mata abunda Asim.yayi mata, ta san ba zai mata daɗi ba kuma ba zata ƙyale ba, bayan kuma koma minene itace ta jawa kanta.
“Babu abunda yake damuna, na riga na ci abinci gidan Gwaggo ne, har wanka ma nayi ina shirin bachi suka zo”
“Amman duk da haka Namra kina da damuwa be kamata ki ɓoye min ba, dan nasan wannan zuwan bana banza bane, babu yadda za ayi ki tsallake Asim ki zo nan bayan kin san yana gadon asibiti kwance”
“A...an sallame shi ai, yana gida Mamanshi take jinyarsa shine yace na zo saboda na sha kai da maganar gida ne, nima kwana biyu zan yi na koma”
Army uniform ya saka ya shiga wata motar ya koma asibitin. Ko da ya isa har an canjawa Amira asibiti zuwa asibitin daya buƙata, wajen asibitin ya fito yayi magana da ƴan jarida ya tabbatar musu da abunda ya faru, sannan ya juya ya koma cikin asibiti shima aka soma duba lafiyarsa duk da sun san albarushin be same shi ba.
“Sir Hajiya ta matsa sai ta yi magana da kai, Mai Martaba ma ya kira tun ɗazu kusan sau biyar”
Ya faɗa bayan ya tsare masa ya maƙe guri ɗaya kamar irin ya sha jinin jikinsa ɗin nan.
Sai da aka cire masa abun awan jini sannan ya karɓi wayar. Number Mai maitaba ce wannan karon hakan yasa shi murmushi.
“My Royal Highness”
“Babana kana lafiya?”
“Ina nan ƙalau Mai martaba”
“Babana karka ɓoye min komai”
“Wallahi Babu abunda ya same ni, sai dai yarinya ita sun same ta”
“Ga mu nan gida duk sun rikice sai koke-koke suke, Ummin ka ma ta kirani wai nayi waya da kai? Ta kira ba kai ka ɗauka ba, tana jin dai ko sun same ka bata san halin da kake ciki ba”
“i'm fyn Mai martaba, yanzu nan ma nayi magana da ƴan jarida, da kun kalli news za ku gani ai”
“Wai ya abun ya faru? Kuma su wanene?”
“Wallahi ban san su ba, amman dukan an kashe su, ni ina fito daga restaurant ne kawai sai naga yarinya tana gudu ta doso inda nake, shine sai kawai naga wani ya fito a wata mota dake can nesa da mu, amman haka be hana bingdigar samunta da yake Allah ya rubuto, sai duk muka faɗi, sai na kira boys ɗin mu dake nan gida na faɗa musu sannan na kira head quarter na faɗa musu, kamin su bar gurin sai da suka harbi mutum biyu, kuma duk sun mutu. Sai dai dikansu basu tsira ba sai akayi musu ƙofar rago suna ganin haka sai suka fara buɗawa boys ɗin mu wuta, suma sai suka buɗa musu. Anyi nasara akan su dan an kashe su duka, sai dai suma sun kashe mana soldiers biyu”
“Subhanallah Allah ya tsare gaba, amman ita yarinya ba tare take da su ba?”
“Bana jin haka da ba zasu harbe ta ba, kuma ta zo da wata takardar hannunta an rubuta, wai nayi taka tsan-tsan akwai masu son kashe ni suna bibiyar sawuna, ba zasu min komai a garin Abuja ba har sai na isa katsina saboda sasu akayi”
“Amman ya akayi ita yarinyar ta san da wannan? Anya ba haɗin kai ba ne?”
“Tunanin hakan yasa aka bincika bullet ɗin dan a tabbatar na ƙwarai ne ko roba, an bincika bullet ɗin na ƙwarai ne irin wannan ne da ake shigo da shi ta waje, ta ɓarauniyar hanya, yanzu dai duk wasu tambayoyi sai idan ta farka zamu mata”
“Allah ya tsare gaba, a riƙa taka tsantsan Babana kana wasa da rayuwarka fa”
“Kar hakan ya dame ka Mai martaba, ɗan Adam baya wuce ƙaddararsa, kuma abunda Allah ya kawo babu mahani”
“Haka ne, amman gobe zaka dawo ko?”
Yayi dariya yana mai miƙewa tsaye ya nufi window gurin.
“Gobe kuma? Ai bamu gama meeting ba, akwai wanda za muyi gobe da jibi kamin na dawo”
“Kai ni wannan aiki naka Babana yana tsorata ni”
“To ya muka iya? Dole ne mu saiyardar rayuwarmu dan wasu su rayu”
“Toh Allah ya kyauta. Ga Mamanka zaku gaisa”
Haka Abdool ya bisu ɗaya bayan ɗaya yana gaisawa da matan uban masa da ƙannensa da ƴan'uwansa da suke gidan.
Yana katse kiran Mai martaba ya kira Ummi, ringing ɗaya ta ɗauka tana kuka.
“Son...”
“Ummi I'm fine Wallahi babu abunda ya same ni”
“Ban yarda da kai ba, ai ba zaka faɗa min gaskiya ba, naso na biyo mota saboda babu jirgi yanzu amman gobe da safe zan zo”
“Ummi you don't have to, Wallahi babu abunda ya same ni, yarinyar data tare min bullet ɗin ita aka samu, kuma an yi nasarar kashe su duka”
“I don't trust you”
“If you don't trust me, you should trust yourself, believe yourself remember how you treated your Son he will never ever lied to you”
“You started it”
“No I'm just show it”
“Whatever ni dai gobe zan zo”
“To Allah ya kai mu”
“Amin. Ga sisters naka za ku gaisa sun ta kiran wayarka sai wani ya ɗauka”
Ɗaya bayan ɗaya ya gaisa da su sannan Ummi ta karɓa.
“Ka kira Mai Martaba ɗazu na kira shi yace shi ma hankalinsa a tashe yake be same ka ba”
“Yanzu muka gama waya da shi”
“Okay, Son su waye ne suka maka haka?”
“Nima ban san su ba maƙiya ne kawai”
“Amman ita yarinya ta rayu? Ka santa ne? Ina ka haɗu da ita”
“Na fito ne kawai sai na ganta tana gudu ta doso inda na ke, shine suka buɗe mata wuta, tana da rai amman tana buƙatar addu'ah dan tana cikin mawuyacin hali”
“Allah ya tashi kafaɗunta, ko dan na mata godiya for what she did to our family”
“Ni kaina ina son ta tashi dan akwai tambayoyin da na ke son ta amsa min”
“Allah ya bata lafiya gobe zan zo”
“Ummi”
“Don't!”
Ya riƙe bakinsa kamar tana gabansa.
“To Allah kawo ki lafiya”
Daga haka ya kashe wayar ya juya ya fice daga ɗakin. Ba shi ya bar asibitin ba sai da ya karɓa waya ta fi a ƙirga ɗuk masu tambayar lafiyarsa ne ƴan'uwa da kuma abokan arziki.
NAMRA POV.
Tun da Yasmin ta bar gidan bata fito ko bakin ƙofa ba, balle har ta fito falo, Gwaggo Kulu bata takurata ba, dan tasan halin Namra daman can ba mai son surutu bace balle yanzu data fuskanci kamar tana cikin damuwa.
Duk wainar da ake toyawa a falon Namra bata sani ba, dan hankalinta ma kwata-kwata baya jikinta yana can wata duniyar tana tunanin lamarin rayuwa, yadda ta sauya mata a lokaci ɗaya. Turo ƙofar da Hindatu tayi ne yasa ta dawo hayyacinta har ta ɗan tsorota.
“Anty Namra”
Ta rumgune ta zumuɗi ita da Aisha. Ƴar far'ah tayi irin far'ar nan data zame maka dole tun da tasan ba zuwan daɗi ne ta yi ba.
Sai daga baya Maryam ta shigo dan tun shigowarta tana can gurin Gwaggo tanan mata faɗa akan rashin son zumunci, wai rabonta da gidan har ta manta.
A bakin ƙofa ta tsaya tana murmushi.
“Ta so muje ƴar Anty Abbah yace mu zo muje da ke”
“Da gaske?”
Namra ta tambaya tana zaro ido, irin mamakin ɗin nan da rashin yarda da zancen Maryam. Sai Aisha ta karɓa mata.
“Wallahi kuwa, da gaske shine ma ya kira ki a waya yace muje mu ɗauko ki”
“Ko dai wani abun ai min?”
Ta faɗa da muryar tausayi tana kallonsu, dan bata gamsu Abbah zai ce aje a zo da ita hakan nan kawai ba.
“Babu abunda zai miki baya ma gidan yanzu na fita, Anty ce ta buɗe masa wuta shiyasa ya yarda”
Shiru ta ɗan yi tana tunani, kamin ta miƙe tsaye ta ɗauki jakarta ta rayata, ta kalli Maryam.
“Dan Allah Abbah ne yace na zo?”
Maryam ta dafe kanta.
“Kai ni Allah na, Namra nawa zaki biya ni ne da zan miki ƙarya”
“Ina jin tsoro ne”
“Daman ai kullum cikin tsoro kike”
Ta juya ta fice tana mai jin haushin lamarin Namra. Cikin rashin kuzari ta fito ɗakin tana riƙe da hannun Aisha ta zo ta risina gaban Gwaggo dake zaune falon tana mata sallama kamar wanda bata son zuwa.
Gwaggo na kallon idonta ta kalli Maryam tace
“Duk aka haɗa baki da ke aka yi ma Namra wani abu ko? Heeeee Wallahi sai kin raina kan ki”
Maryam ta ɗora hannu saman kai tana dariya
“Oh Ni na shiga uku, wai fuskata tayi kama da mugaye ne hala?”
“Na dai san halin ki, shegen karanbani da iyayi, kuma na faɗa miki, wallahi ran ki sai ya fi na kowa ɓaci duk aka haɗa baki da ke”
Da dariya ta fita falon. Har gurin Mota Gwaggo ta raka su, tana yi Maryam jan kunne ta daina tuƙin dare kuma ta kula da hanya ban da gudu.
Har suka isa gida gaban Namra be daina dakan uku-uku ba, saboda tsoro da tunanin abunda Abbah zai mata. Lokacin da Namra ta fito motar sai ta ɗaga kanta sama ta kalli gid, idonta ya cika da hawaye, tuna rayuwar da tayi a ciki, da hawaye shaɓe-shaɓe Hindatu taja hannunta suka shiga falo.
Tsaye suka same Anty Amarya tana tsumayinsu, duk wani kunya da take na Namra yau cireshi tayi sai ta zo da sauri gurin ƙofa ta rumgume ƴarta idonta cike da hawaye, haƙiƙa tayi farincikin ganin Namra, sai dai kuma bata jidaɗin ganin yadda ta lalace ba, kamar wance ta shekara tana ciwo.
Maryam ne da Aisha suka ɗauko mata abinci da sha suka jera saman center table. Namra ta kallesu da murmushi.
“Thank you Sisters amman ni ba na cin komai”
“Saboda me? ”
Anty Amarya ta tambaya.
“Namra kamar akwai abunda yake damun ki?”
Shiru ta ɗan yi tana nazarin abunda zata cewa Anty Amarya, dan bata jin zata iya faɗa mata abunda Asim.yayi mata, ta san ba zai mata daɗi ba kuma ba zata ƙyale ba, bayan kuma koma minene itace ta jawa kanta.
“Babu abunda yake damuna, na riga na ci abinci gidan Gwaggo ne, har wanka ma nayi ina shirin bachi suka zo”
“Amman duk da haka Namra kina da damuwa be kamata ki ɓoye min ba, dan nasan wannan zuwan bana banza bane, babu yadda za ayi ki tsallake Asim ki zo nan bayan kin san yana gadon asibiti kwance”
“A...an sallame shi ai, yana gida Mamanshi take jinyarsa shine yace na zo saboda na sha kai da maganar gida ne, nima kwana biyu zan yi na koma”